08
Feb
Daga BASHIR ISAH A matsayin wani mataki na neman daƙile tsadar rayuwa da ƙarancin abincin da 'yan ƙasa ke fuskanta, Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin gaggawa kan a saki kayan abinci har ton 100,000 don amfanin 'yan ƙasa. Ministan Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Fadar Shugaban Ƙasa bayan kammala taron Kwamitin Shugaban Ƙasa Kan Bada Tallafin Abinci a ranar Alhamis. Idris ya ce, gwamnati ta shirya shigo da abinci daga ƙetare domin cike giɓin da ka iya aukuwa bayan kammala raba kayan abincin.…