09
Aug
Wani mutum da ake zargin yana safarar makamai ya ɓace ɓat bayan karɓar Naira miliyan 95 daga hannun wani fitaccen jagoran ’yan bindiga a Jihar Katsina, da sunan zai saya masa manyan makamai. Rahotanni sun ce zargin ya fito ne daga ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Musawa/Matazu, Abdullahi Aliyu, wanda aka fi sani da Janar, yayin wata hira da ya yi da NTA Hausa. A cewarsa, mutumin ya karɓi kuɗin ne daga wani shugaban ’yan bindiga da ke aiki a ƙaramar hukumar Matazu, bayan ya yi masa alƙawarin samar masa da manyan makamai. Sai dai bayan karɓar kuɗin, ana…
