11
Aug
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani atisayen jami'an tsaro na haɗaka da rundunar sojoji ta jagoranta ya yi sanadiyyar sako baki ɗaya mutane 16 da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Ofu ta Jihar Kogi. A ranar Lahadi, 9 ga Agusta 2026 ne aka sace mutanen bayan 'yan bindigar sun farmaki mutanen da ke zirga-zirga a yankin titinan Ojuwo zuwa Ajengo zuwa Memarebo da Ojiwo zuwa Itobe. Bayan samun wani bayanin sirri da ke nuna cewa an garzaya da mutanen ta yankin ƙauyen Adumu a Ƙaramar Hukumar Dekina, dakarun Bataliya ta 21 da haɗin-gwiwar…
