16
Mar
Daga AISHA ASAS Rundunar 'yan sanda a jihar Anambra, ta ce ta gano wani gida da ake yi zargin ana safarar jarirai a cikinsa a Nnewi cikin ƙaramar Nnewi ta Arewa a jihar. Jami'in Hulɗa da Jama'a na Rundunar, CSP Haruna Muhammed ne ya bada sanarwar haka, yana mai cewa wadda ake zargin ita ce mai masana'antar jariran, Ms Gladys Nworie Ikegwuonu ta tsere sannan an kuɓutar da 'yan mata masu juna-biyu su huɗu. Jami'in ya ce sun yi nasarar kama wasu mutum biyu da ake zargin suna da alaƙa da harƙallar. Ya ci gaba da cewa sun gano masana'antar…
