26
Feb
Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, yayi gargaɗin cewa babu wani sassauci game da matakan da gwamnati ta shirya ɗauka na neman kawar da matsalolin 'yan fashi da masu tada ƙayar-baya da sauran manyan laifuka da suka addabi al'umma a faɗin ƙasa. Buhari ya yi wannan gargaɗi ne ta bakin Shugaban Ma'aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Farfesa Ibrahim Gambari, yayin wani taro kan sha'anin tsaro wanda gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya suka gudanar a Jihar Kaduna. Buhari ya yarda cewa lallai Nijeriya na fama da matsalolin tsaro, amma cewa ya buƙaci sabbin shugabannin tsaro da samar da sabbin dabaru kuma…