ukarofi

11204 Posts
Atiku da Obi sun caccaki Tinubu kan kalamansa na “ba talakawan Nijeriya kaɗai ke talauci ba”

Atiku da Obi sun caccaki Tinubu kan kalamansa na “ba talakawan Nijeriya kaɗai ke talauci ba”

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, Atiku Abubakar, da jam’iyyar Labour sun caccaki shugaba Bola Ahmed Tinubu da cewa ba Nijeriya ce kaɗai ke fuskantar irin wannan matsanancin yanayi da ake ciki ba. Idan za a iya tunawa, Tinubu a lokacin da yake karɓar tawagar 'yan majalisar dokokin ƙasar da suka zo taya shi murnan bikin Babbar Sallah, a daren ranar Litinin, ya ce, duk da cewa akwai talauci da wahalhalu a ƙasar, ba Nijeriya ce kaɗai ke fuskantar irin wannan matsalar ba, inda ya gargaɗi masu laifi kan lalata hanyoyin jirgin…
Read More
Nijeriya na asarar Dala Miliyan 362.5 a shekara sakamakon rashin fitar da wake

Nijeriya na asarar Dala Miliyan 362.5 a shekara sakamakon rashin fitar da wake

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yayin da kasuwanni da buƙatuwar kayayyakin amfanin gona ke cigaba da ƙaruwa, kwararrun Nijeriya a fannin noma sun yi kira da a samar da ƙa'idoji na ayyukan noma a Nijeriya. Da yake magana a ranar Litinin yayin wani taron masu ruwa da tsaki, Manajan Shirin Abinci da Noma na ActionAid Nigeria, Azubike Nwokoye, ya bayyana cewa ƙasar na yin asarar kusan dala miliyan 362.5 a duk shekara a kuɗaɗen musaya na ƙasashen waje sakamakon hana fitar da wake. A cewar Azubike, ilimin aikin gona na iya rage tarzoma a nan gaba na wadatar abinci a ƙasar…
Read More
Hukumomin samar da haraji na bin Gwamnatin Tarayya Tiriliyan N3, inji FAAC

Hukumomin samar da haraji na bin Gwamnatin Tarayya Tiriliyan N3, inji FAAC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Asusun Kasafin Kuɗin Nijeriya, FAAC, ya bayyyana cewa, Gwamnatin Tarayya za ta iya fuskantar asarar Naira Tiriliyan 2.97 da Dala Miliyan 36.33 idan hukumomin samar da kuɗaɗen shiga a ƙasar nan ba su daidaita kuɗaɗen shiga da aka tara ba. Adadin da wasu hukumomin da ba a bayyana sunayensu ke bin Gwamnatin Tarayya tun daga watan Afrilun 2024 an bayyana shi ne a lokacin taron kwamitin Asusun Kasafin Kuɗin Nijeriya. Mataimakin shugaban kwamitin da ya wakilci shugaban kwamitin Kabir Mashi a wajen taron ya ce, ana cigaba da ƙoƙarin sasantawa da hukumomin da abin ya shafa…
Read More
A karon farko Nijeriya na shirin tura ɗan sama-jannati sararin samaniya

A karon farko Nijeriya na shirin tura ɗan sama-jannati sararin samaniya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta bayyana shirin tura ɗan ƙasarta na farko zuwa sararin samaniya. Darakta Janar na Hukumar Binciken Sararin Samaniya ta Nijeriya (NASRDA), Dakta Mathew Adepoju, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya kira a Abuja, Babban Birnin Tarayyar Nijeiya, a ranar Laraba da ta gabata. Dokta Adepoju ya bayyana cewa, Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta rattaba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna tsakaninta da hukumomin cibiyar binciken sararin samaniya ta SERA, domin sauƙaƙa wannan gagarumin aiki. Shugaban ya bayyana da cewa; "Wannan eanibal'amari ne da ya nuna gagarumin cigaba ga Najeriya…
Read More
Masu kuɗi sun fi talaka cin dankalin Hausa saboda tsada – Tijjani Abdullahi

Masu kuɗi sun fi talaka cin dankalin Hausa saboda tsada – Tijjani Abdullahi

Daga IBRAHEEM HAMZA MUHAMMAD Masu kuɗi sun fi talaka cin dankalin Hausa, don na Turawa sai masu mulki a Babbarn Birnin Tarayya Abuja, saboda tsadarsa da kuma ƙarancinsa a wannan zamani. Alhaji Tijjani Abdullahi, wanda shine Shugaban Kasuwar masu sayar da kayan marmari na lambu a unguwar rukunin gidajen Zangon Daura da ke Birnin Tarayya Abuja, ne ya shaida wa Wakilin Blueprint Manhaja cewa, farashin dankalin Turawa ya yi tashin Gwauron Zabo daga Naira 4,000 zuwa 8,000 zuwa 16,000, wanda ya sa har masu kuɗi da dama dake Abuja suka guje masa, inda suka koma wa na Hausa wanda shi…
Read More
‘Ƴan  banga sun kashe mutum bisa ɓatar wayar da aka ganta daga baya a hannun ɗan mai ita

