Labarai

Hukumar DSS na shirin ɓullo da sabbin dabaru na shawo kan matsalar tsaro a Arewa maso Yamma

Hukumar DSS na shirin ɓullo da sabbin dabaru na shawo kan matsalar tsaro a Arewa maso Yamma

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Daracktocin hukumar tsaro na farin kaya na Arewa maso Yamma da ya ƙunshi jihohi 7 sun fara gudanar da taro a Katsina domin ƙara haɗin kai da ɓullo da shirin sabbin dabarun shawo kan matsalar tsaro a yankin. A jawabin sa Gwamnan Jihar Katsina Malam Dikko Raɗɗa ya bayyana cewa matsalar tsaro da yadda ake tunkarar matsalar a jihohin Arewa maso Yamma yakamata ya zama bai ɗaya domin haka ya yaba wa hukumar DSS da sauka shirya wannan taro mai taken haɗa kai don yaƙar ta'addanci(United against Terror). Gwamnan ya yaba wa da haɗin kai…
Read More

‘Yan sanda ceto ɗan shekara 10 bayan kama mutum biyu bisa zargin garkuwa a Sakkwato

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rundunar 'Yan sanda a Jihar Sakkwato ta yi nasarar cafko wasu mutum guda biyu bisa zargin su da hannu a ayyukan garkuwa da mutane a tisaye mabambanta da kuma ceto wani yaro ɗan shekara 10 da aka yi zargin an sace shi ne a jihar. Rundunar ta ce ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin, mai suna Abdullahi Buba da aka sani da "Osho", mamba ne a wata sananniyar dabar garkuwa a sassan Jihar Sakkwato. Kakakin rundunar, DSP Ahmad Rufa'i, ya ce an kama Buba ne a ranar 8 ga Agusta yayin wani samame da…
Read More

Gwamnan Kebbi ya naɗa shugabanci bayan samar da sabuwar gunduma

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi ya amince da samar da sabuwar gunduma da ta ƙunshi ƙauyuka guda takwas a Ƙaramar Hukumar Dandi da ke jihar. Haka kuma, gwamnan ya amince da samar da sabon jagorancin ƙauye a Ƙaramar Hukumar Augie a matsayin wani ɓangare na ƙarfafa gwamnatin gargajiya da inganta shugabanci daga tushe a jihar. Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomin da Sarauta, Alhaji Garba Umar Dutsinmari ne ya sanar da haka a wata takarda a Birnin Kebbi, ranar Alhamis. A cewar kwamishinan, an kafa sabuwar Gundumar Buma ne daga Gundumar Dolekaina ta Ƙaramar Hukumar…
Read More

Ministan Tsaro zai yi jawabi yayin da Blueprint ta shirya jagorantar taron karrama gwarazan ‘yan ƙasa na 2025

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kamfanin Jaridun Blueprint ya shirya jagorantar taronsa na lakcar shekara-shekara ta 2025 da shirye-shirye da kuma bayar da lambobin yabo a Abuja, wanda ake sa ran zai haɗa jami'an gwamnati, masu samar da tsare-tsare, masana harkar difulomasiyya, jagororin tsaro, 'yan majalisar dokoki, shugabannin masana'antu, malamai, ƙungiyoyin al'umma, abokan hulɗar samar da ci-gaba da sauran masu ruwa da tsaki. Manhaja ta ruwaito cewa, an shirya gudanar da taron ne a ranar Talata, 18 ga Agusta, 2026, a babban ɗakin taro na Bola Ahmed Tinubu, wanda za a fara da misalin ƙarfe 10:00 na safe. Taron…
Read More
Ranar matasa ta duniya: Mahdi ta yi kira da a ƙarfafa matasa domin gina ƙasa

Ranar matasa ta duniya: Mahdi ta yi kira da a ƙarfafa matasa domin gina ƙasa

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Wata mai fafutukar kare muradun matasa, Halima Ahmed Mahdi, ta yi kira ga gwamnatoci, iyaye, al’umma da sauran masu ruwa da tsaki da su ƙarfafa matasa tare da samar musu da damammaki domin su taka rawar gani wajen ci gaban ƙasa. Mahdi ta yi wannan kiran ne a cikin saƙonta na bikin Ranar Matasa ta Duniya ta 2026, inda ta bayyana matasa a matsayin wani muhimmin ɓangare na al’umma da ke da kuzari, buri da kuma damar jagorantar ci gaba. Ta ce matasa da dama na neman ilimi da koyon sana’o’i, yayin da wasu ke…
Read More
AGILE ta yaye ɗalibai ‘yan mata 1,868 a fannin ilimi a Zamfara

