Babaji

4780 Posts

Annobar Kwalara ta ɓarke a kurkukun Kirikiri, yayin da mutane 118 suka kamu a Katsina

Daga FAROUK ABBAS Kwamishinan lafiya na Jihar Legas, Farfesa Akin Abayomi ya ce sun samu rahoton mutane 25 da ake zargin suna ɗauke da cutar ƙwalara daga gidan yarin Kirikiri. Hakan na zuwa ne bayan da hukumar kula da gidajen yari (NCS) ta fitar da bayanin cewa babu mai ɗauke da cutar a gidan kurkukun a makon da ya gabata. Mai magana da yawun hukumar, Abubakar Umar ya ce sun ɗauki matakan kariya wajen ganin ba a samu ɓullar kwalara a gidan yarin ba. Sai dai, ma'aikatar lafiya ta jihar Lagos ta offishin jami'in hulɗa da jama'a, Tunbosun Ogunbawo ta…
Read More

Shugaba Tinubu ya yi wa Sanata Ali Modu Sheriff ta’aziyyar rasuwar mahaifiyarsa

Daga Abdullahi Maitama Sani Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aika saƙon ta'aziyyarsa ga tsohon gwamnan Jihar Barno, Sanata Ali Modu Sheriff kan rasuwar mahaifiyarsa, Hajiya Aisha. Za a gudanar da jana'izar Hajiya Aisha da ta rasu da shekaru 93 a gidansu na marigayi Galadima Modu Sheriff da ke kan hanyar Damboa a Maiduguri, babban birnin Jihar Barno. Wata sanarwa da ta fito daga mai taimaka wa shugaban ƙasa kan harkokin yaɗa labarai, Ajuri Ngelale, ta ce shugaba Tinubu na jajenta wa iyalan Sanatan kan babban rashin da aka yi mu su, yana mai rarrashin su tare da addu'ar fatan samun…
Read More

Rundunar ‘Yan sandan Abuja ta bayar da umarnin kama motoci marasa lamba

Daga EDITA Hukumar 'Yan sandan a birnin tarayya Abuja, ta bayar da umarnin kama duka motoci marasa lamba da ke yawo a faɗin birnin. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, ASP Josephine Adeh ta fitar, ta ce kwamishin 'Yan sandan birnin, CP Benneth C. Igweh ne ya bayar da umarnin don kakkaɓe ayyukan ɓata-gari da ke fakewa da tuƙin mota suna cutar da al'umma. “Rundunar 'Yan sandan birnin Abuja ta damu matuƙa kan yadda ake tuƙa wasu motoci a birnin da lamba ɗaya kacal a jikinsu, da ma waɗanda ba su da lambar har fiye da lokacin da doka ta…
Read More

Yadda Sarki Sanusi ya karɓi baƙoncin Gwamnan Zamfara

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi na II ya karɓi baƙoncin Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawan a fadar Sarkin da ke Gidan Rumfa, wanda haka ke nuna ƙarfin alaƙar da ke tsakaninsu. Alaƙar tasu ta samo asali ne tun lokacin da Sarki Sanusi ke gwamnan babban bankin Nijeriya inda Dauda Lawan shi ne mai bashi shawara na musamman kan harkar bankin musulunci, wanda hakan ya taimaka wajen ƙirƙirar bankunan Ja'iz da TAJ da kuma Lotus gami da samar da tsare-tsare masu kyau a harkar banki. Dauda Lawan, ya yi abin a yaba a harkar banki a…
Read More

Gwamnan Kano ya buƙaci a binciki Ganduje kan rage kuɗaɗen tsofaffin ma’aikata

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya roƙi a yi bincike kan zargin rage kuɗaɗen giratuti na tsofaffin ma'aikata ƙarƙashin gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje. A lokacin da ya ke jawabi a bikin ƙaddamar da zango ba biyu na biyan giratuti da na ma'aikatan da suka mutu, Abba ya ce akwai Naira biliyan 5 da aka rage na ƴan fansho mutum 4,000 cikin kuɗin wanda babu bayanai a kan su, don haka ya buƙaci hukumar da ke da alhaki a kai, ta yi bincike. Abba ya shawarci ƙungiyar ƴan fansho ta ƙasa (NUP), da ta shigar da…
Read More

