Labarai

Gwamnatin Kebbi za ta kula da iyalan ‘yan sanda da suka rasu bakin daga

Gwamnatin Kebbi za ta kula da iyalan ‘yan sanda da suka rasu bakin daga

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamnatin jihar Kebbi ta jaddada ƙudirin ta na kulawa da iyalan 'yan sanda da suka rasu a bakin daga yayin artabu da 'yan ta'adda a ƙaramar hukumar mulki ta Sakaba. Ya yi wannan bayanin ne jiya a fadar gwamnatin jihar yayin da ya ke karɓar baƙuncin wata tawaga daga ofishin Sufeto Janar na 'yan sandan Nijeriya Mista Olatunji Disu ƙarƙashin jagorancin mataimakin Sufeto Janar Umar Dada don jajentawa gwamnati da kuma al'ummar jihar Kebbi. Gwamna Malam Nasir Idris ya jajentawa rundunar 'yan sanda tare da bayyana cewa rayuwar su ba ta tafi a banza ba…
Read More
Gwamnatin Kebbi ta raba wa makarantun gaba da sakandare motoci

Gwamnatin Kebbi ta raba wa makarantun gaba da sakandare motoci

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamna Malam Nasir Idris ya raba wa makarantun gaba da sakandare mallakar jihar Kebbi guda bakwai da ke faɗin jihar manyan motoci ƙirar Bas-bas. Da ya ke jawabi yayin ƙaddamar da motocin a gidan Gwamnatin jihar da ke Birnin Kebbi ranar Laraba ɗin nan, gwamna Nasir Idris ya ce wannan ya biyo bayan la'akari da akwai buƙatar motoci musamman ga ɗalibai don ƙara saukaka musu zirga-zirga daga makarantu zuwa wajen kwana musamman waɗanda ke zama a cikin gari da ke da nisa da makarantu. Ya ce yana fata hukumomin makarantun za su riƙe motocin tare…
Read More
An buƙaci gwamnatin Gombe ta bai wa matasa masu sa-kai fifiko wajen ɗaukar ma’aikatan tsaro

An buƙaci gwamnatin Gombe ta bai wa matasa masu sa-kai fifiko wajen ɗaukar ma’aikatan tsaro

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Ƙungiyar BREACH Initiative for Leadership Development ta yi kira ga Gwamnatin Jihar Gombe da ta bai wa matasan da suka yi aiki a ƙungiyoyin sa-kai masu sanya kayan aiki na musamman fifiko a duk lokacin da za a ɗauki sabbin jami’an ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro. Ƙungiyar ta yi wannan kiran ne a yayin gasar fareti da aka gudanar a Gombe domin bikin ranar matasa ta duniya ta shekarar 2026. Da yake jawabi a wajen taron, tsohon daraktan hukumar wayar da kan jama’a ta ƙasa (NOA) a Jihar Gombe, Ado Solomon, ya ce mambobin…
Read More
Gyaran farce bisa tsari: Karamar hanya da ke kare lafiyar ƙafa

Gyaran farce bisa tsari: Karamar hanya da ke kare lafiyar ƙafa

Daga AISHA ASAS Akwai wasu abubuwa da muke yi a kullum waɗanda muke ɗauka ba su da wani tasiri mai yawa a rayuwa. Daga cikinsu akwai yadda muke kula da farcen ƙafa. Ga mutane da dama, gyaran farce wani ɓangare ne na tsafta kawai ko kuma gyaran kwalliya, amma masana lafiya sun nuna cewa yadda mutum yake yanke farcensa na iya taimaka masa wajen kauce wa matsalolin da kan jawo ciwo da wahalar jinya. Kafa na ɗaukar nauyin jiki gaba ɗaya, kuma duk wata matsala da ta shafe ta na iya shafar tafiyar mutum da sauran harkokinsa na yau da…
Read More

‘Yan sanda sun bada belin sanatan Osun bayan bincike kan barazanar mambobin AP

Daga BELLO A BABAJI a Abuja Sanatan da ke wakiltar Osun ta Gabas, Francis Fadahunsi, ya samu beli daga hannun rundunar 'yan sandan jihar bayan bincikensa akan kalamansa da suka tayar da hazo na "kill Accord" a jihar. A wani bidiyo da aka wallafa a kafar X a ranar Talata, an ga yadda sanatan APCn ke magana cikin harshen Yarabanci, inda ya kirayi magoya bayansa da su halaka mambobin jam'iyyar Accord Party (AP). Saidai daga bisani ya gaggauta kare kalaman nasa bayan sun tayar da ƙura a kafafen sada zumunta, inda ya ce an fassara su ta wata hanya. A…
Read More
Zamfara AGILE ta gudanar da horarwa na kwanaki biyu

