Nishadi

An shirya gudanar da babban taron KILAF na bana

An shirya gudanar da babban taron KILAF na bana

Daga BASHIR ISAH Kamfanin Moving Image Limited tare da haɗin gwiwar Tsangayar Nazarin Sadarwa ta Jami'ar Bayero, Kano, sun shirya gudanar da babban taronsu na shekara-shekara na tallata harsunan gida na Kano a kasuwar fina-finai ta Afirka, wato Kano Indigenous Languages of Africa Film Market and Festival ko kuma KILAF a taƙaice. Taron KILAF na 2021 zai gudana ne a ranakun Litinin 22 da Talata 23 ga watan Nuwamban da ake ciki. Wannan shi ne karo na huɗu da ake shirya taron. Sanarwar manema labarai da ta sami sa hannun mu'assasin KILAF, Abdulkareem Mohammed da shugaban tsangayar nazarin sadarwa na…
Read More
Yadda aka fara haska fim ɗin Fanan a Sinima

Yadda aka fara haska fim ɗin Fanan a Sinima

Daga MUKHTAR YAKUBU, a Kano A yanzu haka dai an fara haska shahararren fim ɗin  'FANAN' a Cinimar Platinium da ke kan titin Zaria, kusa da Masallacin Umar Bin Khaddab da ke cikin garin Kano. An daɗe dai ana ta sanar da bayyanar fim ɗin wanda aka shirya shi tare da kammala aikin sa kusan shekaru biyu da suka gabata. Kuma an ƙiyasta fim ɗin ya laƙume miliyoyin Naira. Fim ɗin dai na tsohuwar jaruma Mansurah Isah ne, wanda aka shirya shi a ƙarkashin kamfanin 'Today's Life' tare da haɗin gwiwar wasu kamfanoni domin samun ingantuwar aikin. A lokacin da…
Read More
Yadda zaɓen ƙungiyar MOPPAN reshen Abuja ya gudana

Yadda zaɓen ƙungiyar MOPPAN reshen Abuja ya gudana

Daga IBRAHIM HAMISU a Abuja Haɗaɗɗiyar ƙungiyar masu shirya Fina-finai ta Nijeriya, Motion Picture Practitioners Association of Nigeria (MOPPAN) reshen Abuja ta gudanar da zaɓen shugabanni a ranar Asabar 30 ga Oktoba, 2021, a harabar ɗakin taro na kamfanin Kufaina Films da ke Abuja. Malaman zaɓen dai sun fara tantance 'yan takara da misalin ƙarfe 10:30 na safe. An kuma kammala tantance su ne zuwa ƙarfe 11:30, inda aka tantance 'yan takara guda 10. An fara kaɗa ƙuri'a ne da misalin 11:30 na safiyar a ƙarƙashin kulawar Babban Ma'ajin ƙungiyar MOPPAN ta ƙasa, Alhaji Bala Mu'azu Kufaina. Bayan ƙirga ƙuri'un…
Read More
Yadda na ci kyautar da wani jarumi a Kannywood bai ci ba – Gidan Dabino

Yadda na ci kyautar da wani jarumi a Kannywood bai ci ba – Gidan Dabino

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano A makon jiya mun yi muku gabatarwa kan wannan tattaunawa da Manhaja ta yi da fitaccen jarumi kuma marubuci, Malam Ado Ahmad Gidan Dabino (MON), inda mu ka yi muku alqawarin cewa, a wannan makon za mu kawo muku cikakkiyar tattaunawar. Shi dai Gidan Dabino ba baƙo ba ne a masana'antar Kannywood, domin su ne suka yanke mata cibiya, ya fara da dirama ne tun a shekarar 1984, wato shekaru 37 da suka gabata, a zantawarsa da wakilin Manhaja a Kano Ibrahim Hamisu, za ku ji yadda Ado Ahmad Gidan Dabino ya lashe kyautar jarumin…
Read More
Me ya sa Ado Gidan Dabino ya ke mamaye kyautar jarumin jarumai?

Me ya sa Ado Gidan Dabino ya ke mamaye kyautar jarumin jarumai?

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Ado Ahmad Gidan Dabino (MON) ba baƙo ba ne a masana'antar Kannywood da kasuwar adabi, domin su ne suka yanke wa Kannywood cibiya. Ya fara da dirama (wasan daɓe) ne tun a shekarar 1984, wato shekaru 37 da suka gabata. A zantawarsa da Wakilin Manhaja a Kano, Ibrahim Hamisu, za ku ji yadda Ado Ahmad Gidan Dabino ya lashe kyautar jarumin jarumai har sau uku a shekara ɗaya kuma da fim ɗaya a fim ɗin ɗaya, wato Juyin Sarauta’. Ko a watan Nuwambar da ya gabata (2020), Malam Gidan Dabino (MON) ya samu nasarar lashe…
Read More
An yaye sabbin ɗaliban fim a Kano

