Nishadi

Ganduje ya naɗa Khalid Musa hadiminsa kan sha’anin Kannywood

Ganduje ya naɗa Khalid Musa hadiminsa kan sha’anin Kannywood

Daga BASHIR ISAH Gwamna Abdullahi Ganduje na Jihar Kano ya naɗa Khalid Musa a matsayin Babban Hadimi na Musamman (SSA) kan sha'anin masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood, naɗin da ya soma aiki daga ranar 8 ga Fabrairun 2022. Sanarwar naɗin na ƙushe ne cikin wasiƙar da sashen REPA da ke ƙarƙashin Ofishin Sakataren Gwamnatin Kano, wadda Babbar Sakatariyar REPA, Bilkisu Shehu Maimota ta sanya wa hannu a madadin Sakataren Gwamnatin Jihar. A cewar wasiƙar, an naɗa Musa a matsayin SSA ne duba da jajircewarsa, sadaukarwa a bakin aiki, sanin makamar aiki, ƙwazo da kuma biyayyar da yake da su, wanda…
Read More
Hukumar NFC ta naɗa Shugaban MOPPAN, Dr. Sarari, jagoran kwamitin bajekolin finafinai na ƙasa

Hukumar NFC ta naɗa Shugaban MOPPAN, Dr. Sarari, jagoran kwamitin bajekolin finafinai na ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An naɗa Shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinan Hausa ta Nijeriya (MOPPAN), Dr. Ahmad Muhammad Sarari, a matsayin Shugaban Ƙaramin Kwamitin Shirya Bajekoli na Ƙasa (Zuma Film Festival) na bana, wato shekara ta 2022, mai kula da Shiyyar Kano da Kaduna a bajekolin da zai gudana a ranakun 2 zuwa 8 ga Afrilu, 2022. Naɗin na ƙunshe ne a cikin wata wasiƙa da Daraktan Shirin Bajelkolin, Edmund Peters, ya aike wa Shugaban na MOPPAN mai ɗauke da kwanan watan 15 ga Fabrairu, 2022, kuma Blueprint Manhaja ta samu kwafi. A cikin wasiƙar, hukumar da…
Read More
Hirar Ladin Cima: MOPPAN da AFMAN sun jagoranci sulhu tsakanin Naziru Sarkin Waƙa da sauran ‘yan fim

Hirar Ladin Cima: MOPPAN da AFMAN sun jagoranci sulhu tsakanin Naziru Sarkin Waƙa da sauran ‘yan fim

Daga WAKILINMU A jiya Litinin 14 ga Fabrairun 2022 ne, ƙungiyar MOPPAN tare da haɗin gwiwar ƙungiyar AFMAN da kuma Kwamitin Dattawan Kannywood suka yi zaman sulhu tsakanin ‘ya’yan masana’antar da suka sami rashin fahimta sakamakon hirar Hajiya Ladin Cima da BBC Hausa ta watsa kwanan nan. Zaman da aka yi a zauren taron Kannywood TV da ke Kano, ya samu halartar shugabannin ƙungiyoyin MOPPAN da na AFMAN da shugabannin ƙungiyar mata na 'K-WAN' da kuma dattawan Kannywood. Daga cikin Dattawan da suka halarci taron, akwai akwai, Malam Auwalu Masha, Mai’unguwa Ibrahim Mandawari, Ibrahim Gumel, da Kabiru Maikaba. Sanarwar da…
Read More
MOPPAN ta kama hanyar magance rikicin Kannywood

MOPPAN ta kama hanyar magance rikicin Kannywood

Daga BASHIR ISAH A yayin da ake ci gaba da tafka zazzafar muhawara, Ƙungiyar Masu Shirya Fina-finai ta MOPPAN ta bayyana cewa, ta miƙe domin ɗaukar matakin daƙile rikicin da ya kunno kai a masana'antar Kannywood tun bayan da jaruma Ladin Cima ta bayyana cewa abin da ake biyan ta a masana'antar bai taka kara ya karya ba yayin wata tattaunawa da BBC Hausa ta yi da ita. A bayyane yake cewa har ila yau, zancen na ci gaba da jan hankalin al'umma, musamman mabiya lamurran fina-finan Hausa, inda kowa ke tofa albarkacin bakinsa dangane da batun. Lamarin da ya…
Read More
Ƙungiyar ’yan fim ta Arewa ta zaɓi Sani Sule Katsina a matsayin sabon shugabanta

Ƙungiyar ’yan fim ta Arewa ta zaɓi Sani Sule Katsina a matsayin sabon shugabanta

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Ƙungiyar masu shirya fim ta Arewa, wato Arewa Film Makers Association Of Nigeria, ta gudanar da sabon zaɓen shugabannin da za su tafiyar da shugabancin ta na gaba a taron da ta gudanar a ranar Lahadin makon jiya. Taron wanda aka gudanar da shi da yammacin ranar Lahadi, 23/1/2022 a wajen taro na Hazeen Event Center da ke cibiyar digan gona a cikin garin Kano, ya samu halarta dukkan wakilai daga jihohin arewacin ƙasar nan da sauran masu ruwa da tsaki a ƙungiyar. Tun da farko da yake bayanin yadda taron ya gudana, shugaban kwamitin…
Read More
Sarkin waƙa Naziru ya bai wa Ladin Cima kyautar Miliyan biyu

