Labarai

’Yan wasan ƙwallon ƙafa ta Katsina Academy sun tafi Belarus

’Yan wasan ƙwallon ƙafa ta Katsina Academy sun tafi Belarus

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina ’Yan wasa takwas daga kwalejin ƙwallon ƙafa na Jihar Katsina sun bar Najeriya zuwa ƙasar Belarus, domin halartar horo a ƙungiyar FC Torpedo Zhodino da ke Minsk. An zaɓi ’yan wasan ne a gasar Malam Dikko Raɗɗa Scouting Tournament da ta gudana a Katsina. Shugaban kwalejin, Ahmed Mohammed, ya ce Gwamna Dikko Raɗɗa ya shirya gasar ne domin gano tare da bunƙasa ƙwararrun matasan ’yan wasan ƙwallon ƙafa daga ƙananan hukumomi 34 na jihar. Ya ce akwai yiwuwar wasu daga cikin ’yan wasan su samu kwangilar ƙwararru da FC Torpedo Zhodino-Belaz bayan kammala horon. Ya…
Read More

Sanata ya warware tsokacin ‘kill Accord’ yayin da sabon hari ya yi ajalin mutum uku gabanin zaɓen gwamnan Osun

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanata Francis Fadahunsi da ke wakiltar mazaɓar Osun ta Gabas a Majalisar Dattawan Nijeriya ya yi bayanin ainihin abin da kalamarsa ta "kill Accord" take nufi, inda ya ce yana nufin a yi galaba akan jam'iyyar a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe ba wai a farmaki mambobinta ba kamar yadda wasu suka ɗauka. Wannan warwara na zuwa ne a daidai lokacin da Rundunar 'Yan sanda ta tabbatar da kisan mutane uku a wani rikicin 'yan ƙungiyar asiri da ya gudana a garin Ilesa da ke jihar, kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamnan jihar da…
Read More

Zaɓen Osun: Gwamnatin Amurka ta amsa wa ƙorafin mawaƙi Davido ga Shugaba Trump

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen mawaƙin Nijeriya, David Adeleke da aka fi sani da Davido, ya yi iƙirarin cewa gwamnatin Amurka ta ba shi amsa kan kokawa da ya yi game da zaɓen da ke tafe na gwamnan jihar Osun. Davido ya yi wannan tsokaci ne a sahfinsa na kafar X yayin da al'amuran siyasa a ihar suka yi kamari gabanin zaɓen, wanda za a gudanar a ranar Asabar. Kawun mawaƙin, Gwamna Ademola Adeleke na jihar, na neman a sake zaɓar sa a karo na biyu a kujerar gwamnan jihar a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar AP, wato Accord Party.…
Read More

Sarkin Dutse ya nemi NUJ ta tsaftace aikin jarida

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mai Martaba Sarkin Dutse a Jihar Jigawa, Dakta Hameem Nuhu Sanusi ya nuna damuwa akan yadda wasu da ba su samu ƙwarewa ba suke shiga harkar aikin jarida a Nijeriya, inda ya ce ayyukansu na haifar da cin fuska ga darajar fannin. Manhaja ta ruwaito cewa, Sarkin ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi baƙuncin Shugaban Ƙungiyar 'Yan jarida ta Ƙasa (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya da mambobin Majalisar Zartarwarsa (NEC), waɗanda suka ziyarce shi a fadarsa a lokacin da suka je Dutse taron NEC da NUJ reshen Jigawa ta shirya. Alhaji Hameem Sanusi…
Read More

Shekarau ya buƙaci a samar da ƙarin damarmaki ga matasa bayan ɗaukar nauyin yaye ɗaliban NCE 830

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Aƙalla ɗalibai guda 830 ne tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon sanatan Kano ta Tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau ya ɗauki nauyin yaye su bayan kammala karatun NCE daga Community College of Education da ke Kano, a wani yanayi na bunƙasa ilimin malamai da inganta ɗan-adam a jihar. A safiyar ranar Asabar ne aka gabatar wa ɗaliban shaidar kammala karatun nasu, wanda aka gudanar a ɗakin taro na School of Arabic Studies (SAS) a Kano, wanda kuma ya kawo nasarar kammala shirin ɗaukar nauyi karatu da Shekarau ya samar a 2022 a lokacin da yake…
Read More
Musa Funtua ya ƙaddamar da ƙungiyar Gwagware Continuity a Katsina

