Editor

9513 Posts
ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

ICPC ta tsare Ojerinde saboda badaƙalar milyan N900

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar yaƙi da rashawa ta ICPC ta cafke tsohon shugaban hukumar jarrabawar shiga jami'a (JAMB), Dibu Ojerinde bisa zargin badakalar Naira miliyan 900. Jami'an hukumar ne suka cafke Ojerinde ran15 Maris a Abuja bisa zargin aikata zambar kuɗaɗe a lokacin da ya shugabanci hukumar JAMB da kuma Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO). A cewar sanarwar da mai magana da yawun ICPC, Mrs. Azuka C. Oguguata fitar, ana tsare da wanda ake zargin. ICPC ta cafke Ojerinde bisa laifukan zambar kuɗaɗe ciki har odar sayo fensura da abun goge rubutu kan Naira miliyan 450 kowanne tsakanin 2013…
Read More
Legas kaɗai na da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi milyan 4, cewar Marwa

Legas kaɗai na da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi milyan 4, cewar Marwa

Daga WAKILINMU Shugaban Hukumar Yaƙi da sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) Janar Muhammadu Buba Marwa, ya ce aƙalla mutum miliyan 4 da rabi ke mu’amala da miyagun ƙwayoyi a birnin Legas, abin da ke nuna ƙaruwar matsalar da ta addabi ƙasa baki ɗaya. Yayin da ya ke ziyarar gani da ido tun bayan naɗa shi a matsayin shugaban hukumar, Marwa ya bayyana birnin Legad a matsayin jihar da ake samun kashi 30 na masu amfani da miyagun ƙwayoyin. Ya ce daga cikin mutane miliyan 15 da aka yi ƙiyasin suna mu‘amala da miyagun ƙwayoyin wajen sha da…
Read More
Ba mu da tabbacin za a gudanar da Hajjin 2021 – NAHCON

Ba mu da tabbacin za a gudanar da Hajjin 2021 – NAHCON

Daga AISHA ASAS Hukumar Alhazan ta Nijeriya (NAHCON) ta ce kawo yanzu ba ta tabbacin ko za a gudanar da aikin hajjin bana, amma cewa tana kyautata zaton yiwuwar hakan. Bayan taron liyafar karrama sabon Jakadan Saudiyya a Nijeriya, Faisal bin Ibrahim Al-Ghamdi, NAHCON ta ce ba a kai ga sanya hannu na yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin ba kamar yadda aka saba amma hukumar a shirye take don fara aiki da zarar ta samu amincewa daga Gwamnatin Saudiyya. Hukumar ta ce dare da rana tana kan tsare-tsare na zaman ko-ta-kwana kan izinin gudanar da aikin da Hajji wanda hakan…
Read More
Kwara: An samu hatsaniya tsakanin Musulmi da Kirista saboda hana ɗalibai amfani da hijabi

Kwara: An samu hatsaniya tsakanin Musulmi da Kirista saboda hana ɗalibai amfani da hijabi

Daga UMAR M. GOMBE An samu rashin jituwa biyo bayan yadda iyaye mabiya addinin Kirista suka hana ɗalibai mata Musulmi shiga makarantar Sakandaren Baptist a babban birnin jihar Kwara, Ilori. Bayanai sun nuna cewa sakandaren na daga cikin goma da tun farko gwamnati ta rufe don hana fitina yayin da jihar ta bada dama ga mata musulmi da ke sha'awa su sanya hijabi in za su tafi makaranta. Gwamnatin ta nuna hakan shi ne zai tabbatar da zaman lafiya da fahimtar juna a tsakanin jama'ar jihar. Dakatar da ɗaliban da kiristoci suka yi, ya jawo ɗauki ba daɗi na jifa…
Read More
Ibadan: EFCC ta gurfanar da dattijo gaban kotu kan zambar kuɗin fili milyan N25

Ibadan: EFCC ta gurfanar da dattijo gaban kotu kan zambar kuɗin fili milyan N25

Daga WAKILINMU Hukumar Yaƙi da yi wa Tattalin Arziki Zagon Ƙasa da Zambar Kuɗaɗe (EFCC) ta shiyyar Ibadan, ta gurfanar da wani dattijo ɗan shekara 68 a gaban kotu bisa zargin zambar kuɗaɗen fili har naira milyan 25. EFCC ta gurfanar da Ezekiel Oluwadare James a gaban Mai Shari'a Patricia Ajoku ne kan laifuka guda biyu, wato haɗin baki da kuma samun kuɗi ba ta hanyar da ta dace ba. Wanda a cewar hukumar hakan ya saɓa wa sashe na 8(a) na dokokin zamba da sauran laifuka masu alaka da haka na 2006, wanda hakan ya cancanci horo a ƙarƙashin…
Read More
Buhari ya jinjina wa Uzodinma kan ayyukan cigaba

Buhari ya jinjina wa Uzodinma kan ayyukan cigaba

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, da ya ɗore da ayyukan cigaba da gwamnatinsa ke yi don kyautata rayuwar talakawan jiharsa. Talatar da ta gabata Shugaba Buhari ya yi wannan kira, tare da yaba ƙoƙarin Gwamna Uzodinma na kammala tarin ayyukan cigaba a tsakanin shekara guda. Buhari ya yi kalamansa ne ta bidiyo yayin ƙaddamar da wasu hanyoyi guda biyu a garin Owerri, babban birnin jihar waɗanda aka kammala aikinsu cikin shekara guda da gwamnan ya yi kan mulki. Buhari ya jinjina wa gwaman dangane da kammala hanyar Assumpta Cathedral…
Read More
Anambra: ‘Yan sanda sun bankaɗo gidan da ake safarar jarirai

Anambra: ‘Yan sanda sun bankaɗo gidan da ake safarar jarirai

Daga AISHA ASAS Rundunar 'yan sanda a jihar Anambra, ta ce ta gano wani gida da ake yi zargin ana safarar jarirai a cikinsa a Nnewi cikin ƙaramar Nnewi ta Arewa a jihar. Jami'in Hulɗa da Jama'a na Rundunar, CSP Haruna Muhammed ne ya bada sanarwar haka, yana mai cewa wadda ake zargin ita ce mai masana'antar jariran, Ms Gladys Nworie Ikegwuonu ta tsere sannan an kuɓutar da 'yan mata masu juna-biyu su huɗu. Jami'in ya ce sun yi nasarar kama wasu mutum biyu da ake zargin suna da alaƙa da harƙallar. Ya ci gaba da cewa sun gano masana'antar…
Read More
Hajjin bana: Indonesiya za ta kammala yi wa maniyyatanta rigakafin korona a Mayu

Hajjin bana: Indonesiya za ta kammala yi wa maniyyatanta rigakafin korona a Mayu

Daga WAKILINMU Babban Sakataren Ma'aikatar Lafiyar Ƙasar Indonesiya, Oscar Primadi, ya ce gwamnati na sa ran kammala yi wa maniyyatan Hajjin bana allurar rigakafin cutar korona a watan Mayu mai zuwa. Oscar ya faɗi haka ne yayin wani taron haɗin gwiwa tsakanin Ma'aikatar Harkokin Addini da Ma'aikatar Sufuri da kuma Majalisar Wakilai ta ƙasar, wanda ya gudana a ranar Litinin da ta gabata. A cewarsa, "Duba da yanayin shirin bada allurar, muna da tabbacin da yardar Allah za mu kammala yi wa maniyyatan Indonesiya rikagafin ya zuwa Mayu." Ya ƙara da cewa, sai waɗanda suka kammala biyan kuɗin tafiya Hajjin…
Read More