Labarai

Tinubu ya bada umarnin gaggawa kan raba ton 100,000 na abinci ga ‘yan ƙasa

Tinubu ya bada umarnin gaggawa kan raba ton 100,000 na abinci ga ‘yan ƙasa

Daga BASHIR ISAH A matsayin wani mataki na neman daƙile tsadar rayuwa da ƙarancin abincin da 'yan ƙasa ke fuskanta, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin gaggawa kan a saki kayan abinci har ton 100,000 don amfanin 'yan ƙasa. Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa bayan kammala taron Kwamitin Shugaban Ƙasa Kan Bada Tallafin Abinci a ranar Alhamis. Idris ya ce, gwamnati ta shirya shigo da abinci daga ƙetare domin cike giɓin da ka iya aukuwa bayan kammala raba kayan abincin.…
Read More
Bai wa al’ummarmu tsaro ne babbar manufarmu – Gwamna Lawal

Bai wa al’ummarmu tsaro ne babbar manufarmu – Gwamna Lawal

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jadda cewa, bai wa al’ummar jihar cikakken tsaro shi ne babbar manufar da gwamnatinsa ta sa gaba. Lawal ya bayyana haka ne a wajen tsaron majalisar tsaron jihar da ya gudana a karkashin jagorancinsa  ranar Laraba a Fadar Gwamnatin Jihar da ke Gusau, babban birnin jihar. Cikin sanarwar manema labarai da ya fitar, Kakakin Gwamnan Jihar, Sulaiman Bala Idris, ya ce samar da Dakarun Tsaron Al’umma na Jihar Zamfara da kaddamar da kwamitin kula da Asusun Tallafa wa Sha’anin Tsaro na daga cikin manyan batutuwan da taron ya tattauna. Idris…
Read More
Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen karshe a garsa AFCON 2023

Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen karshe a garsa AFCON 2023

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya taya ’yan wasan Super Eagles murnar samun nasarar kaiwa zagayen karsahe a gasar AFCON 2023 da ke gudana a Ivory Coast. ‘Yan wasan Super Eagles na Nijeriya sun taki wannan nasarar ce bayan da suka yi galaba a kan ‘yan wasan Bafana Bafana na Afirka ta Kudu a wasan da suka buga ranar Laraba a filin Stade de la Paix da ke Bouake. An kare wasan ne da 1-1 bayan shafe mintoci sama da 100, wanda a karshe wasan ya kammala da bugun fenariti. Yanzu dai tun da ta samu tsallake…
Read More
AFCON 2023: Tsohon ɗan majalisar Nijeriya ya mutu a wajen kallon wasan Super Eagles da Afirka ta Kudu

AFCON 2023: Tsohon ɗan majalisar Nijeriya ya mutu a wajen kallon wasan Super Eagles da Afirka ta Kudu

Daga BASHIR ISAH Bayanai da MANHAJA ta samu na nuni da cewa wani tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Delta ya mutu a wajen kallon wasan kwallon da aka buga tsakanin Super Eagles da Afrika ta Kudu na gasar AFCON 2023 a ranar Laraba. Wata majiya ta kusa da ahalin marigayin ta ce, Ojuogboh ya yanke jiki ya fadi ne a lokacin da aka bai wa Afirka ta Kudu damar buga fenariti a kurarren lokaci a yayin wasan da aka buga a filin Stade de la Paix da ke Bouake. A halin rayuwarwa, marigayi Cairo Ojuogboh tsohon dan Majalisar Wakilai…
Read More
Mace ’yar jarida ta fi namiji samar da gamsasshen rahoto kan cin zarafi – Salamatu Abdullahi

Mace ’yar jarida ta fi namiji samar da gamsasshen rahoto kan cin zarafi – Salamatu Abdullahi

"Mata ne suka fi dacewa da aikin jarida" Daga AISHA ASAS Bakuwar tamu ta wannan makon dai bata buqatar doguwar gabatarwa, saboda kasancewarta ‘yar gida ga kaso mafi yawa daga cikin masu karatunmu, musamman ma mazauna Jihar Kaduna. Duk da cewa, fuskarta da gangarar jikinta bata kewaye Arewacin Nijeriya ba, sai dai tuni amon sautin muryarta ya karade mutanen Arewa, musamman ma ma’abota sauraron littafan Hausa. Kwararriya ce da ta qware wurin iya sarrafa murya yayin karanta littafan Hausa, kuma tana gabatar da shiri na musamman domin kawo gyara ga zamantakewar aure. ’Yar jarida ce da ta yi aiki a…
Read More
Kotu ta bai wa gwamnatin Tinubu umarnin daidaita farashin kayayyaki cikin mako guda

