13
Mar
Daga WAKILINMU Bayanai daga Kano sun tabbatar da aukuwar gobara a fitacciyar kasuwar nan ta Kano, wato Kasuwar Singa. Majiyarmu ta ce gobarar ta fara ne da tsakar daren da ya gabata zuwa safiyar Litinin. An ga jami'an kwana-kwana tare da 'yan kasuwar a lokacin da suke ƙoƙarin kashe gobarar wadda ta ƙone shaguna da daman gaske. Abubakar Aminu, na ɗaya daga cikin 'yan kasuwar da gobarar ta shafa, ya shaida wa jaridar News Point cewa ya samu kiran waya da misalin ƙarfe 1:15 na dare, kuma da ya isa kasuwar da misalin ƙarfe 2:00 na daren, ya tarar da…
