Kasuwanci

Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Daga WAKILIN MU Ofishin Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa na 'Zone C', ya ce ya samu nasarar kama kayayyakin da aka haramta shigo da su cikin ƙasa wanda harajinsu ya haura milyan N869 a Janairun da ya gabata. Kayayyakin da ofishin ya ce ya kama ciki har da katan 1,024 na magungunan da ba a yi musu rajista ba, da shinkafar ƙetare buhu 1,046, da katan 62 na sabulun, da mota ƙirar Toyota da dai sauransu. A cewar Comptroller Yusuf Lawal, haƙƙinsu ne tabbatar da cewa ana kiyaye dukkan ƙa'idojin da gwamnati ta shimfiɗa dangane da haramcin shigo da…
Read More
Buhari ya ƙaddamar da aikin layin dogo daga Kano Zuwa Nijar

Buhari ya ƙaddamar da aikin layin dogo daga Kano Zuwa Nijar

Daga BASHIR ISAH A Talatar da ta gabata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin gina layin dogo wanda zai tashi daga Kano-Katsina-Jibiya-Maraɗi, da kuma wanda zai ratse zuwa Dutse a jihar Jigawa. Da yake jawabi ta bidiyo daga fadarsa da ke Abuja yayin bikin ƙaddamawar, Buhari ya ce bayan kammala aikin hakan zai taimaka wajen bunƙasa harkokin tattalin arzikin ƙasa musamman ma hada-hadar kasuwanci a tsakanin Nijeriya da Nijar. Daga nan ya kira ga 'yan kasuwa da su yi amfani da wannan dama wajen gudanar da harkokin kasuwancin da ba su saɓa wa dokoki ba da nufin bunƙasa…
Read More
‘Yan kasuwa sun buƙaci a ɗaga farashin fetur

‘Yan kasuwa sun buƙaci a ɗaga farashin fetur

Daga AISHA ASAS 'Yan kasuwar man fetur sun ce bisa la'akari da yadda abubuwa ke tafiya a kasuwar ɗanyen mai ta duniya, kamata ya yi farashin fetur kan lita guda ya zama tsakanin N185 zuwa N200 a Nijeriya. Bayanan da Manhaja ta kalato sun nuna an samu tashin farashin fetur a kasuwar mai ta duniya a makon da ya gabata wanda hakan ya sanya 'yan kasuwar nuna damuwarsu kan yadda ba a aiwatar da cikakken shirin sakar wa 'yan kasuwar mara ba a harkar man fetur, lamarin da ya hana samun sauyin farashin litar fetur sama da watanni biyu A…
Read More
Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Legas: NAFDAC ta rufe kamfani mai sayar da kayayyakin da wa’adin amfaninsu ya ƙare

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC) ta rufe wani kamfanin sarrafa abinci a Jihar Legas bisa laifin sayar wa jama'a da sinadarin haɗa abinci (Thyme da Curry) bayan kuma wa'adin amfaninsu ya ƙare. NAFDAC ta ce ta ɗauki wannan mataki ne domin tsaftace Nijeriya daga abinci mara inganci domin ci gaba da kare lafiyar 'yan ƙasa. A sanarwar da jami'in yaɗa labarai na shiyya na hukumar Sayo Akintola ya fitar, Babbar Daraktar hukumar Prof. Mojisola Adeyeye ta bayyana damuwarta kan lamarin. Tana mai cewa za a ƙaƙaba wa kamfanin da lamarin ya…
Read More
Atiku ya roƙi gwamnati kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet

Atiku ya roƙi gwamnati kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet

Daga FATUHU MUSTAPHA Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya roƙi gwamnatin Shugaba Buhari kada ta dakatar da hada-hadar kuɗaɗen intanet wanda aka fi sani da 'cryptocurrency' a Turance. A Juma'ar da ta gabata Babban Bankin Nijeriya (CBN) aya bada umarnin bankuna da dangoginsu su rufe duka asusun da ke da alaƙa da harkar kuɗaɗen intanet ba tare da ɓata lokaci ba. A wata sanarwa da ya sanya wa hannu Asabar da ta gabata, Atiku ya ce kamata ya yi gwamnati ta ɗauki matakin sanya wa harakar ido maimakon daƙile ta baki ɗaya. Tare da bada misalin yadda hada-hadar kuɗaɗen…
Read More
CBN ya haramta wa bankuna hada-hadar kuɗaɗen intanet

