Labarai

Ya damfari jagoran ’yan bindiga miliyan N95 da sunan sayo masa makamai a Katsina

Ya damfari jagoran ’yan bindiga miliyan N95 da sunan sayo masa makamai a Katsina

Wani mutum da ake zargin yana safarar makamai ya ɓace ɓat bayan karɓar Naira miliyan 95 daga hannun wani fitaccen jagoran ’yan bindiga a Jihar Katsina, da sunan zai saya masa manyan makamai. Rahotanni sun ce zargin ya fito ne daga ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Musawa/Matazu, Abdullahi Aliyu, wanda aka fi sani da Janar, yayin wata hira da ya yi da NTA Hausa. A cewarsa, mutumin ya karɓi kuɗin ne daga wani shugaban ’yan bindiga da ke aiki a ƙaramar hukumar Matazu, bayan ya yi masa alƙawarin samar masa da manyan makamai. Sai dai bayan karɓar kuɗin, ana…
Read More
PTDF ta buƙaci ’yan jarida su riƙa bayar da sahihan rahotanni kan fannin mai da gas

PTDF ta buƙaci ’yan jarida su riƙa bayar da sahihan rahotanni kan fannin mai da gas

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Asusun Bunƙasa Fasahar Man Fetur (PTDF) ya buƙaci 'yan jarida su riƙa wallafa sahihan rahotanni masu cike da gaskiya kan harkokin mai da iskar gas a Nijeriya, yayin da ya kammala wani shirin horaswa da aka gudanar a Legas domin ƙara wa ƙwararrun kafafen yaɗa labarai ilimi kan yadda ake ba da rahoto a wannan muhimmin fanni. Shirin horaswar ya samu halartar kusan 'yan jarida 50 da masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai, inda aka koya musu dabarun fahimtar fannoni na fasaha da manufofin da suka shafi masana'antar mai da iskar gas, tare da…
Read More
Ku yi amfani da ɗimbin damar kasuwancin Nijeriya – Shettima ga Saudiyya

Ku yi amfani da ɗimbin damar kasuwancin Nijeriya – Shettima ga Saudiyya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mataimakin Shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga masu zuba jari daga ƙasar Saudiyya da su yi amfani da ɗimbin damar kasuwanci da ke Nijeriya, yana mai tabbatar musu cewa Gwamnatin Tarayya ta samar da yanayi mai kyau da zai ba su damar gudanar da harkokinsu cikin kwanciyar hankali. Shettima ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin buɗe baje kolin zuba jari da yawon buɗe ido na Nijeriya da Saudiyya na kwanaki biyu da aka gudanar a Abuja. Kamfanin Al-Yaro International Limited ne ya shirya taron tare da haɗin gwiwar Hukumar ’Yan Nijeriya…
Read More
Dangote ya zuba Dala miliyan 800 don ƙarfafa kamfanin simintinsa na Ogun

Dangote ya zuba Dala miliyan 800 don ƙarfafa kamfanin simintinsa na Ogun

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamfanin Dangote ya rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta Dala miliyan 800 da kamfanin Sinoma International Engineering Company Limited na ƙasar Chana, domin faɗaɗa matatar simintinsa da ke Itori a Jihar Ogun daga ƙarfin samar da tan miliyan shida zuwa tan miliyan 12 a shekara. Ana sa ran wannan shiri zai ƙara ƙarfin Nijeriya wajen fitar da siminti zuwa ƙasashen waje tare da ƙarfafa matsayinta a matsayin ƙasa mafi girma wajen samar da siminti a nahiyar Afirka. Shugaban Rukunin Kamfanonin Dangote, Alhaji Aliko Dangote, da Shugaban Kamfanin Sinoma, Lin Zhong, ne suka sanya hannu kan…
Read More
 Fulani makiyaya sun zargi hukumar OYRLEA da ƙwace dabbobinsu ba bisa ƙa’ida ba a Oyo

 Fulani makiyaya sun zargi hukumar OYRLEA da ƙwace dabbobinsu ba bisa ƙa’ida ba a Oyo

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Fulani Makiyaya da ke ƙaramar Hukumar Ido a Jihar Oyo sun zargi jami'an Hukumar Tabbatar da Bin Doka ta Jihar Oyo (OYRLEA) da karɓar kuɗaɗe ba bisa ƙa'ida ba, nuna wariya da kuma ƙwace dabbobinsu ba tare da hujja ba. Makiyayan sun yi waɗannan zarge-zarge ne a ranar Asabar yayin da suka kai wasu 'yan jarida zagayen wuraren da suka ce jami'an hukumar suka ƙwace musu dabbobi. Shugaban ƙungiyar Miyetti Allah a yankin, Alhaji Ahmed Babangida, ya yi zargin cewa jami'an OYRLEA ne tare da jami'an Amotekun Corps da masu tsaron sa-kai suka gudanar da waɗannan…
Read More
NFHI ta nemi haɗin gwiwa domin ƙarfafa matasa da rage talauci

