Kasuwanci

CBN zai sauya tsarin wasu takardun kuɗin Nijeriya

CBN zai sauya tsarin wasu takardun kuɗin Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya ce, nan ba da daɗewa ba zai sake tsarin wasu takardun kuɗin Nijeriya. Bankin ya ce takardun da sake tsarin zai shafa sun haɗa da N200 da N500 da kuma N1,000. Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya bayyana hakan ga taron manema labarai ran Laraba a Abuja. Emefiele ya ce, ya zuwa 15 ga Disamban wannan shekarar za a fara amfani da takardun kuɗin da aka sake wa tsarin. A cewar Emefiele, Gwamnatin Tarayya ce ta buƙaci CBN da ya duba ya sake tsarin takardun kuɗin da lamarin ya shafa.
Read More
Yadda Abdulsamad Rabi’u ya ture Mike Adenuga daga matsayin mutum na biyu mafi kuɗi a Nijeriya

Yadda Abdulsamad Rabi’u ya ture Mike Adenuga daga matsayin mutum na biyu mafi kuɗi a Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI A halin yanzu dai Biloniya Abdussamad Rabi'u ya ture Adenuga ya ɗare kujerar matsayin mutum na biyu a arziki a faɗin Nijeriya. Wannan ya faru ne a yayin da Attajirin ya samu cinikin sama da kimanin Naira biliyan N87 wato dalar Amurka biliyan biyar da rabi, a cikin sa'o'i kaɗan a ranar Larabar da ta gabata. Abdulsamad Rabiu Rabiu ya samu damar ture tsohon mai kuɗin nan Adenuga wanda kafin ranar Larabar nan shi ne mutum na biyu ma fi kuɗin a Nijeriya. To amma yanzu wannan ya zama tarihi tunda Abdussamad ya yi masa juyin…
Read More
Dubai ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza

Dubai ta dakatar da bai wa ‘yan Nijeriya biza

Daga BASHIR ISAH Hukumomin Dubai sun ba da sanarwar dakatar da bai wa 'ya Nijeriya biza ta shiga ƙasar har sai abin da Allah Ya yi. Bayanin dakatawar na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da suka aika wa abokan kasuwancinsu na Nijeriya. Dubai ta ce ta dakatar da dukkan yakardun da aka tura mata don neman biza daga Nijeriya. Bayanai sun ce wannan mataki da Dubai ta ɗauka na da nasaba da matsayar da Hukumar Kula da Shige da Fice ta Haɗaɗɗiyar Dular Larabawa ta cimma, tare da cewa dakatarwa ta shafi dukkan 'yan Nijeriya ne. Sanarwar ta ƙara da…
Read More
Hukumar FCTA ta gargaɗi masu gudanar da sana’ar kanikanci a gefen hanyoyin jirgin ƙasa

Hukumar FCTA ta gargaɗi masu gudanar da sana’ar kanikanci a gefen hanyoyin jirgin ƙasa

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar gudanar da al'amuran Birnin Tarayyar Abuja (FCTA), a ranar Lahadin da ta gabata ta yi jan kunne ga masu buɗe shagunan kanikanci a gefen hanyoyin jirgin ƙasa a Abuja. Daraktan kula da cigaba na FCTA, Director Muktar Galadima, shi ya bayyana wannan gargaɗin. Kuma a cewar sa nan gaba hukumar za ta dinga kama waɗanda suka yi kunnen ƙashin a game da dokar tare da ƙwace ababen hawan da suke aikin a kai. Galadima ya ƙara da cewa, waɗancan kanikawa za a gurfanar da su a gaban kotun tafi da gidanka. Sannan ya ƙara da…
Read More
Zugacoin na daga cikin kamfanoni ukun kan gaba a harkar kuɗin yanar gizo a duniya – Farfesa Jibia

Zugacoin na daga cikin kamfanoni ukun kan gaba a harkar kuɗin yanar gizo a duniya – Farfesa Jibia

Daga WAKILINMU Wani tsohon malami a tsangayar koyar da kimiyyar siyasa a Jami'ar Bayero da ke Kano, Farfesa Aliyu Abdullahi Jibia, ya ce kuɗin kasuwanci na yanar gizo mai suna Zugacoin ɗaya ne daga cikin kamfanoni 3 da suka fi shahara a harkar kuɗin yanar gizo a duniya. Aliyu Jibia, ya bayyana haka ne a yayin da Jaridar Hausa Daily Post ta yi bikin karrama shugaban gidauniyar Samzuga, wanda ya assasa Zugacoin da Green Zugacoin. Ya kara da cewa, “Archbishop Farfesa SamZuga, jami’in diflomasiyya ne a tsarin International Society OF Diplomats and Global Emissary Council, wanda shine shugaban tattalin arziki…
Read More
Gobara ta lamushe wani ɓangare na Kasuwar Balogun ta Legas

