Kasuwanci

Kamfanin KAEDCO zai iya rasa lasisinsa sakamakon Bashin Naira biliyan 51.93

Kamfanin KAEDCO zai iya rasa lasisinsa sakamakon Bashin Naira biliyan 51.93

Daga AMINA YUSUF ALI Kamfanin rarraba wutar lantarki na jihar Kaduna (KAEDCO) yana fuskantar barazanar rasa lasisin gudanar da kamfanonin saboda bashin Naira biliyan 51.93. Kamfanin KAEDCO ya amshi sanarwa daga hukumar kula da ƙa'idojin wutar Lantarki (NERC) a ranar Litinin xin da ta gabata. Inda ake umartar Bankin game da niyyar NERC na soke lasisinsa na gudanarwa. Wasu rahotanni da suka bayyana a ranar Talatar da ta gabata sun bayyana cewa, KAEDCO ta tara wa kanta bashin Naira biliyan 41.49 a tsakanin shekaru 2015 zuwa 2021, wanda Hukumar rarraba wutar ta Nijeriya a kan sari (NBET) da MO suka…
Read More
Farashin kayayyaki ya ƙaru da kashi 22.22 a Nijeriya – NBS

Farashin kayayyaki ya ƙaru da kashi 22.22 a Nijeriya – NBS

A halin da ake ciki, farashin kayayyakin masarufi a Nijeriya ya ƙaru zuwa kashi 22.22 a watan Afrilu saɓanin 22.04 a watan Maris. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin sanarwar da Hukuma Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS), ta fitar a ranar Litinin. A cewar Hukumar, ƙididdigar hauhawar farashi ta watan Afrilun 2023, ta nuna an samu ƙarin kashi 0.18 na tsadar kayayyaki idan an kwatanta da watan Maris da ya gabata. NBS ta ce bisa la'akari da sheka-shekara, an samu hauhawar farashi mai yawa a Afrilun bana idan aka kwatanta da yadda lamarin yake a Afrilun 2022, wato kashi 16.82. Hukumar…
Read More
Tsadar rayuwa: Kamfanin MTN zai ƙara kuɗin kira da farashin data

Tsadar rayuwa: Kamfanin MTN zai ƙara kuɗin kira da farashin data

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kamfanin Telecomms na MTN, ya ce, yana shirin ƙara farashin ayyuka a layinsa saboda hauhawar farashin kayayyaki a wuraren aiki. An bayyana hakan ne a cikin rahoton kafanin na farko da aka shigar a kasuwar hada-hadar hannayen jari ta Johannesburg a ranar Alhamis. A hasashen da ta yi na sauran shekarar 2023, kamfanin ya MTN ya ce, “Muna sa ran cewa yanayin kasuwanci a faɗin kasuwanni zai ci gaba da zama ƙalubale har zuwa ƙarshen shekarar 2023 kuma za mu ci gaba da aiwatar da matakan da za mu ɗauka don shawo kan ƙalubalen da ke…
Read More
Dangote ya kusa ƙaddamar da katafariyar matatar mai a Legas

Dangote ya kusa ƙaddamar da katafariyar matatar mai a Legas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ana sa ran Kamfanin Matatar Man Fetur na Dangote na biliyoyin daloli zai kawo mafita ga al'amuran matatar mai a Nijeriya. An ruwaito wata majiya ta bayyana cewa, shugaba Buhari zai ƙaddamar da kamfanin. A baya dai, kamfanin Dangote ya yi nuni da cewa, za a ƙaddamar da matatar man a Legas kafin ƙarshen wa’adin mulkin shugaba Buhari a ranar 29 ga watan Mayun 2023. Babban jami’in hulɗa da jama’a na kamfanin Dangote, Mista Anthony Chiejina, a wata sanarwa da ya fitar ya ƙaryata rahotannin da ke cewa matatar na daga cikin ayyukan da Buhari zai…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ƙara harajin shigo da shinkafa da alkama

Gwamnatin Tarayya ta ƙara harajin shigo da shinkafa da alkama

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin tarayya ta ba da sanarwar sake waiwayar harajin shigo da kayan waje (IAT) a matsayin wani ɓangare na tsara dokar harajin Gamayyar kasuwanci ta Afirka (ECOWAS) (CET) 2022-2026, wannan ya sa ta yi ƙari a kan haraji ga jasashe masu shigo da shinkafa, alkama, barasa, da sauran hajoji guda 189. Wannan sabon ƙarin harajin na shekarar 2023, ya ɗaga harajin kan shinkafa da ta haura kilo 5, ko mai yawa amma a rarrabe zuwa kilo 5, to za a biya harajin kaso 60, wanda kaso 50 ake biya a baya. Hakazalika, shigo da alkama ko…
Read More
Duniya rawar ‘yammata: BUA ya kere arzikin Ɗangote a watan Afrilun bana

