Nishadi

An gudanar da taron ƙaddamar da fim ɗin ‘Lu’u-Lu’u’

An gudanar da taron ƙaddamar da fim ɗin ‘Lu’u-Lu’u’

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Bayan kammala shirya katafaren fim ɗin wanda ya zo da wani sabon salo na ban mamaki. Kamfanin shirya finafinai na 'Kannywwod Executive' ya shirya taron ƙaddamar da shi kafin a ɗora shi a shafin su na 'YouTube' wanda a ke sa ran za a fara kallon sa a farkon shekarar nan ta 2022. Taron, wanda aka gudanar da shi a ranar Litinin, 27/12/2021, a wajen taro na Ali Jita da ke Lawan Dambazau Road a Kano, ya samu halartar manya daga ciki da kuma wajen masana'antar finafinai ta Kannywwod. Tun da farko da ya ke jawabi…
Read More
Majalisar Dattawan Kannywood ta kai ziyarar ta’aziyyar rasuwar Bashir Tofa

Majalisar Dattawan Kannywood ta kai ziyarar ta’aziyyar rasuwar Bashir Tofa

Daga NASIR S. GWANGWAZO A yammacin ranar Litinin, 3 ga Janairu, 2022, wato ranar da aka yi jana’izar marubuci kuma ɗan siyasa a Nijeriya, Alhaji Bashir Othman Tofa, rasuwa, Majalisar Dattawan Kannywood ta kai ziyarar ta’aziyya gidansa da ke Gandun Albasa a Birnin Kano. Wannan ya biyo bayan taron da majalisar ta gabatar ne a daren Lahadin da ta gabata, wato 02 Janairu, 2022, inda ta shirya liyafar taya murnar shigowar sabuwar shekara lafiya, to amma sai aka wayi gari da rasuwar hamshaƙin dattijon ƙasar, inda nan da nan dattawan na Kannywood suka sake tattara kansu, suka ɗunguma wajen ta’aziyya. …
Read More
Babu ɗan siyasar da ya taimaki Kannywood kamar Sanata Barau – Sani Indomie

Babu ɗan siyasar da ya taimaki Kannywood kamar Sanata Barau – Sani Indomie

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano A daidai lokacin da guguwar siyasar 2023 ta fara kaɗawa, su ma' yan fim da su ke shiga harkar siyasa sun fara motsi domin ganin harkar ba ta bar su a baya ba. Sani Ali Abubakar, wanda aka fi sani da Furodusa Sani Indomie yana ɗaya daga cikin 'yan fim da su ke shiga harkar siyasa, don haka ne mu ka ji ta bakin sa kan irin matakin da za su ɗauka dangane da zave mai zuwa don ganin sun samar wa da masana'antar cigaban da a ke buƙata, in da ya fara da cewar.…
Read More
Har yanzu Kannywood ba ta san ciwon kanta ba, inji Abdulkareem Muhammad

Har yanzu Kannywood ba ta san ciwon kanta ba, inji Abdulkareem Muhammad

*Yadda taron Karramawa na KILAF 2021 ya gudana Daga MUKHTAR YAKUBU, a Kano Tsohon Shugaban Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinan Hausa ta Ƙasa (MOPPAN), Alhaji Abdulkareem Mohammed, ya bayyana cewa, masana’antar shirin fim ta Kannywood har yanzu ba ta gama sanin ciwon kanta ba. Abdulkareem ya bayyana hakan ne a yayin gudanar da bajekoli da kuma karramawa na KILAF a Birnin Kano da aka kammala kwanan nan. Taron bajekolin finafinai da karramawa mai taken "Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Fastival" wato KILAF AWARD da aka saba gudanarwa a duk shekara a bana ma an gudanar da shi…
Read More
Fim ɗin ‘Fanan’ ya fito da ni idon duniya – Jaruma Sabira Mukhtar