Gobara ta lamushe wani ɓangare na Kasuwar Balogun ta Legas

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar Lahadin da ta gabata ne dai aka yi wata gobara da ta lamushe shaguna da dama a kasuwar Balogun dake kan titin Martins Street a jihar Legas. Hotunan wannan ƙazamar gobarar da ta farmaki wani sashe na babbar kasuwar suna ta yawo a kafafen yanar gizo da yadda gabarar ta dinga ci ganga-ganga tana jawo asara. Jami'in kula da abokan hulda na Hukumar kashe gobara ta Legas yayin wata zantawar manema labarai da shi a wayar tarho a lokacin da gobarar take cigaba da ruruwa ya ba da tabbacin cewa, hukumar tana iya bakin…
Read More
Buhari ya ba da umarnin buɗe kamfanin simintin Ɗangote da ke Obajana

Buhari ya ba da umarnin buɗe kamfanin simintin Ɗangote da ke Obajana

Daga BASHIR ISAH Shugaba Buhari ya ba da umarnin a gaggauta buɗe masana’antar simintin nan ta Ɗangote da ke Obajana, Jihar Kogi. Gwamnati ta ba da umarnin haka ne a taron Majalisar Tsaro da ya gudana a Fadar Shugaban Ƙasa ƙarƙarƙashin jagorancin Shugaba Buhari ranar Juma'a. Bayanin sake buɗe masana'antar ya fito ne daga bakin Ministan Harkokin ’Yan sanda, Mohammed Dingyadi da takwaransa na Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola da kuma Babban Hafsan Tsaro, Janar Lucky Irabor yayin da suke yi wa manema labarai jawabi jim kaɗan bayan taron. Aregbesola ya ce, an cimma yarjejeniya tsakanin Gwamnatin Jihar Kogi da…
Read More
Amai da lashewa: Musk ya sake zawarcin sayen Kamfanin manhajar Tiwita

Amai da lashewa: Musk ya sake zawarcin sayen Kamfanin manhajar Tiwita

Daga AMINA YUSUF ALI A yanzu haka dai Biloniya, kuma attajiri mafi kuɗi a Duniya, Elon Musk ya sake waiwayar maganar sayen Kamfanin manhajar Soshiyal midiyar nan ta Tiwita.Musk ya yi wanna batu mai kama da amai da lashewa ne a ranar Talatar da ta gabata kamar yadda jaridar Reuters ta rawaito. A kwanakin baya dai idan ba mu manta ba, Attajirin ya so ya sayi kamfanin na Tiwita, a kan farashin Dalar Amurka biliyan $44. Inda daga baya kuma ana tsaka da cinikin kuma muka ji Attajirin ya sake bayyana cewa, ya fasa sayen Kamfanin saboda wasu abubuwa masu…
Read More
Anya CBN zai iya farfaɗo da darajar Naira da ƙarin kaso 15.5% na kuɗin ruwa?

Anya CBN zai iya farfaɗo da darajar Naira da ƙarin kaso 15.5% na kuɗin ruwa?

Daga AMINA YUSUF ALI Kwamitin harkokin kuɗi na Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya yanke shawarar ɗaga darajar kuɗin ruwansa da kaso 15.5%. Kwamitin ya yanke wannan shawarar ne a ranar Talatar da ta gabata. Kuma ya yanke wannan hukunci ne, saboda a ceto Naira daga rugurgujewar da take ta fama a 'yan kwanakin nan, abinda suke sa ran zai ƙaro sassauci ga 'yan Nijeriya ta fuskar haɓakar tattalin arziki da kuma sauki a farashin kaya. Amma abin tambayar a nan shi ne, shin wannan mataki da CBN ya ɗauka zai kai ga kwalliya ta biya kuɗin sabulu kuwa? Jaridar ta…
Read More
FIRS ta gargaɗi hukumomi da ma’aikatun gwamnati kan katsalandan a harkar haraji

FIRS ta gargaɗi hukumomi da ma’aikatun gwamnati kan katsalandan a harkar haraji

Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tattara haraji ta Nijeriya (FIRS) ta gargaɗi hukumomin gwamnati a kan tsoma baki a harkar haraji. Wato ɗora haraji, karɓar harajin da bibiyar waɗanda ba sa biyan harajin. Wannan jawabi dai ya fito daga shugaban zartarwa na hukumar FIRS, Mista Muhammad Nami. Kamar yadda yadda kamfanin dillancin labarai ya rawaito. Mista Nami ya ya yi ƙarin jan kunne ga hukumomi da ma'aikatun a kan yadda suke ɗaukar ma'aikatan da za su dinga karɓar harajin da gwamnatin tarayya take bin kamfanoni da mutane, masana'antu bankuna, da sauran cibiyoyin gudanar da kasuwanci ba bisa tsarin doka ba.…
Read More