Babaji

4782 Posts

Majalisar wakilai za ta ƙirƙiro ƙarin jiha a kudu-maso-gabashin Nijeriya

Daga EDITA Majalisar wakilan Nijeriya ta gabatar da ƙudurin ƙirƙiro ƙarin jiha guda da za a kira jihar Etiti a yankin kudu maso gabashin ƙasar. Ƙudirin, wanda Amobi Godwin Ogah tare da wasu ƴan majalisa huɗu suka gabatar, ya tsallake karatu na farko a majalisar ranar Talata. Ƙudurin na buƙatar yin gyara a sashe na uku na kundin tsarin mulkin ƙasa, domin goge lamba ta 36 tare da maye gurbinta da lamba 37 don bai wa sabuwar jihar damar shiga jerin jihohin ƙasar, sannan a saka Etiti bayan Enugu cikin jerin sunayen jihohin ƙasar. Sabuwar jihar da za a yanka…
Read More

‘Muna so Nijeriya ta fara amfani da fasaha don kawar da ‘yan bindiga’- Majalisar Dattijai

Daga BUHARI FAGGE Majalisar Dattijan Nijeriya ta nemi gwamnatin tarayya ta koma amfani da fasahar zamani a yaƙin da take yi da mayaƙan Boko Haram da ƴan bindiga. Hakan na ƙunshe cikin ƙudurin da Sanata Ali Ndume ya gabatar don ɗaukar matakin gaggawa kan harin da aka kai a yankin Gwoza da yake wakilta. Bayan doguwar muhawara da aka kwashe sa'o'i ana yi tare da jajentawa kan harin, majalisar ta yarda cewa amfani da fasahar zamani a yaƙin zai kawo ƙarshen masu kai hare-haren ƙunar baƙin wake. BBC Hausa ta ruwaito cewa, Majalisar ta amince a ƙara bayar da muhimmanci…
Read More

Kotu ta yanke wa masu garkuwa hukuncin kisa ta hanyar rataya

Daga EDITA Wata babbar kotun jiha da ke zamanta a Osun ta yanke wa wasu masu garkuwa biyar hukuncin kisa ta hanyar rataya, bayan samunsu da laifin sace wani mutum mai suna Alhaji Ibrahim Adamu, tare da kashe shi. An gurfanar da mutanen biyar a gaban alƙali bisa tuhume-tuhume da suka ƙunshi haɗa baki don yin garkuwa da mutumin da kuma laifin kisan kai, zargin da suka musanta a lokacin da aka fara gurfanar da su ranar 28 ga watan Oktoban 2021. Jaridar 'BBC Hausa', ta ruwaito cewa a lokacin zaman sauraron shari'ar, lauyan gwamnati, Faremi Moses, ya gabatar da…
Read More

‘Yan bindigar da su ka sace mahaifiyar Rarara sun ce a biya Naira miliyan 900

Daga YUSHAU A IBRAHIM Waɗanda suka yi garkuwa da mahaifiyar mawaƙi Dauda Kahutu Rarara sun ce a bada Naira miliyan 900 a matsayin kuɗin fansa don sako ta. Wani makusancin ahalin, wanda ya buƙaci a ɓoye sunansa, ya shaida wa jaridar 'Daily Trust' cewa ƴan bindigar da farko sun ce Naira biliyan 1 za'a biya, daga baya kuma sai suka rage miliyan 100 a wata hirar waya da aka yi da ɗaya daga cikin iyalanta. Bayan garkuwa da ita ne, Rarara ya fara rashin lafiya, don haka sai suka amince da tattauna da wani daga cikin ƴan gidan inda suka…
Read More

‘Tapswap’ ta sake dakatar da bada lasisin shiga

Daga AMINA IBRAHIM Manhajar Tapswap wacce ɗaya daga manyan kafofin 'Blockchain' ce ta ce ta dakatar bada lasisin shiga zauren cinikayya ga masu amfani da ita. Tapswap dai ya samu karɓuwa a cikin ƴan Nijeriya inda a yanzu haka aƙalla mutane sama da miliyan 50 ke amfani da shi tun ƙaddamar da shi a watan Fabrairun 2024. Hukumar kula da manhajar ta ce ta dakatar lasisin cinikayyar ne da aka tsara zai da fara aiki daga 1 ga watan Yuli domin sauƙaƙe wa masu amfani da shi a zango na uku bisa huɗu. Ta kuma ƙara jaddada ƙoƙarinta na inganta…
Read More

