Kasuwanci

Gwamnatin jihar Anambra za ta rushe haramtattun rumfunan a kasuwar NASPA

Gwamnatin jihar Anambra za ta rushe haramtattun rumfunan a kasuwar NASPA

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnati jihar Anambra a yanzu haka ta shirya tsaf don yin rusau ga wasu rumfunan kasuwa da ta ce ba a gina su kan ƙa'ida ba. Ita dai wannan kasuwa ita ce kasuwar sayar da sassan gyaran mota wadda ake fi sani da NASPA da yake a Zone-14 a yankin Nnewi. Kwamishinan kasuwanci da masana'antu na jihar, Dakta Obinna Ngonadi, shi ya bayyana haka bayan ziyarar gani da ido da ya kai na rangadin kasuwar tare da shugaban hukumar tsara gine-gine na jihar, Mista Chike Maduekwe. Kwamishinan ya bayyana rashin jin daɗinsa a kan yadda aka…
Read More
Kamfanonin siminti na BUA da Ɗangoten suna kashe kaso 41.33 na cinikinsu a kan wutar lantarki da makamashi

Kamfanonin siminti na BUA da Ɗangoten suna kashe kaso 41.33 na cinikinsu a kan wutar lantarki da makamashi

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni sun bayyana cewa, kamfanonin siminti na Ɗangote da BUA suna kashe kaso 41.33 na cinikinsu wajen samar da wutar lantarki da sayen makamashi. A yayin da shekarar nan ta 2022 ta raba, waɗannan manyan kamfanonin Sumuntin da suka fi kowanne a Nijeriya Ɗangote da BUA sun kashe kimanin Naira biliyan 173.537 a kan samar da wutar lantarki da makamashi. Wato kaso 41.33 daga cikin jimillar kuɗaɗen cinikin da suka yi tun daga farkon shekarar zuwa wannan lokaci, Naira biliyan N419.965. Wato abinda kamfanonin biyu suka kashe ya qaru da kaso 38.34 a kan Naira biliyan…
Read More
‘Yan Nijeriya za su fara hada-hadar E- Naira a wayar salula nan da mako mai zuwa – CBN

‘Yan Nijeriya za su fara hada-hadar E- Naira a wayar salula nan da mako mai zuwa – CBN

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN) Godwin Emefiele, ya bayyana cewa, nan da mako mai zuwa 'yan Nijeriya za su iya hada-hadar kuɗin ta lalitar E-Naira a wayoyin hannunsu nan da mako mai kamawa. Shi dai tsarin E-Naira tsari halstacce a doka na amfani da fasahar zamani wajen hada-hadar kuɗin a yanar gizo. Bayan hada-hadar kuma, gwamnan CBN ya bayyana cewa, 'yan Nijeriya za su iya buɗe lalaitr E-Naira a wayoyinsu na hannu. A cewarsa, kawai za a danna *997# a cikin wayar hannu domin yin hada-hadar E- Naira a wayoyin hannu. Kuma kowa zai iya amfani…
Read More
Bashi ya sa kotu ta garƙame shalkwatar First Bank a Abuja

Bashi ya sa kotu ta garƙame shalkwatar First Bank a Abuja

Daga AMINA YUSUF ALI Babban Kotun Tarayyar ta Abuja ta ba da umarnin garƙame shalkwatar Bankin First Bank a kan bashi. Bankin ya kasance babban bankin Kasuwanci a faɗin Nijeriya. Rahotanni sun bayyana cewa, a ranar Juma'ar da ta gabata ne dai jami'an kotun suka yi dirar mikiya a Shalkwatar bankin domin ƙwace wasu kayayyaki mallakin bankin. Hakazalika, rahotannin sun ƙara bayyana cewa, bijire wa umarnin kotun ne ya sa jami'an kotun suka fita a Shalkwatar dake Abuja da motocin janwai domin ƙwace wasu kayayyaki mallakin kotun kamar injin janareto da manyan motoci. A cikin kayan da aka ɗauka har…
Read More
Ɗangote ya samu lambar girmamawa saboda tallafin Gidauniyarsa ga harkar lafiya

Ɗangote ya samu lambar girmamawa saboda tallafin Gidauniyarsa ga harkar lafiya

Daga AMINA YUSUF ALI Hamshaqin ɗan kasuwa, babban shugaban gudanarwa na rukunin kamfanoni da masana'antu Ɗangote, Aliko Ɗangote ya amshi lambar yabo daga shugaban ƙasar Nijar, Mohamed Bazoum a babban birnin garin, Yamai (Niamey). Ita dai wannan kyauta wacce take tafe da shaidar girmamawa wacce aka ba wa Ɗangote a birnin Niamey babban birnin Nijar ɗin an ba wa Ɗangote ne saboda hidima wa harkar lafiya a jamhuriyar Nijar da Gidauniyarsa ta Ɗangote (ADF) take yi. Sannan kuma don yaba wa irin taimakon da attajirin yake yi wa al'ummar. Idan za a iya tunawa, da ma gidauniyar Ɗangote ta ADF…
Read More
Gwamnatin Bayelsa ta nemi tallafin Bankin Heritage don ba wa matasa sana’a

