Labarai

Gwamnan Zamfara ya jinjina wa Shugaban APC na Ƙasa kan jagorancinsa yayin cika shekara 58

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya miƙa saƙonsa na taya murna ga Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda bisa zagayowar ranar haihuwarsa ta cikar sa shekaru 58 a duniya, yana mai yaba wa jagoranci da gudunmawarsa ga ci-gaban jam'iyyar. A ranar Asabar, 8 ga Agusta, 2026 ne farfesan ya cika shekara 58 a duniya, inda gwamnan Zamfarar ya bayyana shi a matsayin muhimmin jigo acikin APC kuma mai taka muhimmiyar rawa ga ci-gaban harkokin siyasa a Nijeriya. A saƙonsa na taya murna ga Yilwatda, Dauda Lawal ya kuma ce a matsayinsa na…
Read More

Sojoji sun kama mai kai wa ‘yan ta’adda kayan abinci da tsabar miliyan N5.3, sun daƙile tashin Bom a Zamfara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun haɗaka na Atisayen FANSAN YAMMA a Arewa maso yammacin Nijeriya, sun yi nasarar kama wani mutum da ake zargin abokin hulɗar 'yan ta'adda ne mai samar musu da wasu ababen amfanin yau da kullum. Haka kuma, sun samu tsabar kuɗi a hannunsa da adadinsu ya kai kimanin Naira miliyan 5.302, sannan kuma suka katse wani abin fashewa (IED) da aka dasa a wata babbar hanya a Jihar Zamfara. Jami'in yaɗa labarai na rundunar FANSAR YAMMA, Laftanal Kanal Aliyu Ɗanja ne ya bayyana haka a wata takarda a ranar Juma'a, inda ya ce an…
Read More

Majalisar Ƙasashen Musulmi za ta ƙaddamar da cibiyar kula da ciwon zuciya a Kaduna

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ƙoƙarin Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna na inganta harkar lafiya a Kaduna ya samu ƙarin ƙarfi, bayan Majalisar Kasashen Musulmi ta Muslim World League (MWL) ta kammala gina wata katafariyar cibiyar kula da cututtukan zuciya ta zamani a yankin Tudun Wadada ke Ƙaramar Hukumar Kaduna ta Kudu. Za a ƙaddamar da cibiyar ne a ranar Talata, 11 ga Agusta, 2026, a yayin wani biki da Sakatare Janar na majalisar ta Muslim World League, Sheikh Mohammed Bin Abdulkarim Al-Issa zai jagoranta. Rahotanni sun bayyana cewa, cibiyar za ta samar da gwaje-gwaje, magani da kulawa…
Read More

Da Ɗumi-Ɗumi: Mahaifin Messi ya rasu

Mahaifin shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Argentina da Inter Miami, Lionel Messi, Jorge Messi, ya rasu bayan shafe shekaru 68 a duniya. A cewar rahotannin kafafen yaɗa labarai daga ƙasar Argentina, Jorge ya rasu ne a ranar Juma'a, a wani asibiti da ke mahaifarsa ta Rosario a Argentina bayan fama da wani rashin lafiya na tsawon lokaci. Jorge ya taka muhimmiyar rawa wajen bunƙasa rayuwar ɗansa Messi, musamman lokacin da yake ƙarami. Ya taimaka wajen ganin an samu maganin da Messi ke buƙata domin matsalar girma, sannan ya taimaka wajen kai shi Barcelona yana da shekara 13. Ya kuma…
Read More

Henna Ball da People’s Award na 2026: Gidan talabijin na Tozali zai yi taron dawo da karsashin matan da aka yi garkuwa da su

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gidan talabijin na Tozali na farin cikin sanar da al'umma cewa zai gudanar da taron bayar da lambar yabo na Henna Ball da Tozali People na 2026. Za a gudanar da taron ne a ranar 31 ga watan Oktoba, 2026 a ɗakin taro na Los Angeles, inda za a martaba ƙoƙari, al'ada, jajircewa da tasirin ayyukan jin-ƙai acikin al'umma. Haka kuma, an yi wa taron laƙabi da Empowering Survivors. Restoring Hope.", wato mai manufar inganta rayuwar matan da suka shaƙi iskar 'yanci bayan garkuwa da su da kuma dawo da karsashinsu acikin al'umma. Sannan,…
Read More

