Editor

9513 Posts
IPMAN ta bada umarnin ci gaba da sayar da fetur kan N163

IPMAN ta bada umarnin ci gaba da sayar da fetur kan N163

Daga FATUHU MUSTAPHA Ƙungiyar 'Yan Kasuwar Fetur Masu Zaman Kansu ta Nijeriya (IPMAN), ta ce ba ta samu wata sanarwar ƙarin kuɗin fetur a hukumance ba, don haka ta buƙaci mambobinta da su yi watsi da jita-jitar da ake ta yaɗawa game da ƙarin farashin fetur. A wata ganawa da ya yi da manema labarai a wannan Juma'ar, shugaban IPMAN reshen jihar Kano, Bashir Dan-Malam, ya bai wa mambobinsu umarnin su ci gaba da saida fetur kan farashin N163 kowace lita. Yana mai cewa duk lokacin da aka samu ƙarin farashin mai a ƙasa, masu ruwa da tsaki na fannin…
Read More
Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Mawuyacin halin da Fulani makiyaya su ke ciki laifin gwamnonin Arewa ne?

Daga TIJJANI SARKI  A 'yan makonnin nan an sami tashin tashina a wanin ɓangare na jihohin kudancin ƙasar nan, har inda wani gwamna ya ke ba da sanarwar korar ƙabilar Fulani makiyaya daga faɗin jihar sa, abin har ya kai da ƙona musu gidaje da masallaci  duk dai bisa dogaro da su ba 'yan jihar ba ne. Kuma suna kawo yamutsi a jihar, kodayake mun jiyo Gwamnan Jihar Ogun na cewa suna zaman lafiya da Fulani sama da shekaru ɗari a jiharsa. Zai yi kyau mu ɗan yi waiwaye akan ƙabilar Fulani makiyaya wanda suke da ɗumbin yawa musamman a…
Read More
Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (2)

Gudunmawar harshe da al’ada ga bunƙasa tattalin arziƙi da zaman lafiya (2)

Daga FARFESA SALISU AHMAD YAKASAI Harshe ba shi da alaƙa da mutum, wato ba wai haihuwar mutum a awuri ke sa ya ji harshen su mutanen wurin ba, sai dai idan ya tashi da amfani da shi. Saboda haka, duk wanda ya tashi da wani harshe, to lallai harshen zai koya. Jinin mutum ba ya da alaƙa da harshensa, domin sai a samu Baturen Ingila yana Larabci, ko kuwa Bafaranshe yana Hausa. Kenan furucin mutum ba ya nuna qabilarsa, domin furuci ba manunin ƙabila ne ba sai dai idan mutum ya faɗi ƙabilarsa, tun da duk inda mutum ya tashi,…
Read More
Duk wadda ta zauna za ta ga zaunau – Fatima Yusuf Muhammad

Duk wadda ta zauna za ta ga zaunau – Fatima Yusuf Muhammad

Fatima Yusuf Muhammad ta kasance mace mara kasala wajen fafutikar neman ilimi, sana’ar dogaro da kai da kuma faɗakar da al’umma da nishaɗantar da su ta hanyar rubuce-rubucen littattafan hikaya. A wannan makon Manhaja ta yi wa masu karatu kiciɓis da ita don jin yadda ta ke jifar tsuntsaye uku da dutse ɗaya, ma’ana ga neman ilimi da ta sa gaba, sana’a da kuma rubutu, ga kuma ɗawainiyar iyali. Kai, wani aiki dai sai mai shi. Ga yadda tattaunar ta kasance:  Masu karatu zasu so jin tarihin ki.Ni dai suna na Fatima Yusuf Muhammad. An haife ni a garin Kaugama…
Read More
‘Yan sanda sun ceci motocin BRT a Legas

‘Yan sanda sun ceci motocin BRT a Legas

Daga WAKILINMU Rundunar 'yan sanda a Legas, ta ce ta yi nasarar daƙile harkokin ɓatagarin da suka yi yinƙurin yi wa fasinjoji fashi a dogayen motocin safa na BRT a lokacin da aka samu tsaikon abubuwan hawa sakamakon wani haɗari da ya auku. A cewar sanarwar da ta fito ta hannun jami'in hulɗa da jama'a na 'yan sandan jihar, CSP Olumuyiwa Adejobi, ganin abin da ke faruwa sai kwamishinan 'yan sandan jihar, CP Hakeem Odumosu ya bai wa jami'an sashen kai ɗaukin gaggawa (RRS) na rundunar umarnin su je su tabbatar da lumana a yankin da lamarin ya shafa. Daga…
Read More
Babu buƙatar tada hankula game da rigakafin korona – Gwamnati

