Labarai

‘Yan bindiga sun kashe jigon APC a Filato

‘Yan bindiga sun kashe jigon APC a Filato

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga a Jihar Filato sun bindige kakin Jam'iyyar APC a jihar, Sylvanus Namang. Lamarin ya faru ne a garin Pankshin da ke yankin Ƙaramar Hukumar Pankshin a jihar. Majiya ta kusa da APC a jihar wadda ta buƙaci a sakaya sunanta, ta tabbatar da afkuwar lamarin. Tare da cewa, marigayin ya cika ne sabili da raunin da ya ji sakamakon harin da aka kai masa. Haka nan, majiyar ta ce APC za ta fitar da bayani a hukumance dangane da badaƙalar da ke tattare da mutuwar Namang. News Point Nigeria ta rawaito cewa, an harbe marigayin…
Read More
‘Yadda ‘yan bindiga suka yi awon gaba da ‘yan mata tara a Zamfara

‘Yadda ‘yan bindiga suka yi awon gaba da ‘yan mata tara a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu gungun 'yan bindiga sun afka wa Unguwar Mareri dake cikin Gusau, babban Birnin Jihar Zamfara a daren ran Asabar inda suka yi awon gaba da 'yan mata tara tare da wani maƙwabcinsu . Rahotanni sun nuna cewar 'yan bindigar da ɗauke da muggan makamai sun yi dirar mikiya a Unguwar sunata harbe-harbe kafin su samu nasarar sace 'yan matan. Hakazalika, wakilinmu ya tattaro cewar 'yan matan da lamarin ya shafa 'yan asalin garin Anka ne cikin Ƙaramar Hukumar Anka a jihar ta Zamfara. Waɗanda abun ya rutsa da su sun haɗa da: Sanaratu Marafa,…
Read More
Za a kafa Babban Bankin Afirka a Nijeriya

Za a kafa Babban Bankin Afirka a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana cewa, a shirye Nijeriya take ta karɓi Babban Bankin Afirka bisa la'akari da ƙudirin birnin tarayya, Abuja. Tinubu ya yi wannan furuci ne sa'ilin da yake jawabi a wajen taron Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) da ke gudana a Addis Ababa, babban birnin ƙasar Habasha. Ya ƙara da cewa, gwamnatinsa za ta tattauna da dukkan waɗanda suka dace domin tabbatar da bankin ya fara aiki ya zuwa 2028 kamar yadda aka shirya. Shugaba Tinubu ya faɗa wa taron cewa, iya magance ƙalibalan Afirka na tattare ne da irin matsayar da shugabannin nahiyar…
Read More
Tambuwal ya bayyana a gaban Kwamitin Bincike

Tambuwal ya bayyana a gaban Kwamitin Bincike

Daga BASHIR ISAH A ranar Asabar tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Tambuwal, ya bayyana a gaban Kwamitin Bincike mai bincike kan wasu ayyuka da gwamnatisa ta aiwatar a zamanin mulkinsa. Gwamnan Jihar, Ahmed Sokoto ne ya kafa kwamitin domin bincike kan yadda harkokin gwamnatin da ya gada suka gudana. Tambuwal ya isa gaban kwamitin ne tare da wasu muƙarrabansa, kuma rashin ba da shaidarsa ya sa kwamitin ya buƙace shi da ya sake dawowa ya zuwa wata ranar da za a sanar nan gaba. Sanata mai wakiltar Sakkwato ta Kudu ya wallafa a shafinsa na sohiyal midiya cewa, "Yau…
Read More
‘Yan bindiga sun kashe mutum tara, sun yi awon gaba da tsohon Daraktan CBN a Kaduna

‘Yan bindiga sun kashe mutum tara, sun yi awon gaba da tsohon Daraktan CBN a Kaduna

Daga BASHIR ISAH 'Yan bindiga sun kashe mutum tara a mabambantan hare-hare da suka kai a yankunan ƙananan hukumomin Kauru da Igabi a Jihar Kaduna. Haka nan, sun yi garkuwa da mutum 35 ciki har da wani tsohon Daraka a Babban Bankin Nijeriya (CBN) haɗa da wani ƙanensa da matarsa. Sai kuma wasu mutum tara da suka tagayyara sakamakon hare-haren. A ranar Juma'a 'yan bindiga suka kai hari ƙauyen Kwasam cikin yankin Ƙaramar Hukumar Kauru da misalin karfe 10 na dare inda suka firgita mazaun yankin da harbin bindiga. Bayanai sun ce, maharan sun yi amfani da wasu daga cikin…
Read More
NSCDC za ta haɗa kai da ƙananan hukumomi wajen samar da tsro a Jigawa

