Labarai

Ɗan wasan Katsina United da aka sanar da mutuwarsa ya farfado a mutuware

Ɗan wasan Katsina United da aka sanar da mutuwarsa ya farfado a mutuware

Daga UMAR GARBA a Katsina Tun da farko an kai ɗan wasan Katsina United, Chinedu Ozor, sashen kula da marasa lafiya na gaggawa na babbar asibitin Katsina bayan da aka sanar da mutuwarsa a jiya Talata, bayan ɗan wasan ya faɗi a yayin da yake taka wasan share fagen shiga kakar wasa ta firimiyar Najeriya (NPFL) a ranar Talata. Rahotanni sun ce Ozor ya ya yanke jiki ya fadi ne a lokacin wasan Katsina United da Niger Tornadoes, inda nan da nan aka garzaya da shi asibiti da ke kusa, sai dai likita ya tabbatar da mutuwarsa tun a lokacin.…
Read More

NiMet ta yi hasashen ambaliya a Kano, Kaduna, Abuja da wasu jihohi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar kula da Yanayi ta Ƙasa NiMet, ta yi hasashen samun mamakon ruwan sama mai ɗauke da tsawa a sassan jihohin Nijeriya da tsawa a ranar Laraba, 12 ga Agusta, 2026, don haka ne ta shawarci mazauna a wuraren da ke fuskantar barazanar ambaliya da su kasance a ankare. A wani saƙon hasashen yanayi na kullum da NiMet ta wallafa a kafar X a ranar Talata, hukumar ta ce ana tsammanin samun hadari a jihohin arewacin Nijeriya da safe, tare da tsawa da matsakaicin ruwan sama a Adamawa, Taraba, Bauchi, Gombe, Jigawa, Kaduna da…
Read More
Masoyin Aliyu Wadada ya raba wa mata injin niƙa a Lafia

Masoyin Aliyu Wadada ya raba wa mata injin niƙa a Lafia

Daga JOHN D. WADA a Lafia Wani matashin ɗan siyasa Abbas Zanwa wanda masoyi ne kuma wakilin yaƙin neman takarar mai neman kujerar gwamnan jihar Nasarawa na 2027 a Jam'iyyar APC wato Sanata Ahmad Aliyu Wadada daga gundumar Zanwa da ke ƙaramar hukumar Lafia ta Jihar Nasarawa ya raba wa mata injinan niƙa guda 10, domin taimaka musu wajen samun sana’o’in dogaro da kai. Abbas ya bayyana cewa tallafin ya shafi mata ne musamman waɗanda ke zaune a yankunan da ke ƙarƙashin gundumar Zanwa inda yace burinsa shi ne ganin mata sun rungumi sana’o’in dogaro da kai domin rage musu…
Read More

Kyautar lambar yabo daga Blueprint za ta ƙarfafa gaskiya da adalci yayin sauye-sauye a Zamfara, inji Gwamna Lawal

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya sanar da karɓar kyautar lambar yabo na Gudanar da Kuɗaɗen Al'umma bisa Gaskiya da Adalci ta jaridar Blueprint ta 2025, yana mai bayyana matakin a matsayin ƙarfafa wa ayyukan sauye-sauye da gwamnatinsa ke yi a jihar wajen tabbatar da tsare gaskiya da adalci da kuma gudanar da kuɗaɗen al'umma bisa tsari mai kyau. Gwamnan ya bayyana haka ne a wata takarda da ke ɗauke da sanya hannun Darakta-Janar na Yaɗa Labaransa, Nuhu Salihu Anka, yayin amsa wa saƙo daga hukumar gudanarwar ta jaridar Blueprint na sanar da…
Read More
’Yan wasan ƙwallon ƙafa ta Katsina Academy sun tafi Belarus

’Yan wasan ƙwallon ƙafa ta Katsina Academy sun tafi Belarus

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina ’Yan wasa takwas daga kwalejin ƙwallon ƙafa na Jihar Katsina sun bar Najeriya zuwa ƙasar Belarus, domin halartar horo a ƙungiyar FC Torpedo Zhodino da ke Minsk. An zaɓi ’yan wasan ne a gasar Malam Dikko Raɗɗa Scouting Tournament da ta gudana a Katsina. Shugaban kwalejin, Ahmed Mohammed, ya ce Gwamna Dikko Raɗɗa ya shirya gasar ne domin gano tare da bunƙasa ƙwararrun matasan ’yan wasan ƙwallon ƙafa daga ƙananan hukumomi 34 na jihar. Ya ce akwai yiwuwar wasu daga cikin ’yan wasan su samu kwangilar ƙwararru da FC Torpedo Zhodino-Belaz bayan kammala horon. Ya…
Read More