Sarkin waƙa Naziru ya bai wa Ladin Cima kyautar Miliyan biyu

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Naziru Ahmed Sarkin Waƙa ya gwangwaje Ladin Cima, wacce aka fi sani da Tambaya, da kyautar Naira miliyan 2 domin ta fara kasuwanci da magance wasu matsalolinta. Naziru Sarkin Waƙa ya bayyana hakan ne a sahihin shafinsa na Facebook. A makon da ya gabata ne dai Tambaya, wacce ta daɗe tana harkar fim a masana'antar Kannywood, ta tada ƙura, bayan da ta yi wata hira da BBC Hausa, inda ta ce ba a taɓa ba ta sama da Naira dubu 2 ko 3 idan ta yi fim ba, Wanda hirar ta haifar da ce-ce-ku-ce tsakanin…
Read More
Zaɓen sabbin shugabannin ƙungiyar MOPPAN ya zo da sabon salo

Zaɓen sabbin shugabannin ƙungiyar MOPPAN ya zo da sabon salo

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano  Haɗaɗɗiyar ƙungiyar ƙwararru ta masu shirya fim ta ƙasa, wato ‘Motion Picture Practitioners Associations of Nigeria’ (MOPPAN), ta gudanar da zaɓen sabbin shugabanninta bayan kammala wa'adin shugabancin shugabannin na tsawon shekaru biyu, kamar yadda tsarin mulkin ƙungiyar ya tanada. Zaɓen dai an gudanar da shi ne a ranar Juma'ar da ta gabata a babban ɗakin taro na otel ɗin Ni'ima da ke cikin garin Kano. Taron, wanda kafin gudanar da shi aka fara da Babban Taron Ƙungiyar na Ƙasa, wato 'Congress', wanda a lokacin aka yi zaman Gyaran Kundin Tsarin Mulkin Ƙungiyar, inda aka shafe…
Read More
Kannywood: Babban Kwamandan Hisbah ya watsa wa Shugaban Hukumar Finafinan Kano ƙasa a ido

Kannywood: Babban Kwamandan Hisbah ya watsa wa Shugaban Hukumar Finafinan Kano ƙasa a ido

Daga WAKILINMU a Kano A daidai lokacin da Shugaban Hukumar Tace Finafinai na Jihar Kano, Malam Isma’il Na’abba Afakallahu, bai halarci taron rantsarwa da liyafar cin abincin dare da Gwamnan Jihar Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya shirya wa sababbin zaɓaɓɓun shugabannin Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa (MOPPAN) a Gidan Gwamnatin Jihar Kano ba, shi kuwa Babban Kwamandan Hisbah na Jihar ta Kano, Sheikh Harun Muhammad Ibn Sina, ya halarci taron ne, inda har ma gabatar da addu’o’i a wajen gangamin, ya na mai sanya albarka ga masu sana’ar ta shirya finafinan Hausa a Kano da ma ƙasa…
Read More
Kundin Miftahul Futuhat ya zo da sabon salo a bege

Kundin Miftahul Futuhat ya zo da sabon salo a bege

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Cika da bunƙasar mawaƙi ita ce ya zamo ya shahara a dukkan salon waƙar da ya sa a gaba zai yi ta. Sarkin waƙar Masarautar Dutse, kuma Ɗan Buran na Masarautar Gobir, Aminu Ladan Abubakar Ala, yana ɗaya daga cikin mawaƙan wannan zamani a ƙasar Hausa da Allah ya yi wa wannan baiwa. Domin kuwa yana da baiwar shirya waƙa a kowanne ɓangarori na rayuwa wanda idan ya yi za ka ji kamar a nan fasahar sa ta ƙare, amma daga ya zo da wani salon sai kuma a ji a nan ma ya zama…
Read More
An fara haska fim ɗin ‘Hikima’ a sinima

An fara haska fim ɗin ‘Hikima’ a sinima

Masu kallo sun fara tantance finafinan da za su kalla – Alhaji Sheshe Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Fitaccen furodusa a masana'antar finafinai ta Kannywwod Mustapha Ahmad, wanda aka fi sani da Alhaji Sheshe, ya bayyana sauyin zamani da aka samu a duniyar fim shine ya kai su ga sauya akalar aikin su zuwa aiki mai nagarta, domin a yi tafiya irin yadda ake gudanar da harkar kasuwancin fim a duniya. Don haka ne ma su ka shirya fim ɗin 'Hikima' wanda yake ɗauke da labari mai ban al'ajabi. Mustapha Ahmad ya bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar su da…
Read More