Babaji

4778 Posts

Yadda Gwamna Abba ya biya wa Zainab, ‘yar Ado Bayero, da mahaifiyarta kuɗin haya a Legas

Daga Adnan Muktar Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya biya kuɗin hayar gida ga Zainab, ƴar marigayi tsohon Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero da mahaifiyarta, biyo bayan barazanar korar su daga gidan da su ke da aka yi a Legas. Mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature ya ziyarci wajen da su ke a rukunin gidajen 'Morning Side Suits' da ke Victoria Island a ranar Talata, 25 ga watan Yuni, 2024 which a ranar ƙudinsu zai ƙare da misalin ƙarfe 3 na rana inda har ta kai ga an basu takardar ficewa daga gidan, wato 'notice', sannan ya gana…
Read More

Gwamnoni sun kira taron gaggawa kan batun mafi ƙarancin albashi ga ma’aikata

Daga Farouk Abbas Gwamnonin Jahohi 36 na ƙasarnan zasu gudanar da taron gaggawa a yau, Laraba kan batun sabon mafi ƙarancin albashi da za a ke biyan ma'aikata a Najeriya. A kwanakin baya ne gwamnonin suka ƙi amincewa da tayin dubu 62 da gwamnatin tarayya ta yi inda suka ce amincewa da hakan zai sa sai wasu gwamnonin sun ciyo bashi kafin su iya biya. Sai dai ita kuma haɗaɗdiyar ƙungiyar ƙwadago tana kan bakanta na buƙatar ake biyan naira dubu 250. Taron gwamnonin na zuwa ne sakamakon ficewa daga batun da majalisar ministoci ta shelanta a jiya inda ministan…
Read More

NLC ta kira taron gaggawa kan cire hannu da FEC ta yi a batun mafi ƙarancin albashi

Daga Farouk Abbas Mambobin haɗaɗɗun ƙungiyoyin ƙwadago sun kira taron gaggawa jim kaɗan bayan da majalisar ministoci (FEC), ta sanar da cire hannunta kan batun mafi ƙarancin albashi da ake yi a Najeriya. Wani babban ma'aikacin ƙwadago ya ce za a gudanar da taron ne a ranar Laraba, 26 ga watan Yuni, a babban ofishin NLC, a ɗakin taro na 'Labour House' da misalin ƙarfe 10 na safe. Ma'aikacin ya bayyana cewa, za a yi taron ne musamman saboda hukuncin majalisar ministoci na cire hannu kan tattauna a batun mafi ƙarancin albashi ga ma'aikata da ake tataɓurza a kai da…
Read More

Majalisar Ministoci ta cire hannunta kan batun mafi ƙarancin albashi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Majalisar ministoci (FEC), ta ce ta janye daga tattaunawa kan batun mafi ƙarancin albashin ma'aikata, domin bai wa shugaba Bola Ahmed Tinubu damar cigaba da neman shawarwari da masu-ruwa-da-tsaki kan batun. Ministan harkokin yaɗa labarai da haɗin kan ƙasa, Idris Mohammed ya faɗi hakan a yayin hira da wakilan fadar gwamnatin tarayya dake Abuja a ranar Talata. Idris ya ce, shugaba Tinubu ya yi nazari kan rahoton kwamitoci uku na tattaunawa kan batun mafi ƙarancin albashin, sannan kuma zai yi shawara da waɗanda lamarin ya shafa kafin miƙa sabon mafi ƙarancin albashin ma'aikata ga majalisar ƙasa.…
Read More

Gwamnan Sakkwato ya musanta shirin tuɓe Sarkin Musulmi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmad Aliyu ya musanta zargin da ƙungiyar ƴancin musulmin Najeriya (MURIC), ta yi na cewa yana shirin tuɓe Sarkin musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar na III daga kujerarsa. A kwanakin baya ne babban daraktan MURIC, Farfesa Isiaq Akintola ya tada batun, inda ya ce gwamnati Jihar na shirin korar Sultan Sa'ad Abubakar daga muƙaminsa la'akari da rikicin Masarauta da ke cigaba da aukuwa a Jihar Kano. Farfesan ya yi gargaɗin cewa, al'ummar musulmi a Najeriya ba za su amince da hukuncin sauke Sarkin ba inda ya ce Sarki Sa'ad ba Sarkin gargajiya ba…
Read More