Sanata ya warware tsokacin ‘kill Accord’ yayin da sabon hari ya yi ajalin mutum uku gabanin zaɓen gwamnan Osun

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanata Francis Fadahunsi da ke wakiltar mazaɓar Osun ta Gabas a Majalisar Dattawan Nijeriya ya yi bayanin ainihin abin da kalamarsa ta "kill Accord" take nufi, inda ya ce yana nufin a yi galaba akan jam'iyyar a zaɓen gwamnan jihar da ke tafe ba wai a farmaki mambobinta ba kamar yadda wasu suka ɗauka. Wannan warwara na zuwa ne a daidai lokacin da Rundunar 'Yan sanda ta tabbatar da kisan mutane uku a wani rikicin 'yan ƙungiyar asiri da ya gudana a garin Ilesa da ke jihar, kwanaki kaɗan kafin zaɓen gwamnan jihar da…
Read More

Zaɓen Osun: Gwamnatin Amurka ta amsa wa ƙorafin mawaƙi Davido ga Shugaba Trump

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Sanannen mawaƙin Nijeriya, David Adeleke da aka fi sani da Davido, ya yi iƙirarin cewa gwamnatin Amurka ta ba shi amsa kan kokawa da ya yi game da zaɓen da ke tafe na gwamnan jihar Osun. Davido ya yi wannan tsokaci ne a sahfinsa na kafar X yayin da al'amuran siyasa a ihar suka yi kamari gabanin zaɓen, wanda za a gudanar a ranar Asabar. Kawun mawaƙin, Gwamna Ademola Adeleke na jihar, na neman a sake zaɓar sa a karo na biyu a kujerar gwamnan jihar a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar AP, wato Accord Party.…
Read More

Sarkin Dutse ya nemi NUJ ta tsaftace aikin jarida

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mai Martaba Sarkin Dutse a Jihar Jigawa, Dakta Hameem Nuhu Sanusi ya nuna damuwa akan yadda wasu da ba su samu ƙwarewa ba suke shiga harkar aikin jarida a Nijeriya, inda ya ce ayyukansu na haifar da cin fuska ga darajar fannin. Manhaja ta ruwaito cewa, Sarkin ya bayyana haka ne yayin da ya karɓi baƙuncin Shugaban Ƙungiyar 'Yan jarida ta Ƙasa (NUJ), Kwamared Alhassan Yahaya da mambobin Majalisar Zartarwarsa (NEC), waɗanda suka ziyarce shi a fadarsa a lokacin da suka je Dutse taron NEC da NUJ reshen Jigawa ta shirya. Alhaji Hameem Sanusi…
Read More

Shekarau ya buƙaci a samar da ƙarin damarmaki ga matasa bayan ɗaukar nauyin yaye ɗaliban NCE 830

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Aƙalla ɗalibai guda 830 ne tsohon gwamnan Jihar Kano kuma tsohon sanatan Kano ta Tsakiya, Malam Ibrahim Shekarau ya ɗauki nauyin yaye su bayan kammala karatun NCE daga Community College of Education da ke Kano, a wani yanayi na bunƙasa ilimin malamai da inganta ɗan-adam a jihar. A safiyar ranar Asabar ne aka gabatar wa ɗaliban shaidar kammala karatun nasu, wanda aka gudanar a ɗakin taro na School of Arabic Studies (SAS) a Kano, wanda kuma ya kawo nasarar kammala shirin ɗaukar nauyi karatu da Shekarau ya samar a 2022 a lokacin da yake…
Read More
Musa Funtua ya ƙaddamar da ƙungiyar Gwagware Continuity a Katsina

Musa Funtua ya ƙaddamar da ƙungiyar Gwagware Continuity a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kwamishinan Lafiya na Jihar Katsina,Hon Musa Adamu Funtua,ya ƙaddamar da ƙungiyar a garin Funtua sa mai suna Gwagware Continuity dan samun nasarar zaɓen 2027. Hon Musa Adamu ya bayyana mutanen da suka samar da ƙungiyar a matsayin mutane masu mutunci da kima ga al'ummar Jihar Katsina da ma ƙasa baki ɗaya, dan haka babu ko shakka akwai gagarimar nasara a wannan tafiya ta samun nasara ga 'yan takarar jamiyyar APC tunda sama har ƙasa, nji Hon Musa Adamu Funtua. Kwamishinan mai riƙe da sarautar Ɗan Kafin Katsina,ya kuma tabbatar da cewa,daga yau wannan ƙungiyar babu…
Read More