Fim ɗin ‘Fanan’ ya fito da ni idon duniya – Jaruma Sabira Mukhtar

DAGa MUKHTAR YAKUBU, a Kano Sabuwar jaruma a masana'antar fina-finan Hausa ta masana’antar Kannywwod, Sabira Mukhtar, tana ɗaya daga cikin jarumai mata da a ke ganin nan gaba kaɗan za ta zamo babbar jaruma, saboda irin rawar da ake ganin ta taka a cikin fim ɗin 'Fanan'. Duk da cewar ba shi ne fim ɗinta na farko ba, amma dai fim ɗin 'Fanan' shi ne ya fito da ita. A cikin tattaunawar su da wakilinmu, jarumar ta yi bayani a kan shigowarta harkar fim, da kuma yadda fim ɗin 'Fanan' ya ɗaga darajarta, har ya zamo abin alfahi a gare…
Read More
Mawaƙan Annabi suna rayuwa ne a gaɓa mai haɗari, inji Mahmoud Nagudu

Mawaƙan Annabi suna rayuwa ne a gaɓa mai haɗari, inji Mahmoud Nagudu

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Mahmoud Isma’il Ibrahim, wanda aka fi sani da Mahmoud Nagudu, fitaccen mawaƙi ne a fagen yabon Manzon Allah (SAW) tun yana ƙaramin yaro, sai dai ya yi fice ne a fagen waƙoƙin fim a shekarun baya. Amma dai yanzu ya daɗe ba a jin ɗuriyarsa a fagen waƙoƙin Nanaye, sai na yabon Manzon Allah kaɗai. Kasancewarsa mai ilimi a fagen yabon, ya sa Wakilin Manhaja a Kano, Mukhtar Yakubu, ya nemi tattaunawa da shi a kan abubuwan da yabon ya ƙunsa a fage na ilimin musamman ganin yadda a ke tafiyar da tsarin kara-zube a…
Read More
Kannywood: Mafari da makoma

Kannywood: Mafari da makoma

Daga AL'MUSTAPHA ADAM MUHAMMAD Wasan kwaikwayo wani al’amari ne mai daɗɗaɗen tarihi a rayuwar ɗan Adam. Ya samo asali ne shekaru aru-aru da suka wuce a daulolin Girkawa da Rumawa tun ɗaruruwan shekarun da suka shuɗe. Tun a wancan lakacin akan yi amfani da wasan kwaikwayo ne don nishaɗantarwa da zaburar da rundunonin sojojinsu da suka yi nasara a yaƙe-yaƙen su a wancan zamani. Haka zalika akan yi wasannin kwaikwayo don faranta wa masu mulki rai su samu cikakken muwalati da nishaɗi. A irin waɗannan lokuta ne makaɗa, masu iya bada hikayoyi, maraya da mutanen fadla masu barkwanci kan sheƙe…
Read More
Fim ɗin Gari Guda zai buɗe sabon shafin kallo a sinima – Darakta Sufyanu Kabo

Fim ɗin Gari Guda zai buɗe sabon shafin kallo a sinima – Darakta Sufyanu Kabo

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano A yanzu dai duk wani shiri ya kammala na fitowar sabon fim ɗin 'Gari Guda', wanda Kamfanin 'Islamic Film Empire' suka shirya, kuma Sufyanu Lawal Kabo ya bayar da Umarni.Ganin yadda fim ɗin ya bambanta da sauran fina-finan da aka saba shirya wa a masana'antar fina-finai ta kannywwod ne ya sa muka nemi jin ta bakin Daraktan fim ɗin Sufyanu Lawal Kabo don jin irin abubuwan da fim ɗin ya ƙunsa. Don haka sai ku biyo mu ku ji yadda tattaunawar ta kasance: Akwai wani sabon fim da ka yi aikin sa, kuma ka ke…
Read More
An shirya gudanar da babban taron KILAF na bana

An shirya gudanar da babban taron KILAF na bana

Daga BASHIR ISAH Kamfanin Moving Image Limited tare da haɗin gwiwar Tsangayar Nazarin Sadarwa ta Jami'ar Bayero, Kano, sun shirya gudanar da babban taronsu na shekara-shekara na tallata harsunan gida na Kano a kasuwar fina-finai ta Afirka, wato Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival ko kuma KILAF a taƙaice. Taron KILAF na 2021 zai gudana ne a ranakun Litinin 22 da Talata 23 ga watan Nuwamban da ake ciki. Wannan shi ne karo na huɗu da ake shirya taron. Sanarwar manema labarai da ta sami sa hannun mu'assasin KILAF, Abdulkareem Mohammed da shugaban tsangayar nazarin sadarwa na…
Read More