Babaji

4776 Posts

Ministan yaɗa labarai zai jagoranci buɗe taron tallace-tallace na 2024 a Legas

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Za'a gudanar da taron ne a ranar Alhamis, 27 ga watan Yuni, inda manyan mahlarta taron suka haɗa da ministan yaɗa labarai da haɗin kan ƙasa, Idris Muhammed wanda shi ne shugaban taron da shugaban hukumar hana fatauci da miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA), Janar Buba Marwa Mai ritaya da wanda ya ƙirƙiri cibiyar kimiyyar 'Data' ta ƙasa, Dakta Bayo Adekanbi da kuma babban sakataren ofishin kula da kuɗaɗen makarantun gaba da sekadire, 'ARC.' Sonny Echono da sauran su. Hukumar kula da harkokin tallace-tallace ta ƙasa (ARCON) ta shirya taron inda shugaban NDLEA, Buba Marwa zai…
Read More

“Kar ka sauke Sarkin Musulmi”- MURIC ta gargaɗi Gwamnan Sakkwato

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Ƙungiyar kare ƴancin al'ummar musulmin Najeriya (MURIC), ta gargaɗi gwamnan Jihar Sakkwato, Aliyu Ahmad cewa kar ya sauke Sarkin Musulmi, Sultan Sa'ad Abubakar, daga kan muƙaminsa. MURIC ta yi wannan gargaɗi ne biyo bayan da gwamnan ya sauke sarakunan gargajiya guda 15 a faɗin Jihar watanni biyu da suka wuce inda jita-jitar sauke Sarkin Musulmin ke yawo wanda hakan ya sa ƙungiyar ta nuna damuwa tare da kira ga gwamnan da ya guji duk wani yunƙuri na sauke Sarkin Musulmi daga kujerarsa. Daraktan ƙungiyar, Farfesa Ishaq Akintola ya faɗi hakan cikin wata sanarwa da ya fitar…
Read More

An buƙaci gwamnan Kano da ya sauka daga kan kujerarsa-Rikicin Masarauta

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Wata tawagar al'ummar Jihar Kano ta yi kira ga gwamnan Jihar, Abba Kabir Yusuf da ya sauka daga kan kujerar shugabancin Jihar domin martaba doka da oda. Wani mamban tawagar mai suna Muhammad Bello ya faɗi hakan cikin wata sanarwa, inda ya ce sun yi kiran ga gwamnan ne sakamakon ƙin biyayya ga hukuncin da kotu ta yi na rushe cancantar zaman Sunusi Lamido Sunusi a matsayin halstaccen Sarki. Bello ya ƙara da cewa, ƙin amincewa da hukuncin Alƙali Abdullahi Liman a babbar kotun tarayya ga gwamnan, alama ce dake nuna cewa yana rashin ladabi ga…
Read More

Gwamnatin Kano ta bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin ficewa daga fadar Nasarawa

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJIGwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya aika wa saukakken Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero takardar ficewa daga fadar Nasarawa inda nan ne Sarkin ya ke zama tun bayan da aka sauke shi.Gwamnan ya yi hakan ne, yana mai cewa za su yi wasu gyare-gyare ne a fadar inda ya ce "bai dace Aminu Ado ya cigaba da zama a fadar ba" la'akari da rikicin Masarautar Jihar da ke cigaba da aukuwa.A ranar Asabar da ta gabata ne, gwamnan ya sa hanu a kan kuɗi da adadin ya kai kusan kimanin naira miliyan 100 kan gyaran da…
Read More

Ƴan sanda sun ƙaddamar da binciken kisan tsohon janar a Abuja

Daga Buhari Aliyu Muhammad Kwamishinan 'yan sandan birnin tarayya Abuja, Benneth Igweh, ya bayar da umurnin gudanar da binciken kisan da wasu da ake zargi 'yan fashi ne suka yi wa wani tsohon Janar a gidansa da ke Abuja. Maharan sun kutsa gidan marigayin - Burgediya Janar Uwem Udokwere mai ritaya inda suka kashe shi. Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan Abuja, ASP Josephine Adeh ta fitar, ta ce an kashe tsohon janar ɗin a gidansa da ke rukunin gidajen 'Sunshine' a unguwar Lokogoma da ke birnin tarayyar, ranar Asabar da tsakar dare. Kwamishinan 'yan…
Read More

