Kasuwanci

Kasuwancinmu na yankin Afirka ya fi ko’ina riba – Bankin UBA Africa

Kasuwancinmu na yankin Afirka ya fi ko’ina riba – Bankin UBA Africa

Daga AMINA YUSUF ALI Shugaban Bankunan UBA na Afirka ya bayyana yadda rukunin bankunan nasu suke cin mafi yawan riba a yankin Afirka fiye da ko'ina. Ya bayyana cewa, yankin Afirka yana ba wa bankin nasu ribar da ta kai kusan kaso 50 na dukkan cinikin da kamfanin nasu yake samu. Daraktan zartarwa/Babban jami'in zartarwa na UBA a Afirka, Abiola Bawuah shi ya bayyana hakan. Misis Bawuah ta qara da cewa, kowanne rseshe na bankin UBA a Afirka a zaune yake da ƙafafunsa. Wannan lissafi ma ya ahafi har da ƙasaahen Afirka wanda yaƙi ya illata su. Ko'ina dai ana…
Read More
CBN ya ƙaryata iƙirarin rage darajar Naira akan Dala

CBN ya ƙaryata iƙirarin rage darajar Naira akan Dala

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Babban Bankin Najeriya CBN ya mayar da martani kan rahotannin da ke cewa ya rage darajar Naira zuwa kusan Naira 630 akan dala. Tun da farko dai rahoton faɗuwar darajar kuɗin ne ɗaya daga cikin jaridun ƙasar ta ruwaito. Sai dai a wata sanarwa a ranar Alhamis, muƙaddashin shugaban sashen sadarwa na bankin, Dr Isa Abdulmumin, ya bayyana hakan a matsayin ƙarya. “Rahoton labarai, wanda a tunanin jaridar ya keɓanta, cike yake da ƙarya da ɓatanci, wanda ke nuna yiwuwar jahilci da gangan game da yadda kasuwar canji ta Nijeriya ke aiki,” inji shi.…
Read More
TUC ta buƙaci Shugaba Tinubu ya dakatar da cire tallafin mai

TUC ta buƙaci Shugaba Tinubu ya dakatar da cire tallafin mai

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar 'Yan Kasuwa (TUC), ta yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu da ya dakatar da manufarsa ta cire tallafin mai baki ɗaya. Ƙungiyar ta ce mambobinta sun kaɗu matuƙa bayan da suka ji Shugaban ya ambaci batun cire tallafin mai yayin da yake jawabi jim kaɗan bayan rantsar da shi a ranar Litinin. Da suke jawabi a wajen taron manema labarai da suka shirya ranar Talata a Abuja, Shugaban TUC na ƙasa, Festus Osifo da Sakatarensa Nuhu Toro, sun ce sun sa ran Shugaban ya zama wayayye game da matsalar da ke gaban ƙasar nan. Osifo…
Read More
Ƙarancin mai ya kunno kai sa’o’i bayan da Shugaba Tinubu ya sanar da cire tallafin mai

Ƙarancin mai ya kunno kai sa’o’i bayan da Shugaba Tinubu ya sanar da cire tallafin mai

Da alama layukan ababen hawa a gidajen mai ya dawo a Jihar Legas sa'o'i bayan da Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya sanar da cire tallafin mai. Bayanai sun ce an ga cinkoson ababen hawa a gidajen mai ɗin NNPC a yankunan Ikeja da Alausa waɗanda ke jiran su sha mai. Ya zuwa haɗa wannan labari, an ga da daman gidan mai masu zaman kansu a yankunan ba su sayar da mai. A jawabinsa, Shugaba Tinubu ya ce masu ƙumbar susa kaɗai ke amfna da tallafin mai amma ban da talakawa. Ya ce, “Mun yaba da ƙoƙarin gwamnati mai barin gado…
Read More
CBN ta ƙwace lasisin wasu bankuna 132