Zamfara AGILE ta gudanar da horarwa na kwanaki biyu

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Shirin inganta Ilimin 'yan matan Zamfara AGILE, ya fara horo na kwana biyu yau Talata, a Taula Apartment da ke Gusau ga 'yan kwangila, ma'aikatan gini, injiniyoyi da kuma masu ba da shawara kan kula da muhalli. Bitar ta mayar da hankali kan aiwatar da shirye shiryen gudanar da muhalli da zamantakewa, ESMPs, a fadin wuraren aikin AGILE a jihar. Da yake buɗe taron bitar, mataimakin mai gudanar da ayyukan hukumar ta AGILE a Zamfara, Dr. Salisu Dalhatu ya ce manufar ita ce a wayar da kan mahalarta bitar game da haɗurran muhalli da ke…
Read More
Katsina United ta sake tabbatar da mutuwar ɗan wasanta da aka ce ya farfaɗo a ɗakin ajiyar gawarwaki

Katsina United ta sake tabbatar da mutuwar ɗan wasanta da aka ce ya farfaɗo a ɗakin ajiyar gawarwaki

Daga UMAR GARBA a Katsina Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Katsina United da masu sha’awar ƙwallo a jihar Katsina sun shiga jimami bayan da ƙungiyar ta sanar cewa sabon ɗan wasanta, Ozoh Chinedu, wanda a baya ya taka leda a Kano Pillars, ya rasu. Rahotanni sun ce Chinedu ya rasu a safiyar Talata, 11 ga Agusta, 2026, bayan samun matsalar lafiya yayin wasan sada zumunta da Katsina United ta yi da Niger Tornadoes a filin wasa na Muhammadu Dikko da ke Katsina. A cikin wata sanarwa da sashen yaɗa labarai na Katsina United ya fitar, an bayyana cewa an ba ɗan…
Read More
Sufeto-Janar na ‘ yan sanda ya yi ta’aziyya ga iyalan ‘yan sanda da ‘yan ta’adda suka kashe a Kebbi

Sufeto-Janar na ‘ yan sanda ya yi ta’aziyya ga iyalan ‘yan sanda da ‘yan ta’adda suka kashe a Kebbi

Daga MUHAMMAD SADISU ABUBAKAR a Birnin Kebbi Sufeto-Janar na 'Yan Sandan Najeriya, IGP Olatunji Rilwan Disu ya yi ta'aziyya ga iyalai da gwamnati da kuma al'ummar Jihar Kebbi dangane da rasuwar 'yan sanda 10 a fagen fama. Sufeto-Janar Disu ya turo wata tawaga mai karfi ƙarƙashin jagorancin muƙaddashin Sufeto-Janar mai kula da dabarun yaƙi, DIG Umar Shehu Nadada, zuwa Birnin Kebbi domin gabatar da juyayinsa akan lamarin. A sa'ilin da ya kai ziyarar ban girma ga Gwamna Nasir Idris a gidan gwamnati, DIG Nadada ya shaida masa cewar, ya zo Kebbi ne bisa umurnin IG Disu dangane da lamarin da…
Read More

JAMB ta zayyano kurakurai da ɗaliban UTME da DE kan yi yayin shigar da bayanansu

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Haɗaka ta Shirya Jarrabawar Ɗalibai masu neman shiga Manyan Makarantu (JAMB), ta gargaɗi ɗalibai akan kurakuran da ka iya haifar musu da tsaiko da suke yi yayin shigar da bayanansu domin rubuta jarrabawar Unified Tertiary Matriculation Examination (UTME) ko rajistar Direct Entry (DE). A cewar JAMB, kuskure guda a matakin ka iya samar da babbar matsala yayin neman gurbin shiga babbar makaranta ta hannunta. JAMB ta bayyana haka ne a wani faifan bidiyo da ta fitar domin bayar da shawara ga waɗanda hakan ya shafa, wanda ta yi wa laƙabi da "JAMB Ekplained"…
Read More
Sojoji sun daƙile harin ‘yan bindiga a Katsina

Sojoji sun daƙile harin ‘yan bindiga a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Rundunar sojin Najeriya ta 17 dake Katsina ta fatattaki wasu 'yan bindiga masu tarin yawa bayan da suka yi yunƙurin kai hari a ƙaramar hukumar Charanci da ke jihar Katsina. Rundunar ta samu nasarar daƙile harin ne bayan ta samu kiran gaggawa da misalin ƙarfe 11:20 na safe a ranar Talata da ta gabata, inda aka sanar da cewa wasu da ake zargin ’yan bindiga ɗauke da muggan makamai sun taru a kusa da ƙauyen Kaɗɗanya da ke yankin. Zagazola Makama mai sharhi kan tsaro ya bayyana cewa wani rahoton tsaro ya ce sojojin da…
Read More