Labarai

Matawalle ya sha rantsuwa kan ba shi da hannu a matsalar tsaron Zamfara

Matawalle ya sha rantsuwa kan ba shi da hannu a matsalar tsaron Zamfara

Daga WAKILINMU Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle, ya yi rantsuwa da Ƙur'ani kan cewa ba shi da wata alaka da 'yan bindigar da ke addabar jiharsa. Gwamnan ya ƙalubalanci mazauna jihar, da su ma su kwatanta shan ranstuwa kamar yadda ya yi domin tabbatar da cewa ba su da hannu cikin matsalar tsaro da ta addabi jihar. Gwamnan ya yi hakan ne a ranar Lahadi a garin Gusau, babban birnin jihar yayin karɓar lambar yabo da Cibiyar Karatun Ƙur'ani ta Nijeriya ta ba shi a matsayin Khadimul Ƙur'an. Ya ce kamar yadda ya sha faɗa lamarin rashin tsaron nan ba gwamnatin…
Read More
Ogun: ‘Yan bindiga sun sace Sarkin Ijebu-Igbo

Ogun: ‘Yan bindiga sun sace Sarkin Ijebu-Igbo

Daga WAKILINMU Rahotanni daga yankin Ijebu-Igbo a jihar Ogun sun nuna wasu 'yan bindiga sun sace sarkin yankin, Oba Alade Meta, a ranar Asabar. Wata majiya ta ce a wannan rana, sarkin ya bar fadarsa da misalin ƙarfe 11 da wata motarsa 'jeep' zuwa unguwa. A kan hanyarsa ta komawa gida misalin ƙarfe 3 na rana, 'yan bindiga suka tare shi a hanya, suka fidda shi a motarsa tare da yin awon gaba da shi sanna suka bar motar tasa a nan. Tun daga wannan lokaci ya zuwa haɗa wannan labari, babu wanda ya san inda sarkin yake. Haka ma…
Read More
AMAC: Candido ya ɗauki nauyin karatun yara 29

AMAC: Candido ya ɗauki nauyin karatun yara 29

Daga AISHA ASAS Shugaban Hukumar Abuja Municipal (AMAC) Abdullahi Adamu Candido, ya yi alƙawarin bada tallafin karatu na musamman ga ɗaliban firamare su 29 da suka shiga gasar baje fasahar rubutun insha'i na bikin Ranar Farin Ciki ta Duniya na 2021 da kuma ƙaddamar da littafi wanda ya gudana a sakatariyar Hukumar Makarantun Firamare (LEA) da ke Wuse, Abuja. Shugaban ya sanar da haka ne a wajen wani taron bita ga manema labarai wanda ya gudana a Keffi, Jihar Nasarawa. Candido ya ce tuni an ware kuɗi naira milyan N26 domin cika wannan alƙawari da ya ɗauka na bada tallafin…
Read More

Yadda ’yan bindiga suka kashe Sojoji 4 da ƙona motar su a Zamfara

Matawalle Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne da ba su tuba ba sun afkawa ƙauyen Kabasa da ke Gundumar Magami a Ƙaramar Hukumar Gusau ta Jihar Zamfara, sun kashe mazauna ƙauyuka biyar da kuma sojoji uku da suka haɗa da Manjo wanda Kwamanda ne dake wakiltar Yankunan Magami, Dankurmi da Dansadau tare da ƙone motar sojojin. Wani mazaunin yankin mai suna Malam Lawali Magami a wata hira ta wayar tarho tare da Manhaja a Gusau ya ce, ’yan ta'addan sun yi wa ƙauyen qawanya da misalin ƙarfe 4:30 na yammacin ranar Talata, suka fara…
Read More

‘Yan bindiga sun yi niyyar halaka ni ne – Sarkin Birnin Gwari

Alh. Zubairu Jibril Daga MUHAMMAD AHMAD a Kaduna A sakamakon harin da wasu ’yan bindiga suka kai wa tawagar  Sarkin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Jibril Mai Gwari II, sarkin ya ce an yi niyyar halaka shi ne, amma sai aka samu kuskure ba ya cikin motar tasa. Sarkin ya bayyana haka ne jim kaɗan bayan harin da aka kai wa tawagar tasa a jiya Alhamis, a kan hanyar su ta zuwa Kaduna domin yin taro da gwamnan jihar, yana mai cewa akwai haɗin bakin wasu daga cikin al’ummar Birnin Gwari. Alhaji Zubairu Jibril Mai Gwari II ya ce “Akwai kyakkyawan…
Read More