NSCDC za ta haɗa kai da ƙananan hukumomi wajen samar da tsro a Jigawa

Daga ABDULLAHI SANI DOGUWA a kano Hukumar tsaro ta Civil Defence ta Ƙasa reshen Jihar Jigawa, ta ce za ta ci gaba da haɗa kai da ƙananan hukumomin jihar domin yaƙi da ƙalubalan tsaro a jihar. Kwamandan rundunar, Mohammed Ɗanjuma ne ya bayyana haka a lokacin da ya ziyarci Majalisar Ƙaramar Hukumar Taura a ci gaba da rangadin da yake yi a tsakanin ƙananan hukumomi 27 da jihar ke da su. Da yake jawabi a yayin ziyarar, Mohammed Ɗanjumma, ya ce sun kai ziyara ne da nufin neman haɗin kai dan ganin an tabbatar da tsaro ingantacce, a yankin Taura…
Read More
‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

‘Yan daba sun wargaza zaɓen fidda gwani a Edo

Daga BASHIR ISAH Wasu 'yan daba ɗauke da makamai sun tarwatsa harabar Lushville Hotel and Suites da ke yankin GRA, Benin, inda nan ne wurin da aka shirya gudanar da zaɓen fidda gwani na Jam'iyyar APC don takarar gwamnan Jihar Edo. An ce sun wargaza shirin tattara sakamakon zaɓen ne inda suka kai wa wasu masu faɗa a ji farmaki tare kuma da ji wa 'yan jarida da dama rauni da farfasa musu kayan aiki. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe Jami'in tattara…
Read More
An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe

An sake buɗe Sahad Stores a Abuja bayan shafe sa’o’i 24 a rufe

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta hannun Hukumar Kula da Haƙƙin Masu Amfani da Kayayyaki (FCCPC), ta sake buɗe katafaren shagon nan na zamani, wato Sahad Stores, da ke yankin Garki a Abuja bayan rufe shi na kimanin sa’o’i 24. MANHAJA ta kalato cewar, an ga harkoki sun ci gaba da gudana a shagon yayin ziyarar da aka kai yankin a ranar Asabar. A ranar Juma’ar da ta gabata gwamnati ta garƙame shagon saboda rashin daidaito da gaskiya a farashin kayayyakinsa. Hukumar FCCPC ta bayyana a cikin sanarwar da ta fitar cewa, bincikenta ya gano farashin da ke rubuce a…
Read More
Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Da Ɗumi-ɗumi: Ghazouani ya zama sabon Shugaban AU

Daga BASHIR ISAH Shugabannin ƙasashen Afirka ƙarƙashin Ƙungiyar Haɗi Kan Afirka (AU) sun zaɓi Shugaban Ƙasar Mauritania, Mohamed Ould Ghazouani, a matsayin sabon shugaban AU na 2024. Ghazouani ya gaji wannan kujera ne daga Shugaba Azali Assoumani na ƙasar Comoros, wanda ya yi riƙe shugabancin ƙungiyar a 2023. ’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya Bankin Access ya naɗa sabuwar Babbar jamiar zartarwar rukunin bankunan ta riƙon ƙwarya An yi zaɓen a ranar Asabar, 17 ga Fabrairu yayin babban taron ƙungiyar karo na 37 wanda ke gudana a Addis Ababa, babban birnin Habasha.
Read More
Gwamnatin Tinubu ta tsayar da ranar ganawa da su Ɗangote kan tsadar siminti

Gwamnatin Tinubu ta tsayar da ranar ganawa da su Ɗangote kan tsadar siminti

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ƙarƙashin jagorancin Bola Ahmed Tinubu, ta kira taron gaggawa tare da kamfanoni masu samar da siminti domin tattauna tashin farashin siminti a ƙasa. Kafar Nairametrics ta rawaito cewa, a halin yanzu farashin buhun siminti mai nauyin 50kg a sassan Legas ya kai N9,500. Majiyar ta ƙara da cewa a watan Janairun da ya gabata, farashin buhun simintin bai wuce N6,000 zuwa N6,500 a nan Legas ɗin ba. Tuni dai wasu ƙananan ‘yan kasuwa suka daina sayar da siminti don gudun abin da ka je ya dawo na hauhawar farashinsa. Sai dai a matsayin wani mataki…
Read More