Babu buƙatar tada hankula game da rigakafin korona – Gwamnati

Daga UMAR M. GOMBE Gwamnatin Tarayya ta hori 'yan Nijeriya da su kwantar da hankulansu dangane da rukunin rigakafin korona na Oxford-AstraZeneca da ta karɓa saboda a cewarta, babu wata illa a tattare da rigakafin. Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA) ita ce ta bada wannan tabbaci a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis ta hannun shugaban sashenta na hulɗa da jama'a, Mohammad Ohitoto. Yayin da wasu rahotanni ke nuni da wasu ƙasashe sun dakatar da yin allurar, amma hukumar NPHCDA ta buƙaci 'yan Nijeriya kada su tada hankulansu. Hukumar ta ce yayin da take lura…
Read More
Ogun: Kwastam ta kama shinkafar ƙetare buhu 5,931, tabar wiwi buhu 290

Ogun: Kwastam ta kama shinkafar ƙetare buhu 5,931, tabar wiwi buhu 290

Daga WAKILINMU A matsayin wani mataki na ci gaba da kare rayuwar matasa daga barin faɗawa garari, Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta shiyyar Ogon I ta matse ƙaimi wajen yaƙi da fasa-ƙwaurin miyagun ƙwayoyi da sauran kayayyakin da aka haramta shigo da su cikin ƙasa. Da wannan ne hukumar kwastam ɗin ta ce lallai aikin haɗin gwiwar da suke yi tare da Hukumar Yaƙi da Sha da Safarar Muggan Ƙwayoyi (NDLEA) a shiyyar Ogun ya haifar da ɗa mai ido. A cewar shugaban hukumar kwastam na shiyyar, Comptroller PC Kolo, sun samu nasarar kama tabar wiwi har buhu 290 da…
Read More
Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Zaɓen 2019: Lauyoyi sun nemi APC ta biya su haƙƙinsu a Kano

Daga FATUHU MUSTAPHA Wata tawagar lauyoyi a jihar Kano ta yinƙura neman haƙƙinta daga hannun jam'iyyar APC reshen jihar na aikin da ta yi mata yayin zaɓen 2019. A wata wasiƙa da suka aika wa APC ta hannun lauyansu Usman Umar Fari, lauyoyin da lamarin ya shafa sun buƙaci jam'iyyar ta hanzarta biyansu kuɗeɗen aikin da suka yi mata yayin babban zaɓe na 2019. Lauyoyin sun ce kuɗin da suke nema a biya su, haƙƙin aikin da suka yi wa APC ne kan batutuwan da suka shafi sha'anin shari'ar zaɓe. Lauyan lauyoyin, Usman Fari, ya ja hankalin jam'iyyar kan cewa…
Read More
Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Kuɗaɗen Ibori da aka maido mallakar jihar Delta ne – Majalisa

Daga WAKILINMU Majalisar Wakilai ta Ƙasa, ta buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta maida kuɗaɗen da Ibori ya sata, Pan milyan  £4.2, ga Jihar Delta. Wannan ya biyo bayan ƙudirin da 'yan majalisar daga jihar Delta suka gabatar wa majalisar ne a Larabar da ta gabata. Haka nan, 'yan majalisar sun ce jimillar kuɗin Pan miliyan £6.2 ne amma ba milyan  £4.2 ba kamar yadda aka ruwaito. Bugu da ƙari, Majalisar ta buƙaci Ma'aikatar Kuɗi ta Kasa da ta bai wa Babban Lauyan Gwamnati kuma Ministan Shari'a, Abubakar Malami, umarnin ya miƙa wa Majalisar dukkan takardun da ke da alaƙa da…
Read More
Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Gwamna Sule ya ƙaddamar da rigakafin korona a Nasarawa

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Nasarawa Engineer Abdullahi Sule, ya ƙaddamar da allurar rigakafin cutar koron inda shi da mataimakinsa, Dr. Emmanuel Akabe, suka soma yin rigakafin na Oxford-AstraZeneca. Bikin ƙaddamarwar ya gudana ne ranar Talata a fadar gwamnatin jihar da ke Lafia, babban birnin jihar. Da yake yi wa manema labarai bayani jim kaɗan bayan ya yi allurar, Gwamna Sule ya yi kira ga 'yan jiharsa, musamman ma waɗanda suka fi fuskantar haɗarin harbuwa da cutar kamar 'yan siyasa da sarakunan gargajiya da sauransu, da su tabbatar sun yi allurar. Gwamnan ya yi amfani da wannan dama wajen nuna godiyarsa…
Read More