Labarai

Neja: An yi garkuwa da mutum 30 a ƙauyen Kutunku

Neja: An yi garkuwa da mutum 30 a ƙauyen Kutunku

Daga UMAR M. GOMBE 'Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 30 a Litinin da ta gabata a garin Kutunku da ke yankin ƙaramar hukumar Wushishi a jihar Neja. Wannan na zuwa ne bayan da Gwamnan Jihar Neja, Abubakar Sani Bello, ya fito ya bayyana cewa daga yanzu babu wata tattaunawa da 'yan bindigar da ke yin garkuwa da mutane. Bayanai sun tabbatar cewa 'yan bindigar sun shiga ƙauyen Kutunku ne ɗauke da makamai kuma a qafa, inda suka yi wa ƙauyen zobe. Wata majiya ta ce, 'yan bindigar sun ɓoye baburansu a daji ne sannan suka ƙarasa ƙauyen a…
Read More
Etsu Nupe ya yi jajantawa kan rasuwar Sarkin Kagara

Etsu Nupe ya yi jajantawa kan rasuwar Sarkin Kagara

Daga UMAR M. GOMBE Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya na Jihar Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, ya bayyana rasuwar marigayi Sarkin Kagara, Alhaji Salihu Tanko a matsayin babban rashi ga iyalan mamacin da masarautar Kagara da jihar Neja da ma ƙasa baki ɗaya. Etsu Nupe ya faɗi haka ne ga manema labarai a garin Minna a Larabar da ta gabata a lokacin da yake jajantawa game da rasuwar basaraken. Tare da cewa rasuwar marigayin ta haifar da wagegen giɓin da iya cike shi sai an yi da gaske. Da wannan ne sarkin ya ce, "A madadin Majalisar Sarakunan Gargajiya,…
Read More
Gwamna Sule ya nuna takaicinsa kan jinkirin kammala cibiyar lantarki

Gwamna Sule ya nuna takaicinsa kan jinkirin kammala cibiyar lantarki

Daga BASHIR ISAH Gwamnan Jihar Nasarawa, Engineer Abdullahi Sule, ya nuna takaicinsa kan jinkirin da aka samu wajen kammala aikin cibiyar lantarki mai ƙarfin 330 KV a yankin Akurba. Gwamnan ya nuna damuwarsa ne bayan da ya kai ziyarar gani da ido domin duba yadda aikin kafa cibiyar ke gudana. Sule ya nuna rashin jin daɗinsa ga 'yan kwangilar da aikin gina cibiyar ke hannunsu, tare da bada tabbacin cewa gwamatinsa za ta tallafa don tabbatar da aikin ya kai ga gaci nan bada daɗewa ba. Bayanai sun nuna an samu jinkiri wajen kammala aikin ne sakamakon tsaiko da aka…
Read More
Gudun hijira: Mutum milyan 2.6 suka rasa matsuguni a faɗin Nijeriya – cewar Hukuma

Gudun hijira: Mutum milyan 2.6 suka rasa matsuguni a faɗin Nijeriya – cewar Hukuma

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Kula da 'Yan Gudun Hijira ta Ƙasa ta bayyana cewa a halin yanzu kimanin mutum milyan 2.6 ne suka rasa matsugunansu a faɗin ƙasa. Kwamishinan hukumar, Bashir Mohammed ne ya sanar da hakan a Litinin da ta gabata yayin ƙaddamar da shirin raba tallafin abinci ga mutum 7,500 waɗanda ibtila'i ya shafa a fadar gwamnatin jihar Kano. Garba ya ce 'yan gudun hijirar da ake da su a Kano mutane ne waɗanda matsalar tsaro da ambaliyar ruwa suka shafa daga jihohin Kudancin ƙasa. Ya ci gaba da cewa, Gwamnatin Tarayya ta kammala shirinta na sake tsugunar…
Read More
NDLEA ta kama bindigogi 27 a Neja