A guji amfani da maganin ‘B-GAG’ – Hukumar NAFDAC

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Hukumar kula da dokar abinci da magunguna ta ƙasa (NAFDAC), ta yi kira ga ƴan Najeriya da su guji saya ko amfani da wani magani mai suna 'B-GAG' na ruwa, sakamakon shiga kasuwa da ya yi ba tare da cike ƙa'idoji ko yin rijista da hukumar ba. Bayanin ya fito ne daga ofishin darakta Janar ta hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye a wata takardar sanarwa mai lamba 023/2024 a ranar Lahadin da ta gabata inda ta ce, ana sayar maganin wanda ba a tantance ko yi masa rijista ba daga wani kamfani mai suna 'Babban Gida Agalawa…
Read More

Iyalan ɗalibin sekandiren NAF da aka kashe sun buƙaci a yi adalci

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Iyalai da wakilan cocin wani mataimakin shugaban daliban makarantar sekandire ta rundunar sojin sama (NAF) da ke Kaduna, Felix Blaise da aka kashe, sun buƙaci hukuma da ta yi adalci yayin binciken kisan Ɗalibin mai shekaru 15, ɗan aji biyar, ana zargin an kashe shi ne a ɗakin kwanan ɗalibai inda wata jarida ta yanar gizo ta ce wasu ɗalibai su biyu ƴan aji shida ne suka sa masa lantarki wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwarsa. NAF ta ce, tana cigaba da bincike kan lamarin domin gano haƙikanin abun da ya faru. Haka nan, wakilin cocin…
Read More

‘Yan sanda sun kama mutum huɗu da ake zargi da hannu a kisan wani babban soja

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rundunar Ƴan sanda ta kama wasu mutane huɗu da ake zargi kan kisan tsohon shugaban rundunar soji na ƙasa kuma jami'i Mai ritaya, Burgediya Janar, Harold Udokwere. Jaridar 'Blueprint' ta ruwaito cewa an kashe babban sojan ne a gidansa dake layin Sanga, a rukunin gidajen Sunshine, a unguwar Lokogoma dake Abuja a yayin wani fashi da wasu ƴan bindiga suka kai yankin. An samu bayanin ne a wani faifan bidiyo da ke ɗauke da rubutu inda waɗanda aka kama sun haɗa da; Ibrahim Rabi'u, mai shekaru 33 daga Ƙaramar Hukumar Dala, Jihar Kano mazaunin Rasha Apo…
Read More

Rikicin Masarauta-Rundunar Ƴan sandan Kano ta kori masu gadi a fadojin da Sunusi da Aminu suke tare da ƙara jami’ai

Daga Farouk Abbas Rundunar Ƴan sandan Jihar Kano ta aika da ƙarin jami'anta zuwa fadojin da Sarki Sunusi Lamido Sunusi da kuma Sarki Aminu Ado Bayero su ke, biyo bayan ɗar-ɗar na faruwar rikici a yankunan Masarautun. Tuni dai mafarauta da sauran masu gadin Masarautun suka bar fadojin a lokacin da jami'an suka isa, don inganta tsaro ga rayuka da dokiyoyin al'ummar yankunan. Kwamishinan Ƴan sandan Jihar, Usiani Gumel ya tabbatar da haka yayin ganawa da manema labarai inda ya ce sun ɗauki matakin ne domin tabbatar da wadataccen tsaro a faɗin Jihar. Usaini Gumel ya ce "an tura jami'ai…
Read More

An gano kadarorin naira tiriliyan 1.49 a Dubai, mallakar ƴan Najeriya ciki har da El-Rufa’i da ƴar Atiku da Baba Ahmad da sauransu

Daga Edita Cikin shekaru huɗu, adadin ƴan siyasar da asirin su ya tuno a Najeriya (PEPs), ya ninka inda a shekarar 2020, bincike ya nuna cewa gidaje 800 da ƙudinsu ya kai dala miliyan 400 a Dubai da ke ƙasar Haɗaɗdiyar Daular Larabawa mallakan ƴan Najeriya ne wanda kuma a shekarar 2024 sun kai kimanin mutum 1,600 wanda kuɗin su ya kai kusan dala biliyan 1. Tawagar aikin bincike kan rahoton laifukan sata da almundahana da dukiyar al'umma (OCCRP), ita ce ta gudanar da binciken tare da gidajen jaridu guda 70 yayin da Jaridar 'Economy Post' ta wakilci Najeriya. Rahoton…
Read More