Labarai

Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Kwamishina ya yabi malaman tsangaya kan goyon bayan Inuwa da Jamilu gwamna a 2027

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Kwamishinan ƙananan hukumomi na Jihar Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya yaba wa malaman tsangaya na jihar bisa goyon bayan da suka bayyana wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya da ɗan takarar gwamnan jihar na jam’iyyar APC, Dakta Jamilu Isiyaku Gwamna a zaɓen 2027. Kwamishinan ya bayyana hakan ne a zantawarsa da manema labarai jim kaɗan bayan kammala wani babban taro da ƙungiyar malaman tsangaya ta jihar ta gudanar, inda malaman suka bayyana aniyarsu ta mara wa Dakta Jamilu Gwamna baya tare da tabbatar masa da ƙuri’u 150,000 a zaɓen 2027. Ya ce matakin malaman na…
Read More

Ma’aikatar kuɗi ta ɗora wa NNPCL laifin ɓatan bayanai yayin da majalisa ke binciken aron Dala 3bn da kuɗaɗen NLNG

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Ma'aikatar Kuɗi ta Tarayya ta ɗora wa Babban Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL) laifi bisa rashin gabatar da rahotannin bayanan da ake buƙata don warware tambayoyin kuɗaɗe da aka yi a rahoton shirin tabbatar da gaskiya da adalci kan kuɗaɗen masana'antun fitarwa (NEITI) na mai da gas na 2021 zuwa 2023. Babban Sakataren ma'aikatar, Raymond Omachi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis yayin bayyana a gaban kwamitin binciken kuɗaɗen al'umma na Majalisar Dattawa, inda yake amsa tambayoyi kan rashin fahimtar haƙiƙanin yadda aka sarrafa wasu kuɗaɗe daga rahoton NEITI. Daga cikin ababen…
Read More
Osun 2026: INEC ta fara rarraba kayan zaɓe masu muhimmanci

Osun 2026: INEC ta fara rarraba kayan zaɓe masu muhimmanci

Daga USMAN KAROFI Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC) ta fara rarraba muhimman kayan zaɓe zuwa ƙananan hukumomi 30 na Jihar Osun, gabanin zaɓen gwamnan jihar da aka shirya gudanarwa ranar Asabar, 15 ga Agusta 2026. Kwamishinan INEC mai kula da zaɓen Osun, Kunle Ajayi, ya bayyana cewa ana gudanar da rabon kayan ne daga ofishin Babban Bankin Najeriya (CBN) da ke Osogbo, babban birnin jihar. Ajayi ya ce an samu jinkirin rarraba kayan zaɓen ne sakamakon jinkirin isowar sabbin takardun kaɗa ƙuri’a da sauran kayan zaɓe daga Abuja. Ya bayyana cewa an sake buga takardun ne bayan…
Read More

NAHCON ta amince da kamfanoni biyar don jigilar hajjin 2027

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Jigilar Alhazan Nijeriya NAHCON, ta amince da kamfanonin jiragen sama guda biyar da za su gudanar da jigilar mahajjatan ƙasar yayin harkokin aikin Hajjin shekarar 2027. NAHCON ta sanar da haka ne wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis. Ta ce, kamfanonin da aka amince da su sun haɗa da Air Peace Limited, Flynas, Max Air Limited, Saudi Air da UMZA Aviation Services Limited. A cewarta, an zaɓi kamfanonin ne bayan tantance su da kwamitin tantance kamfanonin jiragen sama ya gudanar, bisa la’akari da ƙa’idojin tsaro, ƙarfin matakin gudanar da aiki da…
Read More
Chadi za ta bai wa ƙasashen Afirka izinin shiga ƙasar babu biza

Chadi za ta bai wa ƙasashen Afirka izinin shiga ƙasar babu biza

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Jamhuriyar Chadi ta sanar da cewa daga 1 ga Janairu, 2027, ’yan ƙasa daga dukkan ƙasashen Afirka za su samu damar shiga ƙasar ba tare da neman takardar izinin shiga ƙasa, wato biza, ba. Shugaban ƙasar Chadi, Mahamat Idriss Deby, ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin ƙasar na ƙarfafa haɗin kan Afirka da kuma sauƙaƙa zirga-zirgar mutane da kayayyaki tsakanin ƙasashen nahiyar. Deby ya bayyana cewa cire takunkumin biza zai taimaka wajen ƙarfafa alaƙa tsakanin ƙasashen Afirka, tare da sauƙaƙa tafiye-tafiye daga wata ƙasa zuwa wata. A cewarsa, wannan manufa ta nuna yadda Chadi ke…
Read More
Karramawar Blueprint ta ƙara mana ƙaimin taka-tsantsan da kuɗin al’umma – Gwamna Namadi

