08
Oct
Daga AMINA YUSUF ALI Hukumar tattara haraji ta Nijeriya (FIRS) ta gargaɗi hukumomin gwamnati a kan tsoma baki a harkar haraji. Wato ɗora haraji, karɓar harajin da bibiyar waɗanda ba sa biyan harajin. Wannan jawabi dai ya fito daga shugaban zartarwa na hukumar FIRS, Mista Muhammad Nami. Kamar yadda yadda kamfanin dillancin labarai ya rawaito. Mista Nami ya ya yi ƙarin jan kunne ga hukumomi da ma'aikatun a kan yadda suke ɗaukar ma'aikatan da za su dinga karɓar harajin da gwamnatin tarayya take bin kamfanoni da mutane, masana'antu bankuna, da sauran cibiyoyin gudanar da kasuwanci ba bisa tsarin doka ba.…