AGILE ta yaye ɗalibai ‘yan mata 1,868 a fannin ilimi a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Jimillar 'yan mata da matasa mata 1,868 sun kammala karatunsu daga rukunin farko na shirin ilimi na AGILE, Subcomponent 2.2C. An gudanar da bikin kammala karatun ne a Otal din Falala da ke Gusau yau Alhamis. Da take gabatar da jawabin maraba, mai kula da ayyukan AGILE na Zamfara Hajiya Sa'adatu Abdu Gusau, ta bayyana taron a matsayin damammaki da mata suka samu. "An gudanar da shirin na tsawon watanni 10 a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar," in ji ta. Ta bayyana cewa shirin ya haɗa ilimin karatu da lissafi tare da dabarun rayuwa,…
Read More
NVMA ta yaba wa Gwamna Lawal kan aiwatar da ƙarin albashin CONMESS ga likitocin dabbobi a Zamfara

NVMA ta yaba wa Gwamna Lawal kan aiwatar da ƙarin albashin CONMESS ga likitocin dabbobi a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Ƙungiyar likitocin dabbobi ta Najeriya, NVMA, reshen Jihar Zamfara ta yaba wa Gwamna Dr. Dauda Lawal saboda amincewa da aiwatar da sabon tsarin albashin likitanci mai haɗaka, CONMESS, ga likitocin dabbobi a jihar. Shugaban ƙungiyar, Dr. Mukhtar Salihu Anka, PhD, ya sanar da hakan ga 'yan jarida a Gusau yau Alhamis. Dr. Anka ya bayyana matakin a matsayin wani muhimmi ga aikin likitocin dabbobi a Zamfara, yana mai jaddada matakin da wata jajircewar gwamnati ga walwalar ma'aikata, ƙwarewa da kuma ci gaban fannin dabbobi. A cewarsa, aiwatar da sabon tsarin albashin ya magance damuwar da…
Read More

Lambar yabon Blueprint za ta ƙarfafa ayyukanmu na ci-gaba a Jigawa, inji Gwamna Namadi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Gwamna Umar Namadi na Jihar Jigawa ya karɓi lambar yabo ta Jaridar Blueprint ta 2025, ta gwarzon gwamna da ya yi fice a harkar Horon Kasafi da Ci-gaban Noma, yana mai bayyana hakan a matsayin ƙarfafa gwiwa ga ƙoƙarinsu na sarrafa dukiyar al'umma bisa kyakkyawan tsari da ci-gaban harkar noma. Gwamnan ya bayyana haka ne a wata takarda da ke ɗauke da sanya hannun Babban Sakatarensa na Musamman, Adamu M. Garun-Gabas mai kwanan wata 5 ga Agusta, 2026, yayin amsa saƙon jaridar kan sanar da shi a matsayin wanda ya samu kyautar. Namadi ya…
Read More
Yadda garin Lokoja ya zama babban birnin Nijeriya kafin Legas da Abuja

Yadda garin Lokoja ya zama babban birnin Nijeriya kafin Legas da Abuja

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Blueprint Manhaja na ci gaba da kawo wa masu karatu shafinsa na tarihi domin waiwayar muhimman abubuwan da suka taka rawa wajen gina tarihin Nijeriya, musamman waɗanda ba kasafai ake ba su kulawar da ta dace ba. A wannan makon, mun duba tarihin garin Lokoja, birnin da ya kasance cibiyar mulkin Turawan Birtaniya a farkon mulkin mallaka. Duk da cewa Legas ce aka fi sani a matsayin tsohon babban birnin Nijeriya, tarihi ya nuna cewa kafin hakan, Lokoja ce ta kasance cibiyar gudanar da harkokin gwamnatin Turawa a yankin da daga bisani ya zama Nijeriya. Ta…
Read More
Illar ƙazantar wurin kiwo ga lafiyar dabbobi

Illar ƙazantar wurin kiwo ga lafiyar dabbobi

Tare da BILKISU YUSUF ALI, Ph’D Gabatarwa: Tsaftar muhalli na da matuƙar muhimmanci wajen tabbatar da lafiyar dabbobi da haɓaka yawan amfanin kiwo. ƙazantar wurin kiwo na haifar da taruwar ƙwayoyin cuta da ƙwari da gurɓataccen ruwa, waɗanda ke haddasa cututtuka da rage ƙarfin dabbobi da ingancinsu. Duk lokacin da aka bar wurin kiwo da ƙazanta ba tare da kula ba to tabbas waɗannan matsalolin ne za su faru.  1. Yaɗuwar cututtukan ƙwayoyin cuta Taruwar kashin dabbobi da fitsari na samar da muhalli mai kyau ga ƙwayoyin cuta irin su Salmonella, Escherichia coli (E. coli) da Clostridium. Waɗannan ƙwayoyin cuta…
Read More