Gwamnatin Bayelsa ta nemi tallafin Bankin Heritage don ba wa matasa sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin jihar Bayelsa ta bayyana ra'ayinta na son ta haɗa hannu da Bankin Heritage don tallafa wa matasanta a vangaren sana'o'i da wasannin motsa jiki. Mataimakin gwamnan jihar mai suna Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, ya bayyana haka ne yayin ziyarar ban girma tare da Kwamishinan matasa da wasanni, Daniel Igali da wasu zuwa ga mahukuntan bankin Heritage da suka kai Shalkwatar Bankin dake jihar Legas a kwanan nan. Ewhrudjakpo ya bayyana cewa, a shirye yake da ya haɗa gwiwa da Bankin Heritage domin samar da abin yi ga matasa da kuma bunƙasa harkar wasanni domin ƙara samar…
Read More
Yadda ƙungiyar Kiristoci ta yi wa Bankin Ja’iz bore don hana shi gyara kasuwar Terminus ta Jos

Yadda ƙungiyar Kiristoci ta yi wa Bankin Ja’iz bore don hana shi gyara kasuwar Terminus ta Jos

Daga AMINA YUSUF ALI Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen jihar Filato tare da Gamayyar qungiyoyin ƙabilu 'yan asalin jihar da sauran ƙungiyoyi makamantansu sun yi kira da a dakatar da aikin gyaran da za a fara a kasuwar Terminus ta Jos saboda abinda suka kira da fuska biyu wajen rubuta yarjejeniyar kwantiragin aiki. A cewarsu, bai kamata a ce yarjejeniyar kwantiragin ta kasance a tsakanin gwamnati da masu ɗaukar nauyin aikin (Bankin Ja'iz) kawai ba. Ƙungiyoyin sun yi wannan kira ne a yayin wani taro wanda shugaban ƙungiyar Kiristoci (CAN) Rabaran Fr. Polycarp Lubo ya kira a ranar Litinin…
Read More
Tashin farashin baƙin mai da canji sun jawo min naƙasu a kasuwancina – Obasanjo

Tashin farashin baƙin mai da canji sun jawo min naƙasu a kasuwancina – Obasanjo

Daga AMINA YUSUF ALI Tsohon shugaban ƙasar Nijeriya a Jamhuriya ta biyu, Olusegun Obasanjo ya bayyana yadda tashin farashin baƙin mai da canji suke kawo masa naƙasu a kasuwancinsa. Shugaban ya ƙara da cewa, tashin farashin baƙin man yana da alaka da yadda ake gudanar da mulkin ƙasar nan ba yadda ya kamata ba. A cewar tsohon shugaban, tashin farashin yana jawo cikas sosai a kasuwancinsa na kifi. Mista Obasanjo wanda ya mallaki sashen kiwon kifi a gidansa dake Abeokuta ta jihar Ogun ya bayyana haka ga manema labarai a ranar Talatar da ta gabata a yayin taron ƙungiyar daidaita…
Read More
Gamayyar Ƙasashen Turai za ta maye gurbin amfani da gas ɗin Rasha da na Nijeriya

Gamayyar Ƙasashen Turai za ta maye gurbin amfani da gas ɗin Rasha da na Nijeriya

Daga AMINA YUSUF ALI a yayin da ake tsaka da yaƙin Yukiren da Rasha, Gamayyar Ƙasashen Turai (EU) ta sanar da dakatar da shigo da gas daga ƙasar Rasha, inda ta bayyana cewa, za ta dawo harkar cinikin gas ɗin da Nijeriya. Mataimakin darakta janar na sashen kula da makamashi na kwamitin Gamayyar Ƙasashen Turai, Matthew Balwdin, ya ce ya zo ƙasar Nijeriya a ƙarshen makon da ya gabata, inda ya gana da manyan jami'an ƙasar. Ya ƙara da cewa, an shaida masa cewa, Najeriya na ƙarfafa tsaro a yankin Neja Delta, inda a can ne ake samar da fetur…
Read More
Tsadar fulawa da kayan haɗi: Gidajen burodi sun sanar da sabon farashinsu

Tsadar fulawa da kayan haɗi: Gidajen burodi sun sanar da sabon farashinsu

Daga AMINA YUSUF ALI Masu gidajen burodi a Nijeriya sun bayyana yadda farashin biredi zai tashi nan gaba. Sabon farashin ana sa ran zai fara daga ranar Litinin ɗin da ta gabata wato 25 ga Yuli, 2022. Rahotanni sun bayyana cewa, a yanzu haka ma farashin biredin ya jima da tashi a wasu jihohin saboda abinda suka alaƙanta da tsadar fulawa da kayan haɗin burodin a Nijeriya. Rahotanni daga jihar Kogi sun bayyana cewa, tuni masu gidajen burodin suka ƙara farashin biredin da ƙarin kaso 20% a kan tsohon farashinsa. Wannan ƙarin farashin ya biyo bayan yakin aikin ƙasa bakiɗayan…
Read More