Editor

9328 Posts
Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) ta rufe wani kamfanin sarrafa abinci a Jihar Legas bisa laifin sayar wa jama'a da sinadarin haɗa abinci (Thyme da Curry) bayan kuma wa'adin amfaninsu ya ƙare. NAFDAC ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin tsaftace Nijeriya daga abinci mara inganci domin ci gaba da kare lafiyar 'yan ƙasa. A sanarwar da jami'in yaɗa labarai na shiyya na hukumar Sayo Akintola ya fitar, Babbar Daraktar hukumar Prof. Mojisola Adeyeye ta bayyana damuwarta kan lamarin. Tana mai cewa za a ƙaƙaba wa kamfanin da lamarin ya…
Read More
Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Afirka ta Kudu ta fasa shirin yi wa ‘yan ƙasar rigakafin korona

Daga AISHA ASAS Ƙasar Afirka ta Kudu ta ce ta fasa shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin cutar korona da ta so somawa bayan da ta gano cewa gwajin maganin AstraZeneca jab da ta yi ya kasa yaƙar nau'in cutar da ya bayyana a ƙasar. Afirka ta Kudu ita ce ƙasar da ta fi kowace ƙasa harbuwa da cutar a faɗin nahiyar Afirka, inda ta so soma aiwatar da shirin yi wa 'yan ƙasar allurar rigakafin korona da ta mallaka daga AstraZeneca da Oxford. A cewar Ministan Lafiyar ƙasar Zweli Mkhize, "Mun dakatar da rigakafin na wucin-gadi har sai…
Read More
Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Cutar Korona: Abu Dhabi ta haramta tarurrukan shaƙatawa da na bukukuwa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani mataki na yaƙi da yaɗuwar annobar korona a Abu Dhabi, Kwamitin Kula da Agajin Gaggawa, rikice-rikice da Ibtila'i na Abu Dhabi ya sanya dokar haramta tarurrukan shaƙawata da na bukukuwa a faɗin birnin sai dai ɗan abin da ba za a rasa ba. Kwamitin ya ce daga ranar 7 ga Fabrairun 2021, an taƙaita adadin mutane da aka amince su halarci taron bikin aure da na zumunta zuwa mutum 10, sannan mutum 20 game da tarurrukan da suka shafi jana'iza da zaman makoke. Haka nan an taƙaita yawan mutanen da aka yarda su gudanar…
Read More
2023: Ba za mu zaɓi matsafa ba a Akwai Ibom – Mbang

2023: Ba za mu zaɓi matsafa ba a Akwai Ibom – Mbang

Daga WAKILIN MU Tsohon Shugaban Ƙungiyar Kiristoci ta Ƙasa (CAN) Sunday Mbang, ya gargaɗi 'yan siyasar jihar Akwa Ibom masu neman tsayawa takara a zaɓuɓɓukan 2023 da su nesanta kansu da harkokin ƙungiyar asiri. Mbang ya yi wannan gargaɗi ne sa'ilin da yake amsa tambayoyin manema labarai a wajen taron addu'a ta musamman da aka shirya wa 'yan majalisun tarayya daga jihar don nema musu kariya daga cutar korona a ƙarshen mako a Uyo, babban birnin jihar. Jagoran addinin ya ce Allah ba zai bari duk wani ɗan siyasa a jihar mai mu'amala da tsafi da makamancin haka ya zama…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

Daga AISHA ASAS Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Tungan Maje da ke yankin Gwagwalada, Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mutum huɗu. Al'amarin wanda ya auku a tsakar daren wannan Lahadin, sai da 'yan bindigar suka shafe kimanin sa'o'i uku suna abin da suka ga dama a Tungan Maje kafin daga bisani suka yi awon gaba da wani tsohon jami'in Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) Abdulahi Idris Rakieu da wasu mutum biyu daga iyalan gidansa. A cewar jaridar TheCable, harin ya shafi wani mai suna Olusola Agun, wanda shi ya zama cikon na…
Read More
Atiku ya roƙi gwamnati kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet

