Kasuwanci

Haraji: An ba wa Tinubu shawarar haɗe hukumomin NIMASA, FIRS da Kwastam a inuwa guda

Haraji: An ba wa Tinubu shawarar haɗe hukumomin NIMASA, FIRS da Kwastam a inuwa guda

Daga AMINA YUSUF ALI Kwamitin mashawartan gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinubu sun ba shi shawarar haɗe hukumomin NIMASA, hukumar haraji (FIRS), da kuma hukumar Kwastam, dukkansu su kasance a ƙarƙashin hukumar tattara haraji ta tarayya wato FIRS. Haɗewar a cewar kwamitin mashawartan za ta taimaka wajen amsar haraji na kai tsaye da ba na kai tsaye ba a madadin gwamnatin tarayya. Majalisar ta nemi a yi garambawul ga dokar tattalin arziki cikin gaggawa don ba wa shugaban ƙasa damar zartar da wannan hukunci. Wannan kwamitin mashawartan wacce Mista Tinubu ya haɗa don tallafawa wajen samar da tattalin arziki mai…
Read More
Bill Gates da Ɗangote sun jinjina wa Tinubu kan cire tallafin

Bill Gates da Ɗangote sun jinjina wa Tinubu kan cire tallafin

Daga BASHIR ISAH Hamshaƙin ɗan kasuwar nan Aliko Ɗangote da takwaransa Bill Gates da ya kasance Shugaban Bill and Melinda Gates Foundation, sun taya Shugaban Ƙasa Bola Tinubu murnar cire tallafin man da ya yi haɗi da sauran nasarorin da ya samu ya zuwa yanzu. Ɗangote ya bayyana hakan ne a ganawar da ya yi da manema labaran Fadar Shugaban Ƙasa jim kaɗan bayan ganawarsu da Shugaba Tinubu a ofishinsa a ranar Litinin. A cewar Ɗangote, ana sa ran cire tallafin ya zama mabuɗi na hanyoyin samun ƙarin kuɗaɗe ga ƙasa don bai wa gwamnati zarafin zuba jari a sauran…
Read More
Hukumar hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya ta haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet na Binance

Hukumar hada-hadar hannayen jari ta Nijeriya ta haramta hada-hadar kuɗaɗen intanet na Binance

Daga AMINA YUSUF ALI Matakin na ƙunshe ne a cikin wata sanarwar da hukumar ta wallafa a shafinta na intanet. Hukumar hada-hadar hannayen jari ta ƙasar ta ce kamfanin na Binance bai yi rajista da ita ba, a don haka ne ta ce ta haramta ayyukan kamfanin a faɗin ƙasar nan. Sanarwar ta kuma gargaɗi 'yan ƙasar da ke mu'alama da kamfanin da su dakata, in ba haka ba kuwa duk abinda ya same su to su kuka da kansu. Sanarwar ta ci gaba da cewa ''An nusar da hukumar kula da hada-hadar hannayen jari ta Najeriya game da shafin…
Read More
Layin lantarki na Shiroro-Kaduna ya lalace – KEDCO

Layin lantarki na Shiroro-Kaduna ya lalace – KEDCO

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na KEDCO, ya yi ƙarin haske dangane da ƙarancin wutar lantarki da ake fuskanta a jihohin Kano da Katsina da kuma Jigawa. Kamfanin a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi wadda shugaban sashen yaɗa labaran kamfanin, Sani Bala Sani, ya sanya ma hannu ta ce, lamarin ya faru ne sakamakon lalacewar layin wutar na Shiroro-Kaduna 330KV. Kamfanin ya bayyana cewa tuni dai TCN ta fara aikin gyaran layin wutar wanda ake saran kammalawa a jiya lahadi. Daga ƙarshe ya bai wa al'umma haƙuri tare da bada tabbacin…
Read More
CBN zai sauya ƙa’idojin kasuwar canji

CBN zai sauya ƙa’idojin kasuwar canji

Daga BASHIR ISAH Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bayyana cewa zai sauya ƙa'idoji na gudanar da kasuwar canji da suka haɗa da soke tsarin musayar canjin kuɗaɗe da dama da aiwatar da tsarin bai-ɗaya na musayar kuɗi da barin kasuwa ta yi halinta game da farashin canjin kuɗaɗe. CBN ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba. Bankin ya ce manufar waannan matakan ita ce ƙara yawan kuɗin ruwa da daidaito, baya ga tasirin hakan da za a iya haifarwa nan da nan ga harkokin kuɗaɗen ƙasar. CBN ya sanar da soke tsarin raba kasuwar musayar…
Read More
Za mu taimaka wa gwamnati da motocin bas 100 saboda cire tallafin mai – DAPPMAN

