Kasuwanci

Gwamnati ta tallafa wa mata 8,000 da kudi N20,000 a Legas

Gwamnati ta tallafa wa mata 8,000 da kudi N20,000 a Legas

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta jaddada aniyarta ta kyautata rayuwar talakawa da marasa galihu a fadin kasa inda ta raba wa mata su 8,000 tallafin kudi na naira 20,000 ga kowaccensu a karkashin shirin nan nata na tallafa wa matan karkara da kudade. Ministar Jinkai da Agaji, Sadiya Umar Farouq ce ta bada jaddadin yayin kaddamar da shirin tallafa wa matan a Legas. Da take jawabi a wajen taron kaddamar da shirin a bisa wakilcin babban sakataren ma'aikatarta Bashir Nura Alkali, Sadiya ta ce, "Kudirinmu shi ne mu ga mata sama da 8,000 sun amfana da shirin a tsakanin…
Read More
An kashe naira miliyan 900 wajen samar da manhajar sayar da tikitin jirgin kasa – Amaechi

An kashe naira miliyan 900 wajen samar da manhajar sayar da tikitin jirgin kasa – Amaechi

Daga WAKILIN MU Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ya bayyana cewa an samar da dandalin sayar da tikitin jirgin kasa ta intanet na Hukumar Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC) a kan kudi naira miliyan 900 ta hanyar wata yarjejeniya ta shekara 10.Ministan ya bayyana haka ne kwanan nan sa'ilin da ya ke kaddamar da manhajar sayar da tikitin, ya na mai cewa hakkin kula da manhajar zai kasance ne a hannun wadanda aka yi yarjejeniyar da su na tsawon shekara 10, kana daga bisani ta koma karwashin kulawar NRC. A cewar sa, samun manhajar babban cigaba ne ga hukumar NRC da…
Read More
Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Gwamnati ta kashe naira tiriliyan 2 wajen sayen abinci a 2020

Daga UMAR M. GOMBE Babban Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Sha’anin Tattalin Arziki, Dakta Doyin Salami ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ta kashe kusan Naira Tiriliyan 2 wajen sayen kayayyakin abinci daga kasashen ketare tsawon watanni tara, lokacin da dukkanin iyakokin kan tudu ke rufe. Dakta Salami ya fadi haka ne a yayin da yake gabatar da jawabi a taron masu ruwa da tsaki kan makomar tattalin arzikin kasar nan da ya gudana ta kafar bidiyo a Legas a tsakiyar wannan makon. A cewar Dakta Salami duk da rufe iyakokin kan tudu da Nijeriya ta yi, sai da gwamnati…
Read More
FCMB ya matse kaimi wajen tallafa wa kananan ‘yan kasuwa

FCMB ya matse kaimi wajen tallafa wa kananan ‘yan kasuwa

Daga jaridar Manhaja Kawo yanzu, bankin FCMB ya ci gaba da kokarin da yake yi na tallafa wa kanana da matsakaitan 'yan kasuwa a fadin kasa. Idan dai za a iya tunawa, a kwanan nan ne aka zabi bakin FCMB a matsayin bakin da ya zarce kowane bakin a yankin Afirka mu'amala da 'yan kasuwa kanana da matsakaitansu. Lamarin da ya karfafa wa bankin gwiwa wajen tallafa wa mata masu kananan sana'o'i ta hanyar shirin nan nasa mai taken "SheVenture". Shirin SheVenture, shiri ne da bankin ya samar don bunkasa kananan 'yan kasuwa mata da kuma masu shirin soma kasuwanci,…
Read More
Bankin Zenith ne lambawan yanzu a bankunan Nijeriya

Bankin Zenith ne lambawan yanzu a bankunan Nijeriya

An zabi Bankin Zenith a matsayin banki na daya a jerin dukkan bankunan Nijeriya a yau. Hakan ta faru ne a wajen bikin bada kyaututtuka ga gwarzaye a bangaren aikin banki wanda mujallar The Banker da kamfanonin Finacial Times Group da ke London su ke shiryawa a kowace shekara. Bikin na bana, wanda aka gudanar a ran Laraba, sunan shi 'The Banker's Bank of the Year Awards 2020'. Da ma tun a farkon wannan shekarar mujallar da guruf din kamfanonin sun zabi bankin na Zenith a matsayin banki mafi daraja a kasar nan a bisa wani sikeli da su ka…
Read More