Bijirarren mataimaki na musamman ga Ganduje zai tsaya takarar Gwamnan Kano

Spread the love

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano

Tsohon mataimaki na musamman kan yaɗa labarai a kafofin sadarwa na zamani, Salihu Tanko Yakasai, ga Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana aniyarsa ta tsaya wa takarar Gwamnan Jihar Kano a zaɓen 2023 da ke tafe.

Yakasai ya bayyana hakan ne cikin wani saƙo da ya wallafa ranar Talata a shafinsa na Tiwita.

Tsohon hadimin gwamnan wanda aka fi sani da Ɗawisu ya ce zai ayyana takararsa a hukumance a yau Juma’a.

Wannan na zuwa ne makonni bayan ficewarsa daga jam’iyyar APC, inda ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PRP.

Idan ba a manta ba a watan Fabrairun 2021 ne Gwamna Ganduje ya sauke shi daga muƙaminsa bisa dalilin maganganun da gwamnati ta ce ba su kamata ba da kuma sukar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

By Editor