28
Jun
Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙasashen Saudiya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, sun sanar da rage adadin lokacin gudanar da huɗubobin sallar jumma'a a masallatai saboda tsananin zafin rana da su ke fama da shi. Al'ummar musulmi a ƙasashe da dama na duniya kan gabatar da sallar jumma'a ne da rana wacce masallata ke zama domin sauraron ta ciki da wajen masallaci da wuraren da babun rumfuna, don haka ƙasashen biyu suka yanke hukuncin hakan domin sauƙaƙa mu su kamar yadda addinin Musulunci ya karantar. Shugaban ma'aikatar kula da harkokin addini na ƙasar Saudiyya ya ce, sun rage adadin lokacin huɗubar zuwa…
