05
Dec
Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Mahmoud Isma’il Ibrahim, wanda aka fi sani da Mahmoud Nagudu, fitaccen mawaƙi ne a fagen yabon Manzon Allah (SAW) tun yana ƙaramin yaro, sai dai ya yi fice ne a fagen waƙoƙin fim a shekarun baya. Amma dai yanzu ya daɗe ba a jin ɗuriyarsa a fagen waƙoƙin Nanaye, sai na yabon Manzon Allah kaɗai. Kasancewarsa mai ilimi a fagen yabon, ya sa Wakilin Manhaja a Kano, Mukhtar Yakubu, ya nemi tattaunawa da shi a kan abubuwan da yabon ya ƙunsa a fage na ilimin musamman ganin yadda a ke tafiyar da tsarin kara-zube a…