Mutane 13 sun rasu, ana riƙe da yara 12 har yanzu – Ba’asin ‘yan Kwara da suka shaƙi iskar ‘yanci

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wasu daga cikin mutanen ƙauyukan Woro da Nuku na Ƙaramar Hukumar Kaiama ta Jihar Kwara da suka shaƙi iskar 'yanci bayan harin ranar 3 ga Fabrairu, sun bayyana cewa mutane 13 sun rasu a lokacin da suke hannun 'yan bindiga, yayin da kuma har yanzu akwai yara guda 12 da ke komar 'yan ta'adda. Sun bayyana haka ne ga manema labarai bayan Gwamnatin Jihar Kwara ta karɓi baƙuncinsu a hukumance, inda suka bayyana yadda suka tsinci kansu a daji da rayuwar cin abinci sau guda a yini na tsawon kusan watanni shida. Mutanen na…
Read More

Mourinho ya sanya dokoki huɗu don dawo da ɗa’a a Real Madrid

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sabon kociyan Real Madrid ta Ƙasar Sifaniya, Jose Mourinho, ya samar da wasu dokoki guda huɗu da nufin dawo da ɗa'a, ƙwarewa da haɗin kai acikin 'yan wasan ƙungiyar. A cewar jaridar Sifaniya AS, ɗan ƙasar Portugal ɗin mai shekaru 63 ya gano wasu ɗabi'u da yake ganin akwai buƙatar a sauya su tun bayan dawowarsa Bernabeu. Kocin ya samar da sababbin tsarin gudanarwa akan cin abinci, tsare aiki, gyaran tsarin kula da lamuran raunin 'yan wasa sa kuma dunƙule tawagar 'yan wasa. A sabon wa'adin nasa, 'yan wasan Real Madrid za su kasance…
Read More

Jagoran Tijjaniya ya nemi ƙarfafa alaƙar Nijeriya da Aljeriya bayan ganawa da Tinubu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Babban Kalifan Ɗarikar Tijjaniyya kuma Jagoran Majalisar Ƙolinta, Sheikh Sidi Ali Belarabi Tidjani, ya gana da Shugaba Bola Tinubu a Abuja a matsayin wani bangarena ziyararsa ta zuwa Nijeriya a hukumance. Sheikh Tidjani ya isa Nijeriya ne a ranar Alhamis tare da wata tawaga daga Zawiyar Kalifanci da ke Aïn Madhi a Aljeriya, bayan wata gayyata ta musamman daga jagororin Tijjaniyya a Nijeriya. A yayin haka ne ya yi tsokaci kan daɗaɗɗiyar alaƙar da ke tsakanin Nijeriya da Aljeriya, tare da nuna kwaɗayin ƙarfafa alaƙar ta hanyoyi da dama da suka shafi ci-gaba. Tawagar…
Read More

Matakin EFCC na rufe asusun gwamnatin Osun na bisa doka, inji Falana

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Lauyan kare haƙƙin ɗan-adam kuma Babban Lauyan Nijeriya (SAN), Femi Falana, ya kare matakin Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta'annati EFCC, inda ya ce ta yi aiki ne bisa ikon da doka ta ba ta a lokacin da ta sanya wa asusun gwamnatin Jihar Osun takunkumi. Falana ya bayyana haka ne a wata hira da gidan talabijin na Channels a ranar Juma'a a shirin 'Politics Today', a inda ya ce hukumar ba ta yi wani abu da ya saɓa wa doka ba, kuma Shugaba Bola Tinubu ma yana sane da halascin matakin…
Read More

An karrama gwamnan Zamfara da lambar yabo ta ZIK Pan-African a Ghana

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya samu babbar kyauta ta lambar yabo ta 'ZIK International Peace and Leadership Award' da aka gudanar a ƙasar Ghana bisa la’akari da nasarorin da gwamnatinsa ta samu cikin shekaru uku da suka gabata. An gudanar da bikin bayar da lambar yabon karo na bakwai ne a ranar Juma’a a cibiyar British Council da ke Accra, babban birnin ƙasar. A wata sanarwa da kakakin gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ya ce an yi wa taron take da “Jagoranci, Zaman Lafiya da Haɗin Kan Yankuna: Bunƙasa Ci gaban Afirka…
Read More