05
Mar
Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar ‘yan sandan Jihar Borno ta kama wasu mutane 50 da ake zargi da yin sace-sace a kasuwar Monday Market ta Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno. Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan (PPRO), Kamilu Shatambaya ya tabbatar da kama waɗanda ake zargin a ranar Laraba a Maiduguri. Ya ce jami’an rundunar da aka tura domin kare rayuka da dukiyoyin da gobarar ta afku a kasuwar, sun kama waɗanda ake zargin ne a ranar 26 ga watan Fabrairu. Ya ce waɗanda ake zargin sun yi awon gaba da kadarorin waɗanda abin ya shafa…
