24
Jun
'Daga Umar Garba a Katsina 'Yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun yi dirar mikiya a garin Mai Dabino dake ƙaramar hukumar Ɗanmusa ta jihar Katsina inda suka kashe mutane tara(9) suka ƙone gidaje huɗu (4) da motocin 'yan kasuwa tara (9) tare da yin garkuwa da mata da ƙananan yara fiye da hamsin a yayin harin da suka kai a garin na Mai Dabino. Wani mazaunin garin ya shaidawa Blueprint Manhaja cewa 'yan ta'addar sun kutsa kai da misalin ƙarfe goma na dare, inda suka shafe kimanin sa'o'i bakwai suna ta'addanci a garin sun kashe mutane tare da ƙone…
