Brisbane ta samu gurbin ɗaukar nauyin Wasannin Olympic na 2032

Daga UMAR M. GOMBE

Kwamitin Shirya Wasannin Olympic na Ƙasa da Ƙasa ya bayyana birnin Brisbane na ƙasar Australia a matsayin birnin da zai ɗauki nauyin gudanar da Wasannin Olympic na 2032.

Da wannan sasarar da Brisbane ya samu, ya sanya Australia ta zama ƙasa ta biyu a duniya bayan ƙasar Amurka da suka samu damar ɗaukar nauyin gudanar da Wasannin Olympic fiye da sau biyu a birane daban-daban.

Da farko, Australia ta soma ɗaukar nauyin Olympic ne a Melbourne a 1956, sannan Sydney a 2000, sai kuma na ukun kenan ake sa ran gudanarwa a Brisbane ya zuwa 2032.

Ita kuwa ƙasar Amurka, ta soma ɗaukar nauyin Olympic ne a 1904 a St. Louis, sannan a Los Angeles 1984 da kuma 1996 a Atlanta, sai L.A. a 2028.

Kwamitin shirye-shirye na Olympic ɗin Brisbane ya ce ana sa ran tattalin arzikin yankin ya samu amfani na kimanin Dala bilyan $17 albarkacin gasar Olympic ɗin da za a gudanar.

Firam Minista Australia, Scott Morrison, ya ce gwamnatin ƙasar a shirye take ta ba da cikakken goyon bayanta domin ganin an gudanar da wasannin cikin nasara.