Musa Funtua ya ƙaddamar da ƙungiyar Gwagware Continuity a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina,Hon Musa Adamu Funtua,ya ƙaddamar da ƙungiyar a garin Funtua sa mai suna Gwagware Continuity dan samun nasarar zaɓen 2027. Hon Musa Adamu ya bayyana mutanen da suka samar da ƙungiyar a matsayin mutane masu mutunci da kima ga al'ummar Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya, dan haka babu ko shakka akwai gagarimar nasara a wannan tafiya ta samun nasara ga 'yan takarar jamiyyar APC tunda sama har ƙasa, nji Hon Musa Adamu Funtua. Kwamishinan mai riƙe da sarautar Ɗan Kafin Katsina,ya kuma tabbatar da cewa,daga yau wannan ƙungiyar babu…
Read More

Rikicin shugabanci: An halaka ‘yan majalisar shurar ISWAP huɗu

Rikicin shugabanci acikin ƙungiyar ISWAP na ƙara tsananta biyo bayan wani sabon rahoton sirri da ke nuna cewa an kashe mambobi huɗu na Majalisar Shura ta ƙungiyar. A cewar wani rahoton sirri daga Zagazola Makama, mambobin guda huɗu, waɗanda aka garkame su a makon da ya gabata ta hannun dakarun ISWAP, an ce wani babban jami’in ISWAP mai suna Ba Shuwa ne ya kashe su a maɓoyarsu ta Kwatan Dila a ranar Laraba, 6 ga Agusta. Wannan sabon al'amari ana kyautata zaton zai ƙara bayyana ƙaruwar rashin jituwa a tsakanin 'ya'yan ƙungiyar da kuma samun rarrabuwar kawuna a cikinta wanda…
Read More
Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Katsina United ya mutu

Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Katsina United ya mutu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ozah Chinedu ɗan wasan ƙwallon kafa na ƙungiyar Katsina United ya rasu a yayin da yake buga wasan sada zumunta tsakanin ƙungiyar sa da ta Niger Tornadoes a filing wasa na Muhammadu Dikko a Katsina. Dan wasan wanda tsohon ɗan wasan Kano Pillars ne kafin zuwan sa Katsina United ya gamu da ajalinsa a yayin da ana tsaka da wasa inda aka ga ya faɗi ƙasa. Sanarwa daga sashin hulɗa da jama'a ƙungiyar Katsina United ta bayyana cewar an yi gaggawar kai shi asibitin ƙwararru na K_Dara a Katsina amma daga baya ya rasu. Mutuwar…
Read More

Kwamared Ɗahiru Maihula ya ƙudiri aniyar zama kakakin ƙungiyar matasan Nijeriya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Yayin da zaɓen ƙungiyar matasan Nijeriya ta "Youth Assembly of Nigeria" (YAN) reshen jihar Kano ke cigaba da ƙaratowa, Kwamared Muhammad Ɗahiru Maihula ya ƙudiri aniyar tsaya wa takara domin neman kujerar kakaki a tafiyar jagorancin ƙungiyar. Kwamared Maihula ya bayyana haka ne a wata takarda da ke ɗauke da sanya hannunsa da aka fitar a ranar Litinin, 10 ga watan Agusta, 2026. A cewarsa, ya ɗauki wannan mataki ne domin bayar da ga gagarumar gudunmawa ga harkokin shugabancin ƙungiyar bisa la'akari da cancanta da kuma wasu muƙamai da ya riƙe acikin YAN. A…
Read More

‘Yan bindiga 17 da ‘yan sanda 10 sun rasu yayin musayar wuta a Kebbi

Kimanin 'yan bindiga 17 da ’yan sanda 10 ne suka rasa rayukansu yayin wata arangama a lokacin da wani gungun ’yan bindiga ke ƙoƙarin zuwa Jihar Kebbi daga Jihar Zamfara. Haka kuma, rundunar 'yan sanda ta ce fararen hula biyu sun rasu a yayin musayar wutar da aka yi tsakanin ’yan ta’addar da jami’an tsaro a yankin Rafin Makuku na Ƙaramar hukumar Sakaba da ke Jihar Kebbi a safiyar ranar Litinin. Mazauna yankin sun kiyasta cewa ’yan bindigar sun kai kimanin 240 da ke kan babura sama da 200. Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun fito ne daga yankin Sangeko…
Read More