Labarai

Kolmani: Jami’ar NEU Gombe ta rage kuɗin karatun kwasa-kwasai shida da kashi 50

Kolmani: Jami’ar NEU Gombe ta rage kuɗin karatun kwasa-kwasai shida da kashi 50

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Jami’ar North-Eastern University, Gombe (NEU Gombe), ta sanar da tallafin karatu na kashi 50 cikin 100 ga ɗaliban da za su yi karatun digiri a kwasa-kwasai shida na kimiyya, a wani shiri da ta ce zai taimaka wajen shirya matasa domin cin moriyar sabbin damarmakin da ake samu a fannin man fetur da iskar gas. Shugaban jami’ar kuma wanda ya kafa ta, Dakta Sani Jauro (Dan Lawan na Gombe), ne ya bayyana hakan yayin bikin yaye ɗaliban Pen Resources Academy na shekarar 2026 da aka gudanar a Gombe. Ya ce shirin tallafin na daga cikin…
Read More
Sarki Sanusi ya mara wa matakan sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu baya

Sarki Sanusi ya mara wa matakan sauye-sauyen tattalin arzikin Tinubu baya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana goyon bayansa ga sauye-sauyen tattalin arziki da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa tare da yaba wa Babban Bankin Nijeriya (CBN) kan matakan da ya ɗauka, domin daidaita tattalin arzikin ƙasar. Sarkin, wanda tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya ne, ya ce, ƙasar ta kauce wa mummunar barazanar durƙushewar tattalin arziki sakamakon matakan da aka ɗauka na rage yawaitar kuɗaɗen da suke yawo a kasuwa, daƙile hauhawar farashi da kuma daidaita darajar Naira. A yayin da yake magana kan halin da tattalin arzikin ƙasar ke ciki, Sanusi…
Read More
Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin inganta tsarin lantarki

Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin inganta tsarin lantarki

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada aniyarta ta tabbatar da samar da ingantacciyar wutar lantarki ga 'yan Nijeriya, inda ta bayyana shirinta na zuba sabon jari domin ƙarfafa tsarin Grid na Wutar Lantarki na ƙasa, da nufin kawo ƙarshen yawaitar rushewar tsarin da kuma matsalar sauyin ƙarfin lantarki. Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe, ya bayyana cewa ma'aikatar ta fara ɗaukar matakan da suka wuce gyare-gyaren gaggawa, inda ta mayar da hankali kan sake fasalin tsarin wutar lantarki gaba ɗaya. A cewarsa, tabbatar da daidaiton grid shi ne ginshiƙin da zai ba da damar cika duk wasu alkawuran…
Read More
Sauye-sauyenmu sun fara haifar da ɗa mai ido – Martanin Tinubu ga Atiku

Sauye-sauyenmu sun fara haifar da ɗa mai ido – Martanin Tinubu ga Atiku

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Fadar Shugaban ƙasa ta mayar da martani mai zafi ga tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, inda ta kare manufofin sauye-sauyen tattalin arzikin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, tana mai cewa sukar da Atiku ke yi ta ginu ne kan tsofaffin bayanai da ba sa nuna ainihin halin da tattalin arzikin Nijeriya ke ciki a halin yanzu. Mai Bai Wa Shugaban ƙasa Shawara Kan Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa mai taken “Gaskiya Ce, Ba Tsoratarwa Ba: Fadar Shugaban ƙasa Ta Yi Martani Dalla-dalla Kan Sukan Atiku Game da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin…
Read More
DMO ta fara sayar da takardun zuba jari na Gwamnatin Tarayya kan N1,000

DMO ta fara sayar da takardun zuba jari na Gwamnatin Tarayya kan N1,000

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Hukumar Kula da Basussukan Gwamnati (DMO) ta sanar da fara sayar da sabbin Takardun Bashin Ajiya na Gwamnatin Tarayya, wato FGN Savings Bonds, guda biyu, inda aka ƙayyade mafi ƙarancin farashin kowace guda kan Naira 1,000 domin bai wa talakawa da masu ƙaramin jari damar saka hannun jari. A cikin sanarwar da hukumar ta fitar a madadin Gwamnatin Tarayya, ta bayyana cewa takardar bashi ta farko tana da wa'adin shekara biyu, wadda za ta ƙare ranar 12 ga Agustan 2028, tare da ribar kashi 13.96 cikin 100 a duk shekara. Sannan takardar bashi ta biyu tana…
Read More

