14
Aug
Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rikicin da ya daɗe tsakanin ƙungiyar ISWAP da Boko Haram na ci gaba da sauya yanayin tsaro a yankin Arewa maso Gabashin Nijeriya. ƙungiyoyin biyu na fafatawa mai zafi domin mallakar yankuna, samun tasiri da albarkatu. Sabon artabu da aka ruwaito a ranar Juma’a, 7 ga Agusta, ya sake jawo hankali kan mummunan rikicin da ke tsakanin ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya, bayan rahotannin cewa mayaƙan ISWAP sun kai wani samame kan Bok Haram a yankin Bula Murge, cikin ƙaramar Hukumar Bama ta Jihar Borno, inda aka ce an kashe wasu manyan kwamandojin Boko Haram.…
