Kasuwanci

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa dake Kano

Gobara ta tashi a Kasuwar Singa dake Kano

Daga WAKILINMU Bayanai daga Kano sun tabbatar da aukuwar gobara a fitacciyar kasuwar nan ta Kano, wato Kasuwar Singa. Majiyarmu ta ce gobarar ta fara ne da tsakar daren da ya gabata zuwa safiyar Litinin. An ga jami'an kwana-kwana tare da 'yan kasuwar a lokacin da suke ƙoƙarin kashe gobarar wadda ta ƙone shaguna da daman gaske. Abubakar Aminu, na ɗaya daga cikin 'yan kasuwar da gobarar ta shafa, ya shaida wa jaridar News Point cewa ya samu kiran waya da misalin ƙarfe 1:15 na dare, kuma da ya isa kasuwar da misalin ƙarfe 2:00 na daren, ya tarar da…
Read More
Masu safarar itatuwa da gawayi sun ce sun dawo da ƙarfinsu bayan gwamnatin Nijeriya ta ɗage musu takunkumi

Masu safarar itatuwa da gawayi sun ce sun dawo da ƙarfinsu bayan gwamnatin Nijeriya ta ɗage musu takunkumi

Daga AMINA YUSUF ALI Bayan gwamnatin tarayya ta ɗage musu takunkumin fita da hajarsu ƙasashen ƙetare, masu safarar gyararrun gungumen itatuwa da gawayi sun yi kira da a zo a sanya musu hannayen jarin Dalar Amurka biliyan 152.94. 'Yan kasuwar sun lashi takobin haɓaka jarin kasuwancinsu har zuwa Dalar Amurka biliyan $152.94 a wannan shekara ta 2023. Bayan gindaya musu sharuɗɗa, gwamnatin tarayya ta ɗage takunkumi a kan safarar gawayi da guma-guman itace domin ta taimaka wa kasuwancin, musamman ma waɗanda suke gyara shara ta koma dukiya domin havaka hada-hada tsakanin Nijeriya da ƙasashen duniya. Ministan Muhalli na Nijeriya, Mohammed…
Read More
CBN ya kammala shirin canjin kuɗi a yankunan karkara

CBN ya kammala shirin canjin kuɗi a yankunan karkara

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya, CBN, ya ce ya kammala shirin canjin tsoffin kuɗi da sabo a yankunan karkara da sauran yankunan da babu bankuna. Muƙaddashin Kakakin CBN, Isa Abdulmumin, ne ya bayyana haka tare da cewa shirin ya cimma manufarsa. A cewarsa, “Shirin ya kammala. Shirin abu ne mai ƙayyadadden lokaci amma ba wanda zai ci gaba da gudana ba." Sai dai Ƙungiyar Masu Hada-hadar Kuɗi ta Waya da Wakilan Bankuna a Nijeriya, ta bayyana shirin a matsayin mara armashi, saboda taƙaita damawa da masu ruwa da tsaki a cikinsa. CBN ya ce an samar da shirin ne…
Read More
Ɓata-gari sun cinna wa ɓangaren ƙabilar Ibo a kasuwar Legas wuta

Ɓata-gari sun cinna wa ɓangaren ƙabilar Ibo a kasuwar Legas wuta

Daga AMINA YUSUF ALI Ana zargin wasu ɓata-gari da cinna wuta wacce har ta yi sanadiyyar tayar da gobara a kasuwar Legas ta sayar da kayayyakin gyaran mota wacce mafi akasarin ahalinta inyamurai ne, wato 'yan ƙabilar Ibo. Wannan kasuwar sayar da kayan gyaran mota tana kan titin Kirikiri, Ajegunle, ƙaramar hukumar Ajeromi ifelodun ta jihar Legas. Al'amarin ya faru ne a safiyar ranar Laraba, 8 ga Maris, 2023. Rahotanni sun bayyana cewa, wannan hari da aka kai kasuwar sayar da kayan mota wacce akasarinta ƙabilar Ibo ne suke da rinjaye a cikinta an yi shi ne da gayya kuma…
Read More
Gwamnan Kogi ya yi barazanar kama masu ƙin karɓar tsoffin kuɗi a jiharsa

Gwamnan Kogi ya yi barazanar kama masu ƙin karɓar tsoffin kuɗi a jiharsa

Daga BASHIR ISAH Gwamna Yahaya Bello na Jihar Kogi ya yi barazanar kamawa da hukunta masu ƙin karɓar tsoffin kuɗi a jiharsa. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Kwamishinan Labarai da Sadarwa na Jihar, Mr Kingsley Fanwo, ya fitar a Lakwaja babban birnin jihar. A ranar Larabar da ta gabata Koton Ƙoli ta yanke hukuncin ci gaba da a,mfani da tsoffin takardun kuɗi na N1000, N500 da N200 har zuwa Disamban 2023. Da wannan Gwamnan Yahaya ya ce ba daidai ba ne ƙin karvar tsoffin kuɗin duk da Kotun Ƙoli ta ba da damar haka. “Wannan gwamnatin ba za…
Read More
Mazauna Abuja na fuskantar matsanancin matsalar fetur

