14
Aug
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An halaka mutane biyu sannan an yi garkuwa da wasu guda shida a Unguwar Aminu da ke Gundumar Kandarawa ta Ƙaramar Hukumar Bakori a Jihar Katsina. Haka kuma, wasu mazauna su huɗu sun samu raunukan harbin bindiga yayin harin, wanda ya auku a ranar Talata da dare, kamar yadda wani rahoton Daily Trust ya bayyana. Jaridar ta ce waɗanda aka halaka sune Ibrahim Sama'ila da Mashakuru Isa, inda tuni aka yi musu jana'iza a ranar Laraba kamar yadda addinin Musulunci ya tanada. Waɗanda aka sace a ɗaya gefen sun haɗa da maza uku da…
