Editor

9513 Posts
Kwara: Fahimtar juna game da hijabi

Kwara: Fahimtar juna game da hijabi

Daga IBRAHIM SHEME Sau da yawa, na kan yi mamakin yadda wasu ’yan Nijeriya ba su so a zauna lafiya; kullum ƙoƙari su ke yi su tsokano wata magana da za a dinga tada jijiyar wuya a kan ta. Dubi dai tataɓurzar da ake yi kan batun saka hijabi na ’yan makaranta mata Musulmi a Jihar Kwara. Wasu Kiristoci sun tashi haiqan a kan cewa ba su yarda mata ɗalibai su sanya hijabi su je makaranta ba. Abin da ya fi ba ni mamaki shi ne masu wannan kamfen ɗin ba wai wasu zauna-gari-banza kaxai ba ne, waɗanda za a…
Read More
Nijeriya ta shiga sahun ƙasashe mafiya haɗarin rayuwa – Ƙungiyar GTI

Nijeriya ta shiga sahun ƙasashe mafiya haɗarin rayuwa – Ƙungiyar GTI

Daga UMAR M. GOMBE Sakamakon ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga da sauran matsalolin tsaron da suka mamaye wasu sassan Nijeriya, Ƙungiyar dake sanya ido kan ayyukan ta’addanci ta duniya wato “Global Terrorism Index” (GTI), ta bayyana ƙasar nan a matsayin ɗaya daga cikin mafi haɗari wajen rayuwa a faɗin duniya. Rahoton ƙungiyor na shekarar 2020 da aka gabatar, ya nuna cewa an samu ƙaruwar hare-haren mayaƙan Boko Haram da kashi 25 cikin ɗari, yayin da kashe-kashen da ’yan bindiga ke yi kuma ya ƙaru da kashi 26 cikin ɗari, savanin waɗanda aka gani a shekarar 2019. “Ƙasashen da ke gaban Nijeriya…
Read More
Babban buri na shi ne in gina gidan marayu – Fauziyya D. Sulaiman

Babban buri na shi ne in gina gidan marayu – Fauziyya D. Sulaiman

Daga AISHA ASAS Sunan ki sananne ne, sai dai jin tarihin ki ne abin buƙatar masu karatu.Suna na Fauziyya D. Sulaiman. An haife ni a unguwar Fagge ta garin Kano a shekarar 1988. Na yi karatun Islamiyya a makarantar Maikwaru da ke Fagge da firamare ta ‘Festival Special Primary School’. Daga nan na tafi makarantar kwana ta ‘Yargaya inda na yi shekara uku, sannan na dawo makarantar ‘yan mata ta GGC Dala inda a nan na kammala karatu na. Daga nan na yi aure a 1999. A shekarar 2002 na koma karatu na yi difloma a ‘College of Hygiene’ a…
Read More

Duk inda aka san ni in har zan shiga zan samu karramawa fiye da hamshaƙan mutane – Ɗan Sarauta

Ɗan Sarauta Ibrahim Adam wanda yawancin mutane su ka fi sani da Ɗan sarauta, ya kasance wani baharu a fagen rubutacciyar waƙa da kuma waƙoƙin zamani na Hausa. A zantawar sa da jaridar Manhaja ya kwararo bayanin yadda ya tsinci kansa a fagen waƙa da rubuce-rubucen zube da sauran su. Sannan ya faɗi irin ƙalubalen da marubuta waƙa ke fuskanta. Ga dai yadda hirar ta kasance, domin an ce waƙa a bakin mai ita ta fi daɗi. Daga AISHA ASAS a Abuja Mu fara da jin tarihin ka.Suna na Ibrahim Adam, amma an fi sani na da Ɗan Sarauta. An…
Read More
Sai an fifita harkar tsaro sannan Nijeriya za ta inganta – Shugaban NRI

Sai an fifita harkar tsaro sannan Nijeriya za ta inganta – Shugaban NRI

Daga JABIRU A. HASSAN a Dutse Shugaban Ƙungiyar Farfaɗo da Martabar Arewa da Kyautata Haɗin Kan Ƙasa ta “Northern Reformation and National Unity Initiative” (NRI), Alhaji Abubakar Adamu Haɗejia ya buƙaci ɗaukacin al'ummar Nijeriya da su bai wa sababbin hafsoshin tsaro cikakken haɗin kai da goyon baya, ta yadda za su cimma dukkanin nasarorin da ake buƙata domin kyautata zaman lafiya da kwanciyar hankali a wannan ƙasa. Abubakar Haɗeja, ya yi wannan kira ne a ganawar su da wakilin mu a birnin Dutse, inda kuma ya sanar da cewa idan ’yan Nijeriya suka bada goyon baya da haɗin kai ta…
Read More
Ƙungiyar Fulani ta yaba wa Gwamna Buni bisa kafa ginshiƙin fahimtar juna