CBN ya haramta wa bankuna hada-hadar kuɗaɗen intanet

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bai wa bankuna umarnin su rufe duk wani asusun ajiya da karɓar kuɗaɗe a banki da ke da alaƙa da cinikin kuɗin intanet (cryptocurrency). A Juma'ar da ta gabata CBN ya aike wa bankunan umarnin nasa zuwa bankuna masu karɓar ajiyar kuɗaɗe (DMB) da hukumomi masu hada-hadar kuɗaɗe (NBFI) da makamantansu, a kan su gaggauta daƙile dukkan asusun da ake amfani da su wajen hada-dahar kasuwar sulallan intanet (bitcoin). Idan dai za a iya tunawa a Janairun 2017 ne CBN ya bayyana cewa ana amfani da hada-hadar kuɗaɗen intanet irin sulallan bitcoin…
Read More
Hukumar Kwastam ta tara bilyan N4b a cikin wata guda

Hukumar Kwastam ta tara bilyan N4b a cikin wata guda

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Yaƙi da Fasa Ƙwauri ta Ƙasa reshen Oyo/Osun ƙarƙashin jagorancin Comptroller AR Abdulkadir, ta ce ta samu nasarori da daman gaske wajen aiwatar da harkokinta. Yayin ganawar da ya yi da manema larabai a Alhamis da ta gabata, Comptroller Abdulkadir ya ce a watan Janairun da ya gabata kaɗai sun tara wa gwamnati kuɗin shiga da ya kai sama da bilyan N4.895. Ya ce tsakanin Nuwamba da Janairun da suka gabata, sun yi nasar kama ɓatagari da dama da kuma kayayyakin fasa ƙwauri wanda a kiyasce harajinsu ya haura Naira milyan 393. A cewar jami'in, kayayyakin…
Read More
Bankin Zenith ya ciri tuta

Bankin Zenith ya ciri tuta

Daga FATUHU MUSTAPHA A karo na huɗu a jere, bankin Zenith ya sake zama bankin da ya ɗara takwarorinsa ingancin tsarin gudanarwa a Nijeriya kamar yadda mujallar Banker Magazine ta nuna. Daga jerin bankuna 'yan sahun gaba su 500 da mujallar ta nuna a 2021, ta ayyana Bankin Zenith a matsayin bankin da ke kan gaba wajen tsarin aiki a Nijeriya. Mujallar ta nuna cewa, ƙarfin jarin Bankin Zenith ya kai Dalar Amurka milyan 275 wanda hakan ya sa ya zama bankin da ya samu cigaba daga matsayi na 392 a 2020 zuwa matsayi na 390 a 2021 a matakin…
Read More
Jami’an kwastam sun yi kamu a  Ogun

Jami’an kwastam sun yi kamu a Ogun

Daga WAKILIN MU A safiyar Talata (02/02/2021), wasu da ake zargin 'yan fasa-ƙwauri ne suka kai wa jami'an Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri na shiyyar 'Zone A' hari yayin da suke bakin aiki a kan babban hanyar Abeokuta a jihr Ogun. Bayanan da jaridar Manhaja ta samu sun nuna cewa, waɗanda lamarin ya shafa sun yi haka ne domin tirjiya daga kamun jami'an a daidai lokacin da suke ƙoƙarin arcewa da shinkafar ƙetare maƙare cikin motocinsu. Bayanai sun nuna cewa, bayan da jami'an Kwastam suka kama motocin ne sai wasu ɓatagari da ke goyon bayan 'yan fasa-ƙwaurin suka haɗa kansu suka…
Read More
Nijeriya za ta fi Indiya cin gajiyar kasuwancin fasaha a nan gaba, inji NITDA

Nijeriya za ta fi Indiya cin gajiyar kasuwancin fasaha a nan gaba, inji NITDA

Daga UMAR M. GOMBE Shugaban Hukumar Bunƙasa Ilimin Fasahar Zamani NITDA, Malam Kashifu Inuwa Abdullahi, ya bayyana cewa shirye-shiryen hukumar wajen bunƙasa kasuwanci ta fuskar amfani da kafofin intanet a Nijeriya sun yi nisa, inda Nijeriya za ta zarta Indiya damar kasuwancin fasahar zamani. Babban Daraktan ya shaida haka ne ga manema labarai a babban ofishin hukumar dake Abuja, a yayin da yake bayyana matakan da hukumar ke ɗauka don ganin Nijeriya ta bi sahun ƙasashen duniya a fanin kimiyya da fasahar zamani a ɓangaren kasuwanci. Ya ce hukumar ta zo da wani tsari da ake kira 'Strategic Roadmap' wanda…
Read More