NFHI ta nemi haɗin gwiwa domin ƙarfafa matasa da rage talauci

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kungiyar Next Frontiers Hub Initiative (NFHI) ta halarci wani babban taron tattaunawa na masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Abuja ranar 4 ga Agustan 2026, inda aka tattauna batutuwan da suka shafi bunƙasa hada-hadar kuɗi, rage talauci, ƙarfafa matasa da kuma ci gaba mai ɗorewa a Nijeriya. Wacce ta kafa ƙungiyar kuma shugabarta, Dakta Fatima Usman Nazir, ce ta wakilci NFHI a taron.  A yayin taron, ta yi mu'amala da sarakunan gargajiya, shugabannin cibiyoyin kuɗi, masu tsara manufofi da sauran fitattun masu ruwa da tsaki. Taron ya samar da wata muhimmiyar dama ta tattaunawa,…
Read More
Kamfanin barasa a Nijeriya ya samu ribar Naira biliyan 164 cikin wata shida

Kamfanin barasa a Nijeriya ya samu ribar Naira biliyan 164 cikin wata shida

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamfanin barasa na Nigerian Breweries ya sanar da samun ƙarin kuɗaɗen shiga da kashi tara cikin ɗari a tsakiyar shekarar 2026, inda ya samu Naira biliyan 804, yayin da ribar aikinsa ta kai Naira biliyan 164, alamar ci gaba da farfaɗowar harkokin kuɗinsa. Sakamakon kuɗaɗen da kamfanin ya fitar na watanni shida da suka ƙare a ranar 30 ga Yuni, 2026, ya nuna cewa kuɗaɗen shigar sun ƙaru daga Naira biliyan 738 da aka samu a daidai wannan lokaci a shekarar 2025. Kamfanin ya kuma samu ƙarin ribar aiki da kashi takwas cikin ɗari, inda ta…
Read More
Gwamnatin Kano ta cafke likitan bogi yana yin magunguna marasa inganci

Gwamnatin Kano ta cafke likitan bogi yana yin magunguna marasa inganci

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Kano ta kama wani mutum da ake zargi likitan bogi ne, bisa zargin raba magungunan da ba su samu amincewar hukumomi ba tare da gudanar da wani shirin ba da magani ga jama'a ba tare da izini ba a yankin Panshekara. An kama wanda ake zargin ne a wani samame na haɗin gwiwa da jami'an Ma'aikatar Lafiya ta Jihar Kano, da Hukumar Kula da Asibitoci Masu Zaman Kansu ta Jihar Kano (PHIMA), da Cibiyar Daƙile da Yaɗuwar Cututtuka ta Jihar Kano (KNCDC) tare da Rundunar 'Yan Sandan Nijeriya, bayan samun bayanan sirri kan ayyukansa.…
Read More
Ku bar ’yan Nijeriya su ji ta bakina – Shugaban hukumar bogi ya nemi majalisa ta zauna da shi a bainar jama’a

Ku bar ’yan Nijeriya su ji ta bakina – Shugaban hukumar bogi ya nemi majalisa ta zauna da shi a bainar jama’a

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mutumin da ake zargi da ƙirƙira tare da jagorantar Hukumar Majalisar Shugaban ƙasa kan Bunƙasa Zuba Jarin ƙasashen Waje (PFIPC) ba ta halastacciyar hanya ba, Mista Adeniyi Adeyemi, ya yi fatali da shirin Kwamitin Wucin Gadi na Majalisar Wakilai na yi masa tambayoyi a wani wuri da ba a bayyana ba, yana mai cewa, ya kamata a saurare shi a bainar jama'a, domin 'yan Nijeriya su ji abin da zai faɗa. Adeyemi, wanda ke tsare a hannun Rundunar 'Yan Sandan Nijeriya, ya bayyana matsayarsa ne ta bakin lauyansa, Ademola Oyedokun, a ranar Laraba. Lauyan ya ce,…
Read More
Tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87 a 2025 — CBN

Tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87 a 2025 — CBN

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa tattalin arzikin cikin gida na ƙasar ya bunƙasa da kashi 3.87 cikin ɗari a shekarar 2025, idan aka kwatanta da kashi 3.38 cikin ɗari da aka samu a shekarar 2024. Hakan na ƙunshe ne cikin Rahoton Shekara na 2025 da bankin ya wallafa, inda ya danganta wannan ci gaba da aiwatar da sauye-sauyen tattalin arziki a muhimman fannoni, tare da sake fasalin tsarin ƙididdigar tattalin arzikin ƙasar domin haɗa sabbin sassan da suka fara taka rawa. Rahoton ya nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki ta ragu zuwa kashi 15.15 cikin…
Read More