Za mu taimaka wa gwamnati da motocin bas 100 saboda cire tallafin mai – DAPPMAN

Ƙungiyar Dillancin Man Fetur a Nijeriya ta 'Depots and Petroleum Products Marketers Association of Nigeria' (DAPPMAN) ta yi alƙawarin samar da manyan motocin bas 100 don tallafa wa yunƙurin gwamnati na cire tallafin man fetur. Da take magana bayan ganawarsu da Shugaba Bola Tinubu ranar Laraba, shugabar ƙungiyar Dame Winifred Akpani ta ce suna goyon bayan matakin gwamnati na cire tallafin 100 bisa 100. Akpani ta ce motocin ƙirar gida ne kuma masu amfani da iskar gas maimakon fetur. "Cire tallafin mai ba ya nufin tsawwala farashinsa ko kuma rage yawansa a tsakanin 'yan Nijeriya," in ji ta. "Magana ce…
Read More
IMF ta ja hankalin Nijeriya kan kuɗaɗen shiga, kashe kuɗi da kuma cin bashi

IMF ta ja hankalin Nijeriya kan kuɗaɗen shiga, kashe kuɗi da kuma cin bashi

Daga AMINA YUSUF ALI Wakili daga Gidauniyar Kudi ta Ƙasa da Ƙasa (IMF) a ofishinsu na Nijeriya, Ari Aisen, ya bayyana cewa, ya kamata Nijeriya ta san yadda za ta tsara yadda take kashe kuɗinta in dai har tana son ta warware matsalolin bashin da take ciki. Aisen ya bayyana haka ne a yayin sha'anin da Talabijin ɗin yanar gizo ta Proshare WebTV ta shirya a kwanan nan. A cikin jawabin nasa ya yi kira ga ofishin kula da bashin (DMO) a kan buƙatar Nijeriya ta duba al'amarin rashin kuɗin shiga da ake fama da shi. A cewar Aisen, “Ofishin…
Read More
Zan yi bakin ƙoƙari wajen kawo cigaba a ɓangaren kasuwar tattasai a Legas – Aminu Musa

Zan yi bakin ƙoƙari wajen kawo cigaba a ɓangaren kasuwar tattasai a Legas – Aminu Musa

Daga DAUDA USMAN a Legas Sabon shugaban kulawa da cigaban kasuwancin tattasai, atarugu da shambo a Kasuwar Mile 12 dake Legas, Alhaji Aminu Musa, ya bayyana cewar zai yi iyakar ƙoƙarinsa wajen kawo cigaban kasuwancin tattasai, tarugu da shambo a Legas. Alhaji Aminu Musa ya yi wannan tsokaci ne a ofis ɗin sa dake kasuwar Mile-12 a Legas a lokacin da yake karvar baƙuncin waɗansu daga cikin 'yan kasuwar waɗanda suka zo taron walimar taya shi murnar zama sabon shugaban ɓangaren tattasai, tarugu da shambo. Aminu ya ce yana yi wa kowa fatan alheri dangane da wannan al'amari, da fatan…
Read More
Ƙasa mafi arziki a Turai ta tsunduma cikin karayar arziki

Ƙasa mafi arziki a Turai ta tsunduma cikin karayar arziki

Daga AMINA YUSUF ALI Ƙasa mafi arziki a Turai, wato Jamus ta tsunduma a cikin hakin matsin tattalin arziki. A wani rahoto da aka tattara a ofishin tattara bayanai a ranar Alhamis ɗin da ta gabata ya bayyana cewa, gabaɗaya ƙarfin tattalin arzikin ƙasar (GDP) ya ragu zuwa kaso 0.3 a cikin watanni huɗun farkon shekara. Jamus, ƙasar da ta fi kowacce qasa a arziki a Turai, kuma ta huɗu mafi arziki a duniya bakiɗaya, ta tsunduma cikin matsin tattalin arziki a watanni huɗun farko na shekarar nan. Rahotanni sun bayyana cewa, tattalin arzikin ya yi ƙasa sosai a watanni…
Read More
Fa’idojin cire tallafin man fetur guda biyar – Masana

Fa’idojin cire tallafin man fetur guda biyar – Masana

Daga AMINA YUSUF ALI A ranar Litinin ɗin da ta gabata ne fai shugaban ƙasar Nijeriya Bola Tinubu ya ba da sanarwar cire tallafin man fetur jim kaɗan bayan rantsar da shi a matsayin shugaban ƙasar. Wato babu kasonsa a cikin kasafin kuɗi bayan wannan sabon wata da ya kama na Yuni. Shi tallafin man fetur wani tallafi ne daga gwamnati wanda take ba w atalaka, don rage masa tsadar man fetur. Don ya samu sauƙin farashin sayen man. Talakawa sun tashi hankalinsu matuƙa game da wannan cire tallafin domin ana ganin talakan zai iya shiga matsin tattalin arziki da…
Read More