Editor

9444 Posts
Adabi rayayyar kalma ce wadda ba ta mutuwa – Hauwa Lawal Maiturare

Adabi rayayyar kalma ce wadda ba ta mutuwa – Hauwa Lawal Maiturare

Hauwa Lawal Maiturare ba ta da buƙatar doguwar gabatarwa a duniyar rubutu. Sananniya ce ga waɗanda su ka fara karance-karancen littattafan Hausa wuraren 1998. Ta kasance cikin jerin marubuta da su ka shigo duniyar rubutu da ƙafar dama. Masu karatu za su tuna Maiturare da littafin ta na ‘Haske Maganin Duhu’ ko ‘Gobarar Gemu’. Wannan jarida mai farin jini ta yi nasarar kawo maku ita a wannan mako. Ku biyo mu don jin yadda tataunawar ta kasance. Daga AISHA ASAS a Abuja Mu fara da jin cikakken tarihin ki.Suna na Hauwa Lawal Maiturare wacce aka fi sani da Ƙamshi. Ni…
Read More
2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

2023: Matasa sun buƙaci Tinubu ya fito takarar shugaban ƙasa

Daga WAKILINMU Mambobin Ƙungiyar Matasa Magoya Bayan Tinubu (NYMT), sun yi kira ga jigon jam’iyyar APC, Asiwaju Ahmed Tinubu, da ya fito takarar neman shugabancin ƙasa a 2023. Matasan sun yi ra’ayin cewa babu wanda ya fi cancanta ya gaji Shugaba Muhammadu Buhari kamar Tinubu domin ci gaba ƙarfafa nasararorin da gwamnatin APC ta samu. A cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a Abuja, Darakta Janar na ƙungiyar, Mukhtar Husseini ya jigon ya yi sadaukarwa sosai wajen ɗorewar dimukraɗiyyar da ake cin moriyarta a yau. Ya ce buƙatar mara wa Tinubu baya ta taso ne bisa la’akari da…
Read More
Kenya: An yanke wa ‘yar wasan tsere hukuncin shekara guda saboda amfani da maganin ƙara kuzari

Kenya: An yanke wa ‘yar wasan tsere hukuncin shekara guda saboda amfani da maganin ƙara kuzari

Daga FATUHU MUSTAPHA Wata kotun ƙasar Kenya ta yanke wa ‘yar wasan tseren asar, Florence Jepkosgei, hukuncin yi wa al’umma hidima na tsawon shekara guda bayan da ta kama ta da laifin gabatar da takardun bogi na ƙoƙarin kare kanta daga laifin yin amfani da ƙwayoyin ƙara kuzari, in ji Ƙungiyar Yaƙi da Amfani da Abubuwan Ƙara Kuazara ga ‘Yanwasa ta Kenya (ADAK). Da wannan, Florence ta zama ‘yar tseren Kenya ta farko da aka taɓa yanke wa hukuncin manyan laifuka a kotu. An shafe shekaru ana gudanar da bincike kan wannan batu kafin a kai ga yanke hukunci a…
Read More
Shugabar WTO ta iso Nijeriya, za ta gana da Buhari

Shugabar WTO ta iso Nijeriya, za ta gana da Buhari

Sabuwar Shugabar Hukumar Cinikayya ta Duniya (WTO) Dr. Ngozi Okonjo-Iweala, ta iso Nijeriya inda ake sa ran za ta shafe mako guda. Daga bayanan da Manhaja ta kalato, kai ziyara ga Shugaba Muhammadu Buhari na daga cikin harkokin da Ngozi za ta aiwatar domin nuna godiyarta ga irin rawar da Buhari ya taka wajen ganin ta sami ɗarewa sabon muƙamin nata. Okonjo-Iweala ta ce yayin ziyarar tata, za ta tattauna da Shugaba Buhari tare da sauran masu ruwa da tsaki game da irin tanadin da WTO ta yi wa tattalin arzikin Nijeriya a matsayinta na shugabar hukumar.
Read More
Gwamna Sule ya bada umarnin ladabtar da ɗaliban da suka haifar da zan-zanga a kwalejin Mustapha Agwai I

Gwamna Sule ya bada umarnin ladabtar da ɗaliban da suka haifar da zan-zanga a kwalejin Mustapha Agwai I

