23
Feb
Daga WAKILIN MU Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq, ta bayyana alhinin ta kan faɗowar jirgin saman Rundunar Mayaƙan Sama ta Nijeriya (NAF) ƙirar Beechcraft KingAir B350i Aircraft a ranar Lahadi a Abuja. Rahotanni sun ce jirgin ya samu matsalar inji bayan ya tashi sannan ya faɗo ƙasa. Hajiya Sadiya ta bayyana baƙin ciki kan haɗarin jirgin da kuma asarar rayukan waɗanda ke cikin jirgin da aka yi. Ta ce, "Ina cikin tsananin alhini da baƙin cikin wannan abu maras daɗi da ya faru. Ina miƙa gaisuwa ta ga Rundunar Mayaƙan Sama da iyalan waɗanda…