Za a fara cirar kuɗi da katin ɗan ƙasa a watan Agusta-NIMC

Daga Khadija Abubakar Hukumar kula da katin zama ɗan ƙasa (NIMC), ta ce nan da watanni biyu za ta inganta katin zama ɗan ƙasa ta yadda zai ke amfani guda uku ga masu shi. Wani jami'in hukumar da bai yadda a faɗi sunansa ba ya sanar manema labarai hakan a ranar Juma'a, inda ya ce kati zai fara amfani a matsayin shedar zama ɗan ƙasa, da ɓangaren cirar kuɗi kamar katin 'ATM' sannan da kuma wasu harkokin rayuwa. Ya ƙara da cewa, hukumar tana iya ƙoƙarinta wajen cimma hakan, domin kuwa a halin yanzu, ta fara gwajin yiwuwar haka, dan…
Read More

Kotu ta bada umurnin riƙo na din-din-din ga kadarorin naira biliyan 12 da ke da alaƙa da Emefiele

Daga Sadiq Muhammad Wata babbar kotun tarayya dake Jihar Legas, ta jaddada cewa, za a cigaba da riƙe kadarorin gwamnatin tarayya da aka ƙwace a hannun tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, Godwin Emefiele waɗanda adadinsu ya kai sama da naira biliyan goma sha biyu. Mai Shari'a Chukwujekwu Aneke, ya yi hukuncin biyo bayan da wani jami'in hukumar hana yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa da laifukan da suka shafi kuɗi (EFCC), Chineye Okezie ya shigar da ƙara, inda ya ce a shari'ar karo na ƙarshe, za cigaba da riƙe kadarorin na din-din-din. A ranar 5 ga watan Yuni, 2024…
Read More

Rundunar Soji ta hallaka ƙasurgumin ɗan ta’adda a Kaduna

Daga Bala Muhammad Rundunar Sojin Najeriya, ta ce ta kashe wani sanannen ɗan ta'adda mai suna Kachalla Ragas tare da wasu gungun ƴan ta'adda a wani hari da ta kai a ƙaramar hukumar Giwa dake Jihar Kaduna. Kwamishinan sa-ido kan aikin jami'an na ma'aikatar tsaro da harkokin cikin gida, Samuel Aruwan ya fitar da sanarwar, inda ya ce jami'an sun kai harin ne ƙarƙashin atsayen 'Whiri Punch' wanda ya yi sanadiyar mutuwar ƴan bindigan da dama ciki har da manyan kwamandojinsu a yankin ƙauyen Bula dake dajin Yadi a ƙaramar hukumar. Yayin miƙa rahoton ga gwamnatin Jihar, Samuel ya ce…
Read More

Ƴar Galadiman Dutse mai shekaru 62 ta rasu

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Iyalan gidan Galadiman Dutse, Alhaji Basiru Muhammad Sanunsi na cikin alhini, biyo bayan rasuwar ɗaya daga cikin ƴaƴansu mai suna Hafsatu Basiru Sanusi. Marigayiyar wacce aka haifa a ranar 31 ga watan Mayu, 1962, ta bar ƴaƴa huɗu cikin har da Lukman Mahmoud Isa Dutse, ma'aikacin bankin CBN reshen Abuja, da kuma Alawiyyah Mahmoud Isa Dutse, ma'aikaciyar kamfanin inshora na ƙasa (NDIC) dake Abuja. Wasu daga cikin ƴan uwanta sun haɗa da; Jamilu Basiru Sanusi, Turakin Dutse da Zahraddeen Basiru Sanusi, Dan Isan Dutse, da kuma Sanusi Basiru Sanusi, Ɗan Darman Dutse. Hafsatu ta kasance jigo…
Read More

Gwamnatin Shugaba Tinubu ta ware naira biliyan 21 domin bai wa ƴan Najeriya mitocin lantarki kyauta

Daga BELLO ABUBAKAR BABAJI Gwamnatin Tarayya ta sanar da ware kimanin naira biliyan ashirin da ɗaya ga kamfanonin wutar lantarki guda 11, domin bai wa ƴan Najeriya masu amfani da lantarki mitoci a kyauta. Hukumar kula da wutar lantarki ta ƙasa (NERC), ta faɗi hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar 21 ga watan Yuni, 2024. Sanarwar ta ce, za'a raba mitocin ne ga waɗanda basu da shi a gidajensu ko wuraren sana'o'insu a ƴan watanni kaɗan masu zuwa. Hukumar ta ƙara da cewa, wannan huɓɓasa da gwamnatin ta yi, zai taimaka wajen haɓaka asusun kamfanonin ta…
Read More