Yadda wasu maƙiya su ka shirya bayanan ƙarya a kan ɗan jarida, Shuaibu Mungadi

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Shuaibu Mungadi ɗan jarida da ke aiki a gidan telebijin na Farin wata wanda ya tsinci kansa a wani mummunar yanayi, biyo bayan da wata kafa mai suna 'Zamfara News Letter' ta ruwaito cewa ana zarginsa da yi wa ƙawar ƴarsa ciki. Wannan labari ya ɗauki hankalin mutane kasancewar hakan abu ne da zai ɓata sunansa a cikin al'umma. Wani bincike da kafar ta yaɗa daga wasu ƴan siyasa waɗanda ke harin mutanen da suka saɓa da su wajen ra'ayi, ya ce, Mungadi ya ƙulla mummunar alaƙa da ƴar Maijidda Labaran wanda haka ta kai ga…
Read More

Rundunar soji ta kama mutum 47 kan satar turakun hanyar jirgin ƙasa a Kaduna

Daga BALA MUHAMMAD Rahotanni daga Jihar Kaduna na cewa, jami'an soji sun yi nasarar kama mutum 47 da ake zargi da satar turakun hanyar jirgin ƙasa a yanki Kakau Daji, a anguwar Ayaba da ke ƙaramar hukumar Chikun na jihar Kaduna. Mataimakin kakakin rundunar na yankin, Laftanal Musa Yahaya, ya ce jami'ansu sun kama waɗanda ake zargi ne a lokacin da su ke gudanar da wani zagaye a ranar 26 ga watan Yuni, 2024. Ya ce, waɗanda ake zargin sun cika motoci guda biyu da kayayyakin turakun hanyar yayinda aka kama su, sannan binciken su ya ce, wani mai suna…
Read More

Yadda haɗarin tirela ya halaka mutum 19 da raunata wasu a Kano

Daga KHALIFA MUHAMMAD Wata babbar mota ɗauke da kaya ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 19 biyo bayan ƙwacewa da ta yi a garin Imawa da ke ƙaramar hukumar Kura, a Jihar Kano. Haɗarin, ya faru ne a ranar juma'a yayinda wasu masallata ke kan hanyar komawa gida bayan gabatar da sallar juma'a inda nan take ya yi sanadiyyar mutuwar mutane goma sha huɗu tare da raunata wasu da dama. A lokacin da yake jawabi, Kwamandan reshen jihar Kano na hukumar kula da haɗurra ta ƙasa (FRSC), Ibrahim Abdullahi, ya ce sun tabbatar da aukuwar lamarin wanda ya faru da misalin…
Read More

Dalilin tashin farashin wake a Nijeriya

Daga ABUBAKAR ABBA Tsadar farashin wake ya jefa fargaba a zukatan mutane da dama a Nijeriya wanda har yanzu ke ci gaba da haifar da cece-kuce. Jaridar 'Leadership' ta ruwaito cewa, tashin farashin waken na ƙoƙarin wuce gona da iri, wanda a tarihi ba a taba ganin irinsa a faɗin wannan ƙasa ba. Har ila yau, manoman sun danganta tsadarsa da abubuwa da dama da suka shafi nomansa a Nijeriya. Kungiyar manoman farin wake ta ƙasa (CFAN), ta sanar da cewa, ana ɗaukar mataki don lalubo mafita a kan wannan hauhawar farashi a faɗin wannan ƙasa. Shugaban ƙungiyar na kasa…
Read More

DA ƊUMI-ƊUMI: ‘Yan sanda sun kama waɗanda ake zargi da sace mahaifiyar Mawaƙi Rarara

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Rahotanni daga Jihar Katsina sun ce Rundunar 'Yan sandan jihar ta kama mutum biyu da ake zargin su da hannu a garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Dauda Ƙahutu Rarara, Hajiya Ibrahim. Kakakin Rundunar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu, ya ce ana cigaba da binciken waɗanda aka kama, a ƙoƙarinsu na ceto ta. A yau juma'a ne aka yi garkuwa da Hajiyar mai kimanin shekaru 75 a ƙauyen Kahutu dake Ƙaramar Hukumar Danja, a Jihar Kastina da misalin ƙarfe 1:30 na rana. Wannan wani huɓɓasa ne da rundunar 'Yan sandan ta yi wajen ganin an daƙile ayyukan garkuwa da…
Read More