Mazauna Abuja na fuskantar matsanancin matsalar fetur

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Yawancin masu ababen hawa a Babban Birnin Tarayya Abuja, na fuskantar matsalar man fetur da dogayen layuka ake cigaba da yi a gidajen man. Wakilin Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya da ya sa ido a gidajen mai a Abuja a ranar Talata, ya ba da rahoton cewa, yawancin gidajen fetur ɗin a rufe suke, yayin da kaɗan ne kawai ke badawa, wanda ya haifar da mummunar cunkoson ababen hawa saboda dogayen layukan da ake yi. Masu motocin sun kuma nuna rashin jin daɗinsu kan ƙarancin tsabar kuɗaɗen da ake samu a ƙasar nan, wanda suka ce…
Read More
Dillalan hatsi sun ƙi amincewa da tiransfa a Abuja

Dillalan hatsi sun ƙi amincewa da tiransfa a Abuja

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Dillalan hatsi a kasuwannin bayan gari a Babban Birnin Tarayya, Abuja, na ƙin amincewa da hada-hadar kuɗi na tiranfa daga kwastomomi, duk da ƙarancin tsabar kuɗi na babban bankin Nijeriya, CBN. Wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya da ya sa ido a kasuwannin Nyanya, Karu, Mararaba da Masaka a ranar Talata a Abuja, ya lura ’yan kasuwar ba sa karɓan tiranfa sai tsabar kuɗi. A cewar ’yan kasuwar, suna sayen kayayyakin ne kai tsaye daga hannun manoman karkara waɗanda ba su yarda da wani nau’i na hada-hadar banki na lantarki ba. Kadijat Ibrahim, ’yar kasuwa a kasuwar…
Read More
Amfani da tsohon kuɗi: Har yanzu bankuna a Abuja ba su bi umarnin Kotun Ƙoli ba

Amfani da tsohon kuɗi: Har yanzu bankuna a Abuja ba su bi umarnin Kotun Ƙoli ba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Har yanzu ’yan Nijeriya ba su samu wadataccen sababbi da tsofaffin takardun Naira ba kwanaki bayan da Kotun Ƙoli ta bayar da umarni ga Babban Bankin Nijeriya (CBN) kan cigana da amfani tsoffin takardar kuɗi daga ranar 10 ga watan Fabrairu. Har yanzu dai bankunan da ke Abuja ba su nuna gamsuwarsu kam wannan batu ba, saboda har yanzu mazauna garin na fuskantar matsalolin ƙarancin kuɗi a wuraren cire kuɗi na ATM na POS. A ranar Juma’a ne ƙotun ƙolin ƙasar ta halasta amfani da wasu tsofaffin takardun kuɗin Naira a matsayin takardar kuɗi har zuwa…
Read More
Elon Musk ya sake ƙwato kambunsa na mutumin da ya fi kowa arziki a duniya

Elon Musk ya sake ƙwato kambunsa na mutumin da ya fi kowa arziki a duniya

Daga AMINA YUSUF ALI Elon Musk ya sake dawowa matsayinsa na mutumin da ya fi kowa arziki a Duniya bayan ya tara maƙudan kuɗaɗe har Dalar Amurka biliyan $6.98 a cinikin awoyi takwas kacal. Idan ba a manta ba a kwanakin baya ne dai attajiri Musk ya rasa muƙamin nasa na mai arzikin duniya bayan da wani Bafaranshen attajiri mai suna Bernard Arnault ya yi masa ƙafar baya tare da ture shi, kuma ya haye ƙaragarsa ta mutumin da ya fi kowa kuɗi a duniya, a ranar 8 ga watan Disambar, 2022. Al'amarin da ya jawo Musk ya rasa wancan…
Read More
Dalilin bayyanar layukan abubuwan hawa a gidajen mai – NNPCL

Dalilin bayyanar layukan abubuwan hawa a gidajen mai – NNPCL

Daga BASHIR ISAH Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPCL), ya alaƙanta layukan abubuwan hawa a gidajen mai da ake gani a Abuja da wasu sassan ƙasar da hana harkokin kasuwanci da zirga-zirga a lokacin zaɓen Shugaban Ƙasa da na 'yan majalisun tarayya da ya gudana ran 25 ga Fabrairu. Hukumar NNPCL ta ce, defo da manyan motocin ɗaukar mai sun ci gaba da aikin rarraba mai zuwa sassa daban-daban na ƙasar nan don daidaita lamurra. Cikin wata sanarwa da ya fitar, Kakin NNPCL, Garba Deen Muhammad, ya ce bayanan baya-baya sun nuna kamfanin na da mai a tanade da ya…
Read More