CBN ta ƙwace lasisin wasu bankuna 132

Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya amince da soke lasisin da aka ba wasu bankunan ƙananan kasuwanci 132 da suke harkokinsu a Nijeriya. Emefele ya amince da amshe lasisin a ranar Litinin ɗin da ta gabata, a cewar wani jawabi da CBN ɗin ya saki a ranar Talata. A cewar jawabin, Bankin ya ƙaddamar da hukunci a kan ƙananan bankunan kasuwanci bankunan da ba sa yin biyayya ga ƙa'idojin CBN da kuma sharuɗɗan amfani da lasisin. Daga cikin dalilan da ya sa bankin ya ƙwace lasisin, ya bayyana cewa ya ƙaddamar da wannan aikin…
Read More
CBN ya yi ƙarin kuɗin ruwa zuwa kashi 18.5%

CBN ya yi ƙarin kuɗin ruwa zuwa kashi 18.5%

Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya yi ƙarin kuɗin ruwa daga kashi 18 zuwa kashi 18.5 cikin 100. Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ne ya sanar da hakan a ranar Laraba bayan kammala taron kwamitin da ke kula ɓangaren a hedikwatar CBN da ke Abuja. Wannan shi ne karo na uku da bankin ke ƙarin kuɗin ruwan. Da yake yi wa manema labarai ƙarin haske game da batun, Emefiele ya ce ƙalubalen tsadar da ake fuskanta a fannin makashi na daga dalilan da suka haifar da ƙarin. Masana tattalin arziki sun ce mai yiwu ƙarin kuɗin ruwan da bankuna kan ɗora a…
Read More
Muna cigaba da gamsuwa da jagorancin shuwagabanin kasuwar Mile12 a Legas – Alhaji Ummaru

Muna cigaba da gamsuwa da jagorancin shuwagabanin kasuwar Mile12 a Legas – Alhaji Ummaru

Daga Ummaru Dan Gara a Legas Sakataran Kuɗi na Ƙungiyar ’Yan Karas a Jihar Legas, Alhaji Ummaru Dan gara Sarina ta Ƙaramar Hukumar Garko, mazaunin Unguwar mile12 da ke Legas, ya bayyana cewa, shi da sauran al'ummar kasuwar mile12 suna ƙara gamsuwa da jagorancin shugabam a kasuwar mile12, Alhaji shehu Usman jibirin samfam tare da sauran shuwagabannin ɓangarorin kasuwar ta kewayanta gaba ɗaya. Alhaji Ummaru Dan Gara ya yi wannan tsokaci ne a gidansa da ke Sarina jim kaɗan bayan kammala karɓar baƙuncin waɗansu ɗimbin al'ummar da suka fito daga sassa daban-daban na ƙasar nan, su ka shigo jihar Kano…
Read More
MTN na shirin ƙara kuɗin kira da farashin data

MTN na shirin ƙara kuɗin kira da farashin data

Kamfanin sadarwa na MTN ya ce yana shirin ƙara kuɗin kira da farashin Data saboda tsadar rayuwa da yawan harajin da aka ɗora wa kamfanin. Bayanin haka na ƙunshe ne cikin rahoton zangon farko na da kamfanin ya fitar kwanan nan. Kamfanin ya ce da alama yanayin kasuwanci a ragowar 2023 zai kasance mai tattare da ƙalubale. Don haka kamfanin ya ce shi ma zai duba sannan ya yi abin da ya dace don iya tafiyar da harkokinsa a wannan lokaci na ƙalubale. Kamfanin ya ƙara da cewa, ƙarin farashin shi ne mafita a wannan hali, saboda ta haka ne…
Read More
An kafa ƙungiyar mata masu kasuwancin intanet a Kano

An kafa ƙungiyar mata masu kasuwancin intanet a Kano

Daga AMINA YUSUF ALI Mata masu gudanar da kasuwanci a shafukan intanet a jihar Kano da ke Arewacin Najeriya sun kafa wata ƙungiya mai suna Women Online Vendors Association (WOVA) da za ta samar da aminci tare da kyautata hulɗa tsakanin mai saye da mai sayarwa. Shugabar ƙungiyar ta WOVA Hajiya Ayat Uba Adamu ta bayyana wa majiyarmu cewa sun kafa ƙungiyar ne da nufin haɗa kan matan da suke gudanar da kasuwancinsu a shafukan intanet tare kuma da samar da aminci tsakanin masu saye da sayarwa. “Samar da aminci tsakanin masu saye da sayarwa ta hanyar karkaɗe ɓata gari…
Read More