Hare-haren Boko haram ya raba mutane sama da miliyan biyu da muhallin su – Rahoto

Daga MUAHAMMAD AL-AMEEN A wani rahoto da Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, ya bayyana cewa hare-haren mayaƙan Boko Haram sun raba mutane sama da miliyan biyu da muhallin su a Arewa-maso-Gabas, ya kuma haifar da lalacewar kayan more rayuwa da wahalar samun kula da lafiya ga mutanen da suka tsere daga gidajen su. Rahotan ya ƙara da cewa ƙungiyoyin jinƙai da yawa sun damu da halin da mutanen yankin ke ciki, inda waɗan su suka yi ƙoƙarin janyo hankali kan tavarɓarewar al’amura ganin yadda annobar korona ta ɗauke hankalin duniya a halin da ake ciki. Masu aikin jinƙai sun bayyana…
Read More
Gwamnatin Tarayya da Nasarawa za su yi aiki tare wajen kare yankunan haƙo ma’adinai

Gwamnatin Tarayya da Nasarawa za su yi aiki tare wajen kare yankunan haƙo ma’adinai

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Nasarawa sun shirya yin aiki tare domin kare yankuna masu arzikin zinari a jihar Nasarawa da kuma kare iyakokin Abuja da Nasarawa. Ministan Bunƙasa Ma'adinai, Architect Olamilekan Adegbite, shi ne ya bayyana hakan sa'ilin da ya karɓi baƙuncin Gwamna Abdullahi Sule a ofishinsa da ke Abuja a Talatar da ta gabata. A cewar Ministan Gwamnatin Tarayya ta kashe maƙudan kuɗaɗe har biliyan N15 kan harkokin ma'adinai a sassan ƙasa ƙarƙashin shirinta na aikin binciko inda arzikin zinari yake a Nijeriya inda ta gano hakan tsakanin Jihar Nasarawa da Abuja.…
Read More
Legas kaɗai na da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi milyan 4, cewar Marwa

Legas kaɗai na da masu ta’ammali da miyagun ƙwayoyi milyan 4, cewar Marwa

Daga WAKILINMU Shugaban Hukumar Yaƙi da sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA) Janar Muhammadu Buba Marwa, ya ce aƙalla mutum miliyan 4 da rabi ke mu’amala da miyagun ƙwayoyi a birnin Legas, abin da ke nuna ƙaruwar matsalar da ta addabi ƙasa baki ɗaya. Yayin da ya ke ziyarar gani da ido tun bayan naɗa shi a matsayin shugaban hukumar, Marwa ya bayyana birnin Legad a matsayin jihar da ake samun kashi 30 na masu amfani da miyagun ƙwayoyin. Ya ce daga cikin mutane miliyan 15 da aka yi ƙiyasin suna mu‘amala da miyagun ƙwayoyin wajen sha da…
Read More
Buhari ya jinjina wa Uzodinma kan ayyukan cigaba

Buhari ya jinjina wa Uzodinma kan ayyukan cigaba

Daga FATUHU MUSTAPHA Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya yi kira ga gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, da ya ɗore da ayyukan cigaba da gwamnatinsa ke yi don kyautata rayuwar talakawan jiharsa. Talatar da ta gabata Shugaba Buhari ya yi wannan kira, tare da yaba ƙoƙarin Gwamna Uzodinma na kammala tarin ayyukan cigaba a tsakanin shekara guda. Buhari ya yi kalamansa ne ta bidiyo yayin ƙaddamar da wasu hanyoyi guda biyu a garin Owerri, babban birnin jihar waɗanda aka kammala aikinsu cikin shekara guda da gwamnan ya yi kan mulki. Buhari ya jinjina wa gwaman dangane da kammala hanyar Assumpta Cathedral…
Read More