Karramawar Blueprint ta ƙara mana ƙaimin taka-tsantsan da kuɗin al’umma – Gwamna Namadi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya karɓi lambar yabo ta Blueprint Newspapers ta shekarar 2025 kan kula da kuɗaɗen gwamnati da sauye-sauyen harkar noma, yana mai cewa karramawar za ta ƙara wa gwamnatinsa ƙwarin gwiwar yin taka-tsantsan da ci gaba da yin amfani da albarkatun jama’a cikin tsanaki da bunƙasa harkar noma. Gwamnan Namadi ya bayyana hakan ne a wata wasiƙa mai kwanan watan 5 ga Agusta, 2026, wacce Babban Sakataren Ofishinsa na Musamman, Adamu M. Garun-Gabas, ya sanya wa hannu, a matsayin martani ga wasiƙun da Blueprint Newspapers Limited ta aiko masa…
Read More
Zaɓen Osun: Sufeto Janar ya tura DIG Ishyaku domin jagorantar tsaro

Zaɓen Osun: Sufeto Janar ya tura DIG Ishyaku domin jagorantar tsaro

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Sufeto Janar na ’Yan Sandan Nijeriya, IGP Olatunji Disu, ya tura Muƙaddashin Babban Sufeto Janar, DIG Ishyaku Mohammed, zuwa Jihar Osun, domin jagorantar daidaita ayyukan tsaro yayin zaɓen gwamnan njihar da za a gudanar ranar Asabar, 15 ga Agusta, 2026. A cikin wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya (FPRO), CSP Anietie Iniedu, ya fitar a Abuja, ya ce tura babban jami’in na daga cikin matakan da rundunar ta ɗauka domin tabbatar da gudanar da zaɓe cikin zaman lafiya, tsaro da sahihanci a faɗin jihar. Ya ce, DIG Ishyaku Mohammed…
Read More
Na haihu a hanyar tsere wa ’yan bindiga, inji ‘yar gudun hijira a Sakkwato

Na haihu a hanyar tsere wa ’yan bindiga, inji ‘yar gudun hijira a Sakkwato

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD  Wata mata da ’yan bindiga suka tilasta wa barin gidanta a ƙaramar Hukumar Tambuwal ta Jihar Sakkwato, ta bayyana irin mummunan halin da ta shiga, inda ta ce ta haifi jaririnta a kan hanya yayin da take tserewa daga hare-haren ’yan bindiga da suka mamaye garinsu tare da ƙona gidaje. Matar ta bayyana haka ne cikin harshen Hausa yayin wata tattaunawa da Iconic FM, inda ta ce hare-haren sun lalata dukiyoyin iyalansu, har ta kai ga ba ta da isasshen kayan da za ta yi amfani da su wajen ɗaukar jaririn da ta haifa. A cewarta,…
Read More
Akwai buƙatar tuntuɓar manoma a shirin ba da tallafin taki na gwamnatin Kano— Maikuɗi Kadawa

Akwai buƙatar tuntuɓar manoma a shirin ba da tallafin taki na gwamnatin Kano— Maikuɗi Kadawa

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano An shawarci gwamnatin Kano da sauran gwamnatoci har zuwa matakin tarayya da su riƙa tuntuɓar manoma na haƙiƙa kafin su raba tallafin noma, musamman takin zamani da sauran kayan aikin gona kamar taraktoci da makamantansu. An bayyana cewa akwai buƙatar gwamnatoci su riƙa tuntuɓar ƙungiyoyin manoma na gaskiya waɗanda aka tabbatar da cewa manoma ne, domin samun nasarar duk wani shiri na tallafin noma da kuma cimma manufofin gwamnati na bunƙasa tattalin arziki, samar da abinci da ci gaban jihohi da Nijeriya baki ɗaya. Wannan shawara ta fito ne daga bakin shugaban ƙungiyar Masu Sayar…
Read More
Muna taimaka wa masu Umrah wajen samun ƙarin arziƙi — Baba Gambo

Muna taimaka wa masu Umrah wajen samun ƙarin arziƙi — Baba Gambo

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Shugaban UBJ Group, Uzairu Baba Gambo ESK, ya bayyana cewa an kafa kamfanin ne domin taimakawa wajen bunƙasa tattalin arzikin al’ummar Nijeriya, musamman masu gudanar da harkokin Makka da Umrah. Uzairu Baba ya ce kamfanin na daga cikin masu gudanar da harkokin da suka samu amincewar hukumomin da abin ya shafa wajen taimaka wa maniyyata da masu Umrah wajen samun kayayyakin da suke buƙata a Makka, Madina da sauran wurare a ƙasar Saudiyya, da kuma a Nijeriya. Ya ce mutanen da suka yi hulɗa da kamfanin na iya samun riba mai yawa tare da samun…
Read More