Kotu ta bai wa gwamnatin Tinubu umarnin daidaita farashin kayayyaki cikin mako guda

Daga BASHIR ISAH Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Ikoyi, Jihar Legas ce ta ba da wannan umarni a ranar Laraba, 7 ga Fabrairu. Umarnin Kotun ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta daidaita farashin fetur da na saura kayayyaki a cikin mako daya. Mai Shari’a Ambose Lewis-Allagoa ne ya ba da wannan umarni biyo bayan karar da Babban Lauyan Nijeriya kuam mai rajin kare hakkin dan’adam, Femi Falana SAN ya shigar Kotun. A cewar Alkalin, “Na ji mai karar Femi Falana a cikin kararsa mai lamba FHC/L/CS/869/2023 kuma na gano duk da karar da aka shigar kan masu kare kansu,…
Read More
‘Yan bindigar da suka sace ‘yan rakiyar amarya 63 a Katsina sun saki bidiyo

‘Yan bindigar da suka sace ‘yan rakiyar amarya 63 a Katsina sun saki bidiyo

Daga UMAR GARBA a Katsina 'Yan bindigar da suka sace mutane 63 dake kan hanyarsu ta kai amarya gidan mijinta sun saki bidiyo inda suka nuna fuskokin wadanda ake garkuwar da su. Abubuwan da bidiyon ya kunsa shi ne, 'yan bindigar sun fara kalubalantar jami'an tsaro inda suka bayyana cewa idan akwai wanda zai iya karbar mutanen ya zo ya jaraba, ya ga abun da zai faru da shi. Sun kuma bayyana cewar idan ba a fanshi amaryar ba kan lokaci za su sake aurar da ita ga wani mijin. A cikin bidiyoyin wadda yanzu haka ta karade safukan sada…
Read More
Manomi ya yi wa Gwamna Bago kyautar doya don yaba ƙoƙarinsa

Manomi ya yi wa Gwamna Bago kyautar doya don yaba ƙoƙarinsa

Daga BASHIR ISAH Wani manomi a Jihar Neja ya yi wa Gwamnan Jihar, Umaru Mohammed Bago, kyautar luka-lukan doya domin yaba masa da kuma nuna farin cikinsa game da aikin cigaban al’umma da ke gudana a jihar.   Da yake zantawa da shafin Tsalle Daya, Abdullahi Umar ya ce bayan da ya shigo garin Minna, babban birnin jihar ya ga irin ayyukan da Bago ke yi, hakan ya sa ya ga dacewar shirya masa wannan kyauta domin yaba kokarinsa. Mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin siyasa da tsare-tsare, Nma Kolo ne ya karbi doyar a madadin Gwamnan, inda ya…
Read More
NAPPS ta buƙaci Gwamnatin Katsina ta sassauta haraji

NAPPS ta buƙaci Gwamnatin Katsina ta sassauta haraji

Daga WAKILINMU Kungiyar Masu Makarantu Masu Zaman Kansu, watau National Association of Proprietors of Private Schools (NAPPS) reshen jihar Katsina ta roki Gwamnatin jihar Katsina ta rage yawan harajin da hukumomi ke amsa wurin makarantu masu zaman kansu. Shugaban kungiyar Alhaji Mansur Sani Jibia ne ya yi wannan kiran a yayin wani taro da kungiyar ta shirya kuma ta gayyaci masu ruwa da tsaki. Katsina Post ta ruwaito cewa, hukumomin da kungiyar ta gayyata sun hada da hukumar tara kudaden shiga (IRS), sai kuma ma'aikatar ciniki da masana'antu. Shugaban kungiyar ya koka akan yadda membobin kungiyar ke fuskantar matsi lamba…
Read More
Ta haifi ’yan huɗu yayin yi wa ƙasa hidima

Ta haifi ’yan huɗu yayin yi wa ƙasa hidima

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata ’yar Nijeriya, wadda a halin yanzu take tsaka da yi wa kasa hidima (NYSC) ta haifi ’ya’ya hudu a yayin yi wa kasa hidima. Wani faifan bidiyo da ke zagayawa a yanar gizo an yi masa taken, “Haihuwar 'ya’ya hudu yayin hidima” kuma ya nuna matashiyar sanye da kakin NYSC. A cikin faifan bidiyon, mahaifiyar da ke tsaye kusa da wani mutum-mutumi a sakatariyar NYSC, cikinta ya bayyana da girma. A cikin shirin na biye, matar ta matsa kusa da kyamarar, ta bayyana fuskarta. Bidiyon ya nuna fuskokin jarirai hudu da ta haifa. Masu amfani…
Read More