‘Ƴan banga sun kashe mutum bisa ɓatar wayar da aka ganta daga baya a hannun ɗan mai ita

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Lahadi, 16 ga watan Yuni, 2024, wani matashi ɗan shekara 29 mai suna Joe Philip, wanda aka fi sani da Aboy, ya gamu da ajalinsa a hannun 'yan ƙungiyar bijilante ta sa-kai mai suna 'Anioma Security Watch Network' a Agbor, Ƙaramar Hukumar Ika ta kudu a Jihar Delta, lamarin dai ya samo asali daga zargin satar ƙaramar wayar Nokia. A cewar wani ganau, lamarin ya fara ne a lokacin da Joe Philip ya dawo daga cocin ya kunna janareta don shaƙatawa. Wata dattijuwa da ke cikin harabar gida ta nemi ya caja mata wayarta…
Read More
Sufeto Janar ya yi wa jami’ai da dama ƙarin girma

Sufeto Janar ya yi wa jami’ai da dama ƙarin girma

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A cikin makon nan ne Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya yi wa sabon mataimakin sufeto Janar na 'yan sandan Nijeriya DIG Yahaya Sahabo Abubakar ƙarin girma tare da mataimakan Sufeto Janar na 'yan sanda tara, da liƙa wa kwamishinonin 'yan sanda 15 sabbin muƙamansu a wani gagarumin biki da aka gudanar a ɗakin taro na Goodluck Ebele Jonathan da ke hedikwatar rundunar a Abuja. Sabbin Mataimaka Sufeto Janar na 'yan sandan da aka yi wa ƙarin girma sun haɗa da AIG Ahmed Ammani, Dankwara Adamu Mohammed, Mohammed Usaini Gumel, Adebola…
Read More
APC ta buƙaci Tinubu ya saka dokar ta-ɓaci a Ribas

APC ta buƙaci Tinubu ya saka dokar ta-ɓaci a Ribas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jam'iyyar APC mai mulki a Nijeriya ta sake yin kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya saka dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas saboda rikicin siyasar da ya ƙi ci, ya ƙi cinyewa. Jam'iyyar ta buƙaci da a tura sojoji da makamai a girke su a wurare na musamman a jihar domin kare abin da ta kira ɓarkewar rikici. An ruwaito cewa shugaban riƙo na jam'iyyar a jihar, Chief Tony Okocha, shi ne ya yi kiran a ranar Laraba a wani taron manema labarai a babban birnin jihar, Fatakwal, yana mai cewa akwai lamau ƙarara…
Read More
An kashe jami’an tsaro biyu a rikicin siyasar Ribas

An kashe jami’an tsaro biyu a rikicin siyasar Ribas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An kashe aƙalla mutum biyu a Jihar Ribas lokacin da wasu matasa suka mamaye gine-gine hedikwatar Ƙananan Hukumomi da dama, bayan da wa'adin shugabannin ƙananan hukumomin jihar 23 ya ƙare. Lamarin ya faru ne a jiya Talata, bayan da gwamnan jihar, Siminialayi Fubara, ya umarci shugabannin sassan mulki na ƙananan hukumomin su karɓi ragamar tafiyar da ƙananan hukumomin. Tun a ranar Litinin aka shiga zaman ɗar-ɗar bayan da wasu daga cikin shugabannin ƙananan hukumomin suka lashi takobin cigaba da zama a ofis, bisa dalilin cewa ’yan majalisar dokokin jihar 27 da ke rikici da gwamnan, waɗanda…
Read More
Ba mu da ƙarancin ma’aikata da kayan aiki a asibitin ƙwararru na Gombe – Daraktan asibitin 

Ba mu da ƙarancin ma’aikata da kayan aiki a asibitin ƙwararru na Gombe – Daraktan asibitin 

Daga ABUBAKAR A. BOLARI a Gombe Asibiitn ƙwararru na jihar Gombe shi ne mafi daɗewar asibiti a fadar jihar da aka gina shi tun kafin samun ‘yancin kan Nijeriya a shekarar 1958, kuma asibitin ya samu canje-canje sosai domin an fara shi ne tun daga matakin dispensary, ya koma cibiyar lafiyar matakin farko Primary Health Center, daga baya ya zama General sannan aka mayar da shi asibitin ƙwararru wato Specialist. Jin ana kukan cewa asibitin yana fama da ƙarancin kayan aiki da ƙwararrun ma’aikata, wakilinmu ya ziyarci asibiti inda ya zanta da Daraktan Asibitin Dokta Mu’azu Shu’aibu Ishaƙa, don jin…
Read More