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bada umarnin a binciko tare da ladabtar da duk wanda aka samu da hannu a rikicin ɗalibai da ya auku kwannan nan a kwalejin fasaha ta Isa Mustapha Agwai I Polytechnic (IMAP) da ke Lafia. Gwamna Sule ya bada wannan umarnin ne ga shugaban kwlejin, Dr. Justina Anjide Kotso, a Juma'ar da ta gabata, domin tabbatar da an ladabtar da waɗanda suka haifar da rikicin da ya yi sanadiyar lalata kayayyaki da dama a makarantar. Ya bada umarnin ne bayan da ya kai ziyarar gani da ido a makarantar, tare…
Read More
Martani: Muƙabalar Kano

Martani: Muƙabalar Kano

Daga ALIYU SAMBA Naso a ce yadda ka faɗa a farko ɗin ka aikata, shi ne baka so ka ce komai ba dan cewar ka ba za ta hana ba, a lokaci guda kuma ba za ta sa ba, to amma sai ya zam cewa malam ya magantu ta irin usulubin da nake ganin ya kamata ace ya sake bitar abubuwan nan yadda ya kamata. A zaton da nake wa Malam Saleh Ƙaura shi ne, mutum ne da zai ƙoƙarin yin adalci ga kowa ba tare da la'akari da saɓanin dake tsakanin su ba, sashen rubuce rubucen sa suna cike…
Read More
Muƙabalar Kano

Muƙabalar Kano

Daga SALEH ƘAURA Ban so na ce komai ba, saboda na san magana ta ba za ta sa ba, ba kuma za ta hana ba, amma dai ganin cewa da alama addu’ar da muka duƙufa muna yi na Allah ya hana duk wata dama da za a yaɗa wannan baƙar guba ta isa zuwa ga kunnuwan muminai koda da wani irin suna ne, ta amsu, shi ya sanya na ce bari in gabatar da waɗannan tambayoyi, domin dai tsakani da Allah abin mamaki yake ba ni, ya kuma yi matuqar ɗaure mini kai: 1) An ce gwamnatin Kano, ta rufe…
Read More
Gwamnati ta ƙaddamar da rukunin ‘C’ na shirin N-Power

Gwamnati ta ƙaddamar da rukunin ‘C’ na shirin N-Power

An fitar da matakan da masu shiga shirin za su bi Daga WAKILIN MU Gwamnatin Tarayya ta kawo ƙarshen dogon jiran da ake yi na fara aiwatar da rukuni na uku (Batch C) na shirin N-Power wanda za a shigar cikin jerin shirye-shiryen rage matsin rayuwa, wato National Social Investment Programmes (NSIPs). Mai bada shawara kan aikin jarida ga Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Madam Nneka Ikem, ita ce ta bayyana haka a ranar Alhamis cikin wani saƙo da ta tura a Twitter. A cewar ta, ana kira ga dukkan waɗanda su ka cike takardun nema shiga shirin…
Read More
Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Tashin gwauron zabo da farashi ke yi

Rahoton da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta bayar kwanan nan kan alƙaluman farashin kayan masarufi (CPI) abin damuwa ne matuƙa. Rahoton ya ce jadawalin tashin farashi a Nijeriya ya ƙaru da kashi 12.82 cikin ɗari a watan Yuli da ya gabata, kuma ba a taɓa ganin irin wannan tashin ba a cikin watanni 27 tun daga watan Maris na 2018 lokacin da farashi ya yi bala’in tashi da kashi 13.34 cikin ɗari. Wannan yanayin zai ƙara tavarɓarar da fatara da yunwa da ake ciki, wanda hakan kuma bazarana ce ga Shirye-shiryen Agajin Jama’a (SIPs) waɗanda Gwamnatin Tarayya ke aiwatarwa,…
Read More
’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

’Yan bindiga: A yafe ko a bindige?

Daga IBRAHIM SHEME Kwanan nan Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmad El-Rufa’i, ya jawo wata muhawara a kan batun a yafe wa ‘yan bindiga ko a kashe su idan an gan su. Matsayar sa ita ce kada a yi wani zaman tattaunawa da su don a samu hanyar da za a warware ibtila’in kashe-kashe da ke faruwa a yankin Arewa-maso-yamma na ƙasar nan. Gara a nuna masu ƙarfin soja, a murƙushe su, babu sassautawa ko jinƙai. A wata hira da aka yi da shi a gidan rediyon BBC, El-Rufa’i ya bayyana cewa duk wata hanyar lalama da za a bi…
Read More