Bijirarren mataimaki na musamman ga Ganduje zai tsaya takarar Gwamnan Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano

Tsohon mataimaki na musamman kan yaɗa labarai a kafofin sadarwa na zamani, Salihu Tanko Yakasai, ga Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana aniyarsa ta tsaya wa takarar Gwamnan Jihar Kano a zaɓen 2023 da ke tafe.

Yakasai ya bayyana hakan ne cikin wani saƙo da ya wallafa ranar Talata a shafinsa na Tiwita.

Tsohon hadimin gwamnan wanda aka fi sani da Ɗawisu ya ce zai ayyana takararsa a hukumance a yau Juma’a.

Wannan na zuwa ne makonni bayan ficewarsa daga jam’iyyar APC, inda ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar PRP.

Idan ba a manta ba a watan Fabrairun 2021 ne Gwamna Ganduje ya sauke shi daga muƙaminsa bisa dalilin maganganun da gwamnati ta ce ba su kamata ba da kuma sukar Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *