Labarai

Rikicin shugabanci: An halaka ‘yan majalisar shurar ISWAP huɗu

Rikicin shugabanci acikin ƙungiyar ISWAP na ƙara tsananta biyo bayan wani sabon rahoton sirri da ke nuna cewa an kashe mambobi huɗu na Majalisar Shura ta ƙungiyar. A cewar wani rahoton sirri daga Zagazola Makama, mambobin guda huɗu, waɗanda aka garkame su a makon da ya gabata ta hannun dakarun ISWAP, an ce wani babban jami’in ISWAP mai suna Ba Shuwa ne ya kashe su a maɓoyarsu ta Kwatan Dila a ranar Laraba, 6 ga Agusta. Wannan sabon al'amari ana kyautata zaton zai ƙara bayyana ƙaruwar rashin jituwa a tsakanin 'ya'yan ƙungiyar da kuma samun rarrabuwar kawuna a cikinta wanda…
Read More
Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Katsina United ya mutu

Ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙungiyar Katsina United ya mutu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Ozah Chinedu ɗan wasan ƙwallon kafa na ƙungiyar Katsina United ya rasu a yayin da yake buga wasan sada zumunta tsakanin ƙungiyar sa da ta Niger Tornadoes a filing wasa na Muhammadu Dikko a Katsina. Dan wasan wanda tsohon ɗan wasan Kano Pillars ne kafin zuwan sa Katsina United ya gamu da ajalinsa a yayin da ana tsaka da wasa inda aka ga ya faɗi ƙasa. Sanarwa daga sashin hulɗa da jama'a ƙungiyar Katsina United ta bayyana cewar an yi gaggawar kai shi asibitin ƙwararru na K_Dara a Katsina amma daga baya ya rasu. Mutuwar…
Read More

Kwamared Ɗahiru Maihula ya ƙudiri aniyar zama kakakin ƙungiyar matasan Nijeriya

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Yayin da zaɓen ƙungiyar matasan Nijeriya ta "Youth Assembly of Nigeria" (YAN) reshen jihar Kano ke cigaba da ƙaratowa, Kwamared Muhammad Ɗahiru Maihula ya ƙudiri aniyar tsaya wa takara domin neman kujerar kakaki a tafiyar jagorancin ƙungiyar. Kwamared Maihula ya bayyana haka ne a wata takarda da ke ɗauke da sanya hannunsa da aka fitar a ranar Litinin, 10 ga watan Agusta, 2026. A cewarsa, ya ɗauki wannan mataki ne domin bayar da ga gagarumar gudunmawa ga harkokin shugabancin ƙungiyar bisa la'akari da cancanta da kuma wasu muƙamai da ya riƙe acikin YAN. A…
Read More

‘Yan bindiga 17 da ‘yan sanda 10 sun rasu yayin musayar wuta a Kebbi

Kimanin 'yan bindiga 17 da ’yan sanda 10 ne suka rasa rayukansu yayin wata arangama a lokacin da wani gungun ’yan bindiga ke ƙoƙarin zuwa Jihar Kebbi daga Jihar Zamfara. Haka kuma, rundunar 'yan sanda ta ce fararen hula biyu sun rasu a yayin musayar wutar da aka yi tsakanin ’yan ta’addar da jami’an tsaro a yankin Rafin Makuku na Ƙaramar hukumar Sakaba da ke Jihar Kebbi a safiyar ranar Litinin. Mazauna yankin sun kiyasta cewa ’yan bindigar sun kai kimanin 240 da ke kan babura sama da 200. Rahotanni sun ce ’yan bindigar sun fito ne daga yankin Sangeko…
Read More

Jami’an tsaro sun ceto mutum 16 da aka sace a Jihar Kogi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Wani atisayen jami'an tsaro na haɗaka da rundunar sojoji ta jagoranta ya yi sanadiyyar sako baki ɗaya mutane 16 da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a Ƙaramar Hukumar Ofu ta Jihar Kogi. A ranar Lahadi, 9 ga Agusta 2026 ne aka sace mutanen bayan 'yan bindigar sun farmaki mutanen da ke zirga-zirga a yankin titinan Ojuwo zuwa Ajengo zuwa Memarebo da Ojiwo zuwa Itobe. Bayan samun wani bayanin sirri da ke nuna cewa an garzaya da mutanen ta yankin ƙauyen Adumu a Ƙaramar Hukumar Dekina, dakarun Bataliya ta 21 da haɗin-gwiwar…
Read More

DSS ta sako kafinta bayan gano ba shi da hannu a sace ‘yan makarantar Oyo, ta biya diyyar miliyan N3

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Tsaro ta Farin kaya DSS, ta saki wani kafinta mai suna Mustapha Marwana, wanda aka kama bisa zargin sa da hannu a garkuwa da halaka ɗalibai da malaman wasu makarantu a yankin Oriire da ke Jihar Oyo. Darakta Janar na hukumar, Tosin Ajayi ne ya bayar da umarnin sakin nasa bayan masu bincike sun wanke shi daga dukkan wani abin da yake alaƙanta shi da harin. Wata majiyar tsaro da ke da kusanci da batun ta ce kwamitin binciken DSS ya gudanar da bincike mai zurfi akan zargin Marwana da hannu al'amarin kana…
Read More

Sojoji sun ƙwato makamai bayan daƙile harin ISWAP a Borno

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Dakarun tsaro na Atisayen Haɗin Kai a Arewa maso Gabashin Nijeriya, sun yi nasarar halaka wasu 'yan ta'adda a lokacin da suka daƙile wani hari da mayaƙan ISWAP suka yi yunƙurin ƙaddamarwa a sansanin sojoji da ke yankin Gajiram a Ƙaramar Hukumar Nganzai ta Jihar Borno. Jami'in Hulɗa da jama'a na rundunar na riƙo, Kyaftin Mohammed Goni, wanda ya sanar da haka a wata takarda da ya fitar a ranar Litinin, ya ce wani adadi mai yawa na 'yan ta'adda ya ƙaddamar da mummunan farmaki a sansanin dakarun na sansanin FOB a Gajiram da…
Read More

An yi jana’izar ‘yan ƙauyen Benuwai 15 da aka halaka yayin da manoma ke biyan ‘yan bindiga tara

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Asabar aka gudanar da jana'izar mutane goma sha biyar da aka halaka a ranar 28 ga watan Yuli, 2026 a yankin Ƙaramar Hukumar Otukpo da ke Jihar Benuwai. A cewar wani rahoto da AIT ya fitar, mazauna ƙauyen Efeyi-Utikpi ne suka jagoranci jana'izar, makonni bayan irin harin ya auku a ƙaramar hukumar. Rahoton ya ce, harin ya yi sanadiyyar lalata gidaje da jefa al'ummar yankin cikin ƙunci da firgici, inda jagororin jama'a suke kira ga gwamnatocin tarayya da jiha su daina taƙaice matakinsu akan yin alla-wadai tare da ɗaukar matakan samar da…
Read More

EU ta musanta yin watsi da gayyatar INEC ta neman ta sanya ido a zaɓen 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja A ranar Litinin Jakadan Majalisar Tarayyar Turai (EU) ga Nijeriya da ECOWAS, Gautier Mignot a wata sanarwa, ya bayyana cewa, rahotannin da ke yawo cewa EU ta yi watsi da gayyatar da Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta yi mata na neman ta sanya ido a babban zaɓen 2027 da ke tafe a Nijeriya ba gaskiya ba ne kuma jita-jita ce mara asali. Mista Mignot ya tabbatar da cewa, majalisar ta sami saƙon gayyatar daga hukumar zaɓen Nijeriyar tun a watan Afrilu kuma ta bayar da amsa a kai, inda ta ce za ta…
Read More
Mutum 1,932 aka kashe cikin wata uku a Arewa maso Gabas – Majalisar Dinkin Duniya

Mutum 1,932 aka kashe cikin wata uku a Arewa maso Gabas – Majalisar Dinkin Duniya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Majalisar Dinkin Duniya Mai Kula da Daidaita Ayyukan Agaji (OCHA) ta bayyana cewa aƙalla mutum 1,932 ne suka rasa rayukansu a jihohin Borno, Adamawa da Yobe tsakanin watan Afrilu zuwa Yunin 2026, sakamakon matsalolin tsaro da suka addabi yankin. Rahoton, wanda ya fito a ƙarƙashin Binciken Hanyar Isar da Agaji na Farkon Shekarar 2026, ya nuna cewa rashin tsaro, hare-hare kan ma'aikatan agaji da kayayyakinsu, cikas na hukumomi da kuma matsanancin yanayin muhalli ne suka fi kawo tsaiko ga ayyukan jinƙai a yankin. Rahoton ya samo bayanansa ne daga ƙungiyar Aiki Kan Hanyar Isar da…
Read More