Atiku ya roƙi gwamnati kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet

Daga FATUHU MUSTAPHA Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya roƙi gwamnatin Shugaba Buhari kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet wanda aka fi sani da 'cryptocurrency' a Turance. A Juma'ar da ta gabata Babban Bankin Nijeriya (CBN) aya bada umarnin bankuna da dangoginsu su rufe duka asusun da ke da alaƙa da harkar kuɗaɗen intanet ba tare da ɓata lokaci ba. A wata sanarwa da ya sanya wa hannu Asabar da ta gabata, Atiku ya ce kamata ya yi gwamnati ta ɗauki matakin sanya wa harakar ido maimakon daƙile ta baki ɗaya. Tare da bada misalin yadda hada-hadar kuɗaɗen…
Read More
Amnesty International na neman wargaza Nijeriya – inji Lai Mohammed

Amnesty International na neman wargaza Nijeriya – inji Lai Mohammed

Daga AISHA ASAS Gwamnatin Tarayya ta zargi Ƙungiyar Kare 'Yancin Ɗan-Adam ta Duniya (AI) da take-taken neman wargaza Nijeriya da gangar ta hanyar ɗora zarge-zarge a kan gwamnati da kuma sojoji. Ministan Labarai da Al'adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya yi wannan zargi yayin wata hira da wata tashar talabijin ta yi da shi a Juma'ar da ta gabata a Legas wadda Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ta bibiya. Ministan ya bayyana haka ne a matsayin martani ga wani rahoton ƙungiyar a kan yaƙi da batun take 'yancin ɗan-Adam a faɗin duniya inda ta nuna an yi zargin an…
Read More
CBN ya haramta wa bankuna hada-hadar kuɗaɗen intanet

CBN ya haramta wa bankuna hada-hadar kuɗaɗen intanet

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bai wa bankuna umarnin su rufe duk wani asusun ajiya da karɓar kuɗaɗe a banki da ke da alaƙa da cinikin kuɗin intanet (cryptocurrency). A Juma'ar da ta gabata CBN ya aike wa bankunan umarnin nasa zuwa bankuna masu karɓar ajiyar kuɗaɗe (DMB) da hukumomi masu hada-hadar kuɗaɗe (NBFI) da makamantansu, a kan su gaggauta daƙile dukkan asusun da ake amfani da su wajen hada-dahar kasuwar sulallan intanet (bitcoin). Idan dai za a iya tunawa a Janairun 2017 ne CBN ya bayyana cewa ana amfani da hada-hadar kuɗaɗen intanet irin sulallan bitcoin…
Read More
Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Ciwon daji: An damu da shi kuwa?

Daga IBRAHIM SHEME Majalisar Ɗinkin Duniya ta ware ranar 4 ga Fabrairu ta kowace shekara a matsayin Ranar Yaƙi Da Cutar Daji ta Duniya, wato a turance 'World Cancer Day'. Muhimmancin ranar shi ne mutane su tuna da irin ɓarnar da cutar ke yi da matakan da ya kamata a ɗauka don rigakafi da kuma hanyoyin magance ta. A jiya Alhamis ne wannan rana ta kama a bana. Abin mamaki, ban ji inda aka yi wata yekuwa ko gangami don tunawa da ranar ba a jiya. Akwai 'yan labarurruka da ƙungiyoyi masu yaƙi da cutar su ka ɗan yaɗa, su…
Read More
INEC za ta samar da sabbin mazaɓu a faɗin Nijeriya kafin zaɓen 2023 – Mahmood Yakubu

INEC za ta samar da sabbin mazaɓu a faɗin Nijeriya kafin zaɓen 2023 – Mahmood Yakubu

Daga WAKILIN MU Nan da lokacin da za a gudanar da babban zaɓe a Nijeriya, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) za ta samar da ƙarin mazaɓu a faɗin ƙasar. Shugaban kwamitin wayar da kan masu zaɓe a hukumar (IVEC), Mista Festus Okoye, shi ne ya bayyana haka a Abuja. Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, a cikin Agustan 2014 INEC ta gabatar da buƙatar samar da ƙarin mazaɓu 30,027, inda arewacin ƙasar za ta samu mazaɓu 21,615 yayin da kudu za ta samu 8,412. Wannan ya janyo ce-ce-ku-cen da ya sa INEC ta watsar da shirin. Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ya…
Read More