An yaye sabbin ɗaliban fim a Kano

Daga MUKHTAR YAKUBU, a Kano Bayan cigaban da makarantar koyar da harshen Turanci ta Jammaje Academy ta samu daga koyar da harshen Turanci zalla zuwa wasu kwasa-kwasai na koyar da sana'o'i da dabarun yin kasuwanci, a yanzu kuma makarantar ta fannin koyar da dabarun fitowa a fim, wato 'acting', ta kai ga matakin yaye ɗaliban da suka shiga cikin kwas ɗin a zango na farko. A ranar Lahadi, 10 ga Oktoba, 2021, aka gudanar da taron yaye ɗaliban guda 40 tare da ba wa wasu daga cikinsu shaidar kammala karatun nasu da suka yi na tsawon watanni. Taron, wanda aka…
Read More
Dalilin da ya sa mawaƙan bege mata suka zama taron tsintsiya – Fantimoti

Dalilin da ya sa mawaƙan bege mata suka zama taron tsintsiya – Fantimoti

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano. A wannan lokacin masu yabon Annabi, wato sha'irai, musamman mata su na samun ƙalubale a wajen jama'a wajen yadda su ke gudanar da harkokin waƙar tasu ta yadda a ke yi musu kallon suna shigo da wasu abubuwa da dama waɗanda suka sava wa yabon Manzon Allah (SAW), kamar abin da ya shafi yawon majalisi, haɗuwarsu da maza da sauran abubuwan makamantansu. Wannan ya sa Manhaja ta nemi jin ta bakin ɗaya daga cikin fitattu a cikin waƙoƙin Yabon Annabi, wato Hajiya Maryam Saleh, wacce aka fi sani da Maryam Fantimoti, domin ta yi mana…
Read More
Aikin MC ilimi ne mai zaman kansa a aikin jarida – MC Bahaushe

Aikin MC ilimi ne mai zaman kansa a aikin jarida – MC Bahaushe

Daga UMAR GARBA, a Katsina Kabir Sa'idu Bahaushe matashi ne da ya yi fice a fannoni daban daban, kama daga mai shiryawa da gabatar da shirye shirye a gidan radiyo, da kuma yin sharhi da rubuce-rubuce a jaridu da mujallu. Haka nan ma Kabir Sa'idu Bahaushe ya yi fice a harkar gabatar da tarurruka a gidan biki ko taron ƙungiyoyi ko kuma taron marubuta ko na mawaƙa gami da taron siyasa. Manhaja ta tattauna da Bahaushe a kan batutuwan da su ka shafi aikin shi na gabatar da tarurruka watau MC da alaƙarsa da marubuta da ƙungiyoyi har ma da…
Read More
Yadda batun kama ɗan Shah Rukh Khan bisa zargin tu’ammalli da ƙwayoyi ya zama

Yadda batun kama ɗan Shah Rukh Khan bisa zargin tu’ammalli da ƙwayoyi ya zama

Daga AISHA ASAS A ranar 3 ga watan Oktobar wanann shekara ofishin kula da miyagun ƙwayoyi ta Ƙasar Indiya, wato NCB, ta damƙe ɗan shahararren ɗan wasan kwaikwayon Indiya Shah Rukh Khan da laifin tu’amalli da miyagun ƙwayoyi. Ofishin ya damqe shi ne a bakin taikon Mumbai, inda su ke gudanar da sharholiyarsu a cikin wani jirgin ruwa. Rahoton ya bayyana cewa, Ɗan na Shah Rukh ba shi kaɗai ne hukumar ta samu damar damqa ba, domin dai bikin na jin daɗi ne suke gabatarwa wanda ya ɗauki dubban matasa ‘yan'uwansa. Duk da cewa an tabbatar da cewa gayyatar Aryan…
Read More
Ganawar Kannywood da Hukumar NDLEA faɗuwa ce ta zo daidai da zama – Dr. Sarari

Ganawar Kannywood da Hukumar NDLEA faɗuwa ce ta zo daidai da zama – Dr. Sarari

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Masana'antar fina-finai ta Kannywood a ƙarƙashin ƙungiyar ƙwararru ta masu shirya fim ta ƙasa MOPPAN, sun tsara wani haɗin gwiwa da Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi domin magance matsalar da ta ke yaɗuwa a tsakanin matasa a ƙasar nan. Shugaban ƙungiyar ta MOPPAN Dakta Ahmad Sarari ne ya bayyana hakan ga wakilin mu bayan wata ganawa da 'yan fim ɗin su ka yi da Shugaban Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyin na ƙasa, Janar Muhammad Buba mairitaya. Dakta Ahmad Sarari ya bayyana mana cewar, "zaman da muka yi da shugaban wannan Hukumar,…
Read More