NDLEA ta kama bindigogi 27 a Neja

Daga AISHA ASAS Jami'an Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) a jihar Neja, sun kama wasu mutum biyu ɗauke da bindigogi 27 yayin da suke bakin aiki na bincike abubuwan hawa a yankin Kontagora. Waɗanda ake zargin, Danjuma Auta ɗan shekara 35, da Daniel Danrangi mai shekara 25, dukkansu 'yan asalin Dirin Daji ne a yankin Ƙaramar Hukumar Sakaba, jihar Kebbi, sun faɗa a hannun jami'an ne a hanyar Kontagora zuwa Zuru a Litinin da ta gabata da daddare. A cewar Kwamandan Hukumar na jihar Neja, Mr. Aloye Isaac Oludare, an kama su biyun ɗauke da bindigogi AK 47…
Read More
Buhari ya hana jiragen sama shawagi a Zamfara

Buhari ya hana jiragen sama shawagi a Zamfara

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana dokar hana jiragen sama shawagi a Zamfara tare da haramta duka ayyukan haƙar ma'dinai a jihar. Mai bai wa Buhari shawara kan harkokin tsaro, Major General Babagana Monguno (mai murabus) ne ya bayyana haka a ranar Talata a Abuja. Inda ya ce an ɗauki matakin haka ne domin kawar da matsalolin tsaron da ake fuskanta a jihar. Monguno ya bayyana wa manema labarai haka ne jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Tsaro ta Ƙasa wanda ya gudana a Fadar Shugaban Ƙasa ƙarƙashin jagorancin Shugaba Buhari. Wannan mataki na haramta wa jiragen…
Read More
Sarkin Kagara ya rasu

Sarkin Kagara ya rasu

Daga BASHIR ISAH Allah Ya yi wa Sarkin Kagara, Alhaji Salihu Tanko, rasuwa. Tuni dai Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya yi jajantawa ga Etsu Nupe kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Neja, Alhaji Yahaya Abubakar, iyalai da ma ɗaukacin al'ummar Masarautar Kagara dangane da rasuwar. Bello, ya yi addu'ar Allah Ya jiƙan marigayin da rahma, Ya sanya Aljanna makomarsa, kana ya bai wa iyalansa haƙuri da juriyar rashin. Marigayin ya rasu ne a wannan Talatar, a garin Kagara, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Rafi. An haife shi ne a ran 5 ga Afrilun 1930 a Tegina. Ya rasu ya bar 'ya'ya, mata da…
Read More
Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Daga WAKILINMU An bada sanarwar cewa Nijetiya ta samu ƙarin wasu mutum 240 da suka kamu da cutar korona a 'yan sa'o'in da suka gabata. Cibiyar Yaƙi da Yaɗuwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ce ta bada sanarwar haka da daddare a Lahadin da ta gabata, ta shafinta na twita. Ƙarin da NCDC ta ce an samu ya shafi wasu jihohi ne su 13 kamar haka: Anambra 85, Lagos 82, Osun 17, Ogun 10, Kwara 9, FCT 8, Kano 7, Abia 6, Ekiti5, Borno 4, Edo 2, Bayelsa 2, Kaduna 2 da kuma Rivers 1. Cibiyar ta ce katafariyar cibiyar bada…
Read More
Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Daga AISHA ASAS Ministan Abuja Malam Muhammad Musa Bello, ya ƙaddamar da shirin yaƙi da karya dokokin hanya a birnin Abuja a matsayin wani mataki na tabbatar da jama'a na kiyaye dokokin hanya yadda ya kamata a cikin birnin. Ƙaddamar da shirin ya auku ne a ƙarshen makon da ya gabata a Abuja. A lokacin da yake jawabi a wajen taron ƙaddamarwar, Bello ya tunatar da mazauna Abuja cewa dukkanin ƙa'idoji da alamomin da aka sanya a hanyoyi, an yi hakan ne da nufin kare rayukan masu amfani da hanyoyin da kuma hana cunkoso. Yana mai cewa, duba da yadda…
Read More