‘Yan bindiga sun kashe malamin jami’a da garkuwa da ʼyaʼyansa a Katsina

Daga SANI NURA Ƴan bindiga sun kashe wani malamin jami'ar gwamnatin tarayya ta Dutsinma da ke jihar Katsina. Malamin, mai suna Dakta Gyan David wanda shi ne shugaban tsangayar tattalin harkar noma da raya karkara, an kashe shi ne da asubahin ranar Talata da misalin ƙarfe 1:30 a gidansa da ke unguwar rukunin gidajen Low-Coast yayin wani sabon hari da ƴan bindiga suka kai a ƙaramar hukumar Dutsinma a jihar Katsina. Jaridar 'News Point Nigeria' ta ruwaito cewa, ƴan bindigan sun shigo yankin ne da wasu muggan makamai inda suka yi ta harbe-harbe domin su tsorata mutane, sannan sun kuma…
Read More

Sarkin Katsina ya jagoranci sallar roƙon ruwa

Daga SANI NURA da BELLO ABUBAKAR BABAJI Sarkin Katsina, Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya jagoranci dandazon mutane sallar roƙon ruwa a jihar Katsina. An gudanar da sallar ne a safiyar ranar Alhamis a filin Idi biyo bayan shafe kwanaki 16 da aka yi ba a yi ruwa ba. Limamin babban masallacin Katsina, Imam Gambo Mustapha shi ya yi limancin sallar inda al'umma ta yi kira ga sauran ƴan jihar da su yi irin ta a sassa daban-daban na faɗin Jihar. Masallatan sun ce an yi hakan ne ganin yadda amfanin gona ke bushewa tare da fuskantar barazanar lalacewa saboda ɗaukar…
Read More

Gwamnati ta yafe wa manoma da ƙananan masana’antu harajin da ake bin su

Daga HAMZA RUFA'I Gwamnatin tarayya ta ce ta yafe harajin da take bin manoma da ƙananan masana'antu biyo bayan gyare-gyaren da aka yi wa tsarin biyan haraji a Nijeriya. Shugaban kwamitin shugaban ƙasa kan tsarin kuɗi da gyaran haraji, Taiwo Oyedele ya faɗi hakan cikin wata sanarwa inda ya ce an ƙaddamar da sabon tsarin biyan haraji wanda zai warware matsalolin kuɗaɗen haraji da ake bi bashi ciki har da ƙananan masana'antu da manoma. Oyedele, ya ce an fara aiki da tsarin kuɗin harajin da ake bi bashi ne a shekarar 1977 wanda an yi shi ne domin samar da…
Read More

Safarar ƴan ƙunar baƙin wake a ka yi a Borno – Majalisar Wakilai

Daga FAROUK ABBAS Majalisar Wakilai ta ce tana zargin an yi safarar ƴan matan da suka ƙaddamar da ƙunar baƙin wake ne a jihar Borno wanda ya yi sanadiyyar rasa rayuka da dama a ranar Asabar da ta gabata. Wakilin Majalisar, Ahmed Jaha a yayin magana kan wani batu na gaggawa game da al'amarin a Majalisar, ya ce bincike ya nuna cewa an yi hayar ƴan ƙunar baƙin waken ne daga wajen jihar Borno. Sannan, aikin tada bom ɗin wanda ya faru a Gwoza, an samu aƙalla mutane sama da 30 ne su ka rasa rayukansu tare da raunata sama…
Read More

Kotu ta buƙaci EFCC ta biya tarar Naira miliyan 3 kan shelanta kama matar Emefiele ba bisa ƙa’ida ba

Daga HAMZA RUFA'I Wata babbar kotu a jihar Lagas ta ce ba daidai ba ne shelanta neman kama matar tsohon gwamnan babban bankin Nijeriya, Godwin Emefiele, Margaret da hukumar hana yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa da laifukan da su ka shafi kuɗi (EFCC) ta yi. Mai Shari'a, Deinde Dipeolu ya faɗi hakan bayan da Magaret Emefiele ta shigar da ƙara kan EFCC da a bi mata haƙkinta inda kotun ta buƙaci hukumar da ta biya tarar Naira miliyan uku ga daƙile ƴancin matar. Magaret, ta shigar da ƙarar ne ganin yadda hukumar ta wallafa hotunanta a shafukan EFCC…
Read More