Duniya rawar ‘yammata: BUA ya kere arzikin Ɗangote a watan Afrilun bana

Daga AMINA YUSUF ALI AbdulSamad Rabiu, hamshaƙin ɗan kasuwa a Nijeriya, kuma mutum na biyu ma fi dukiya a ƙasar ya buga tarihi a watan Afrilun shekarar bana ta 2023 a cewar sakamakon binciken kwanan nan da Forbes suka gudanar. Ƙarfin arzikin na Abdulsamad Rabi'u ya yi tashin gwauron zabi zuwa Dalar Amurla biliyan $8.6 a ƙarshe watan Afrilun na bana. Wato dai an samu ƙaruwar maƙudan kuɗi har Dalar Amurka biliyan $300 wato kwatankwacin Naira biliyan 138.14 musamman idan aka kwatanta dukiyarsa da dalar Amurka biliyan $8.3 da take a 1 ga watan Afrilu, 2023. Wannan ya nuna cewa,…
Read More
Jarumi Uzee ya zama jakadan Bankin Musulunci na TajBank

Jarumi Uzee ya zama jakadan Bankin Musulunci na TajBank

Daga AMINA YUSUF ALI Fitaccen jarumin nan na Kannywood da Nollywood, Usman Uzee, ya zama jakadan bankin nan na Musulunci, wato TajBank. A ranar Alhamis, 4 ga Mayu, 2023, jarumin ya rattaba hannu kan yarjejeniyar da bankin tare da manyan jami’an bankin. Idan dai za a iya tunawa, bankin na TajBank yana daga cikin kalilan din bankuna a Nijeriya da ba su mu’amula da kudin ruwa. Shi kuwa Jarumi Uzee yana daga kalilan din jarumin Nijeriya da suke fitowa a finafinan Arewa da na Kudu. Daya daga cikin fitattun finafinan da ya fito shine, Voiceless, wanda ya samu hawa manhajar…
Read More
Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara ya ziyarci kasuwar da aka yi gobara a Gusau

Zaɓaɓɓen Gwamnan Zamfara ya ziyarci kasuwar da aka yi gobara a Gusau

*Ya jajanta wa waɗanda iftila'in ya shafa Zaɓaɓɓen gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana alhininsa game da gobarar da ta tashi a shahararriyar kasuwar wayar salula da ke Bebeji Plaza a Gusau, babban birnin jihar. Lamarin dai ya faru ne a daren ranar Litinin, inda gobarar ta lalata ƙadarori na miliyoyin Naira. Da yake jawabi ga shugabannin kasuwar da kuma waɗansu daga cikin waɗanda abin ya shafa a yayin ziyarar gani da ido da ya kai kasuwar ranar Talata, Lawal ya jajanta wa masu sayar da wayoyin salular da kuma masu ƙadarorin waɗanda tabbas suka yi asarar da ba…
Read More
NANS ta ba wa MultiChoice wa’adin kwanaki 7 don cire ƙarin farashin satalayi

NANS ta ba wa MultiChoice wa’adin kwanaki 7 don cire ƙarin farashin satalayi

Daga AMINA YUSUF ALI Ƙungiyar ɗalibai ta ƙasa (NANS) yankin Kudu maso yammacin ƙasar nan, ta ba wa kamfanin satalayi na MultiChoice Nigeria, wa'adin kwanaki 7 kacal a kan ya soke ƙarin farashin da ya yi nufin yi a kan biyan tashoshin DSTV da GOTV. Hakazalika ƙungiyar ta yi barazanar rufe dukkan wuraren da ake sayar da tauraron ɗan'adam ɗin na Multichoice. Ƙungiyar ɗaliban ta bayyana haka ne a ranar Talatar da ta gabata a wani jawabi da shugaban tsare-tsarenta, Adejuwon Olatunji, da mataimakinsa, Alao John, da jami'inta na hulxa da jama'a, Opeoluwa Awoyinfa suka sanya wa hannu. A kwanankin…
Read More
Kamfanin Ɗangote ya ba wa manoma 60 tallafin noma

Kamfanin Ɗangote ya ba wa manoma 60 tallafin noma

Daga AMINA YUSUF ALI A ƙoƙarinsa na bunƙasa harkar noma wadataccen abinci a yayin damina a ƙasar nan, kamfanin Ɗangote ya sanar da ba da tallafin noma ga manoma 60 da suke a yankin Ibese. A wani jawabi da kamfanin ya saki ranar Alhamis ɗin makon da ya gabata, kamfanin ya bayyana cewa, tallafin zai taimaka wajen ƙara musu ƙarfin iya yin noma na zamani don samun ƙarin wadatattun amfanin gona masu inganci.Hakazalika, hukumar gudanarwar kamfanin sun bayyana cewa, wannan shirin musamman an yi shi saboda manoman masara. Azad Nawabuddin, Daraktan reshen kamfanin na reshen Ibese, an zaɓo manoman ne…
Read More