Ƙungiyar Fulani ta yaba wa Gwamna Buni bisa kafa ginshiƙin fahimtar juna

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta ‘Kulen Allah Cattle Rearers Association Of Nigeria’ (KACRAN) yaba wa Gwamnan Jihar Yobe kuma Shugaban Riƙo na Jam’iyyar APC na Ƙasa, Hon. Mai Mala Buni bisa kafa ginshikin samar da fahimtar juna tsakanin makiyaya da manoma a jihar Yobe. Shugaban Ƙungiyar na Ƙasa, Hon. Khalil Mohammed Bello ne ya bayyana haka ga manema labarai a Damaturu ranar Talatar da ta gabata, inda ya buƙaci sauran gwamnatocin ƙasar nan su yi koyi da irin manufofin Gwamnatin Jihar Yobe a ƙarƙashin Gwamna Buni. Hon. Khalil, ya fara da yaba wa Gwamnan na Yobe…
Read More

Hare-haren Boko haram ya raba mutane sama da miliyan biyu da muhallin su – Rahoto

Daga MUAHAMMAD AL-AMEEN A wani rahoto da Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, ya bayyana cewa hare-haren mayaƙan Boko Haram sun raba mutane sama da miliyan biyu da muhallin su a Arewa-maso-Gabas, ya kuma haifar da lalacewar kayan more rayuwa da wahalar samun kula da lafiya ga mutanen da suka tsere daga gidajen su. Rahotan ya ƙara da cewa ƙungiyoyin jinƙai da yawa sun damu da halin da mutanen yankin ke ciki, inda waɗan su suka yi ƙoƙarin janyo hankali kan tavarɓarewar al’amura ganin yadda annobar korona ta ɗauke hankalin duniya a halin da ake ciki. Masu aikin jinƙai sun bayyana…
Read More
Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Imo: Kotu ta umurci INEC ta tabbatar da Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi

Daga WAKILINMU Wata Babbar Kotu a Abuja, ta umurci Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) da ta bayyana Chief Ifeanyi Ararume a matsayin wanda ya lashe zaɓen maye gurbi na mazaɓar Imo ta Arewa wanda aka gudanar ran 5, Disamb, 2020 a jihar Imo. Alƙali Taiwo Oladipupo Taiwo shi ne wanda ya yanke wannan hukunci inda ya ce kotu ta hanzarta ta tabbatar da Ararume na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar. Kazalika, alƙalin ya bai wa INEC odar ta miƙa wa Ararume takardar shaidar lashe zaɓe cikin sa'o'i 72 daga lokacin da…
Read More

Matsalolin ilmi a Jihar Kano

Gwamna Ganduje Daga FATUHU MUSTAPHA Ilmi na cikin vangarorin rayuwa da ya zamewa ɗan Adam tilas ya ba shi kulawa ta musamman. A yau Ƙasar nan tana fuskantar manyan matsaloli kama daga matsalar tsaro da a kullum ke ƙara ta'azzara, zuwa matsalar fatara da talauci, lalaci da jahilci da kuma karyewar tattalin arzikin ƙasa, wanda a ka fara sa ran zai iya farfaɗowa nan da wasu lokuta masu zuwa. Babu inda matsalolin nan suka fi nunawa kan su irin a Arewacin Nijeriya. Inda anan ne aka fi yawan yaran da basa zuwa makaranta, yawan yaran da basa cin jarabawar gama…
Read More
Gwamnatin Tarayya da Nasarawa za su yi aiki tare wajen kare yankunan haƙo ma’adinai

Gwamnatin Tarayya da Nasarawa za su yi aiki tare wajen kare yankunan haƙo ma’adinai

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Nasarawa sun shirya yin aiki tare domin kare yankuna masu arzikin zinari a jihar Nasarawa da kuma kare iyakokin Abuja da Nasarawa. Ministan Bunƙasa Ma'adinai, Architect Olamilekan Adegbite, shi ne ya bayyana hakan sa'ilin da ya karɓi baƙuncin Gwamna Abdullahi Sule a ofishinsa da ke Abuja a Talatar da ta gabata. A cewar Ministan Gwamnatin Tarayya ta kashe maƙudan kuɗaɗe har biliyan N15 kan harkokin ma'adinai a sassan ƙasa ƙarƙashin shirinta na aikin binciko inda arzikin zinari yake a Nijeriya inda ta gano hakan tsakanin Jihar Nasarawa da Abuja.…
Read More