Gwamnatin Kano ta goyi bayan Gwamnatin Tarayya kan hana wasu mallakar rukunin cibiyar kula da gandun daji

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cikakken goyon bayanta ga Gwamnatin Tarayya wajen kare wani ɓangare na Sashen Cibiyar kula da Harkokin Gandun Daji (APCU) da ke yankin Janbulo a Ƙaramar Hukumar Gwale ta jihar daga yunƙurin mayar da shi mallakar masu zaman kansu. Kwamishinan Albarkatun Ruwa, Muhalli da Sauyin Yanayi, Dakta Ɗahir M. Hashim ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a Kano, ranar Juma’a. Ya ce, gwamnatin jihar na goyon bayan Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya, hukumomin NAGGW, NESREA da APCU wajen kare wannan muhimmiyar cibiyar muhalli ta ƙasa daga masu zaman kansu. Dakta Hashim…
Read More
Mutuwa ce kaɗai za ta kawo ƙarshen saɓanin Obasanjo da Atiku – Shehu Sani

Mutuwa ce kaɗai za ta kawo ƙarshen saɓanin Obasanjo da Atiku – Shehu Sani

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Kwamred Shehu Sani, ya bayyana cewa, rikicin siyasa da ya daɗe yana ci gaba da taɓarɓarewa tsakanin tsohon Shugaban Nijeriya, Cif Olusegun Obasanjo, da tsohon mataimakinsa, Alhaji Atiku Abubakar, na iya ci gaba wanzuwa har sai bayan ransu. Sanata Sani ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na ɗ, yayin da yake tsokaci kan sabon musayar yawu tsakanin tsoffin abokan tafiyar siyasar, waɗanda dangantakarsu ta yi tsami sama da shekaru 20 da suka gabata. A cewarsa, rikicin ya daɗe matuƙa har ya ratsa tsararraki, domin ya…
Read More
Yadda ake zargin Sylva da tattara kuɗaɗen shirin hamɓarar da Tinubu

Yadda ake zargin Sylva da tattara kuɗaɗen shirin hamɓarar da Tinubu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Sabbin takardun bincike na sirri da aka samu sun bayyana yadda ake zargin tsohon gwamnan Jihar Bayelsa, Timipre Sylva, da tattara kuɗaɗen da aka ce an yi amfani da su wajen ɗaukar nauyin shirin juyin mulkin da bai yi nasara ba kan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bara. Wani rahoton da jaridar PremiumTimes ta wallafa ya ce, rahoton ya samo asali ne daga dubban takardun bincike sama da 7,400 da hukumomin tsaro suka tattara domin gurfanar da waɗanda ake zargi da hannu a yunƙurin juyin mulkin. Wasu daga cikin waɗanda ake zargin na fuskantar shari'a…
Read More
CBN ya fitar da muhimman matakai biyar don haɓaka fasahar kuɗi

CBN ya fitar da muhimman matakai biyar don haɓaka fasahar kuɗi

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa, mataki na gaba wajen bunƙasa fasahar kuɗi, wato Fintech, a ƙasar dole ne ya ta'allaƙa kan manyan manufofi guda biyar domin tabbatar da ci gaba mai ɗorewa a wannan fanni. Gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Yemi Cardoso, ya bayyana hakan cikin saƙon fatan alheri da aka karanta a madadinsa yayin taron tattaunawa karo na uku kan fasahar kuɗi da bunƙasa harkokin kuɗi na shekarar 2026, wanda Business Journal ta shirya a Legas. Cardoso, wanda Darakta mai kula da sa ido kan tsarin biyan kuɗi, Dakta Rakiya Yusuf, ta wakilta, ya…
Read More
Atiku ga Obasanjo: Na zaɓi Nijeriya da dimokuraɗiyya fiye da biyayya ga wani

Atiku ga Obasanjo: Na zaɓi Nijeriya da dimokuraɗiyya fiye da biyayya ga wani

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya mayar da martani ga tsohon Shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, inda ya ce bai taɓa yin nadamar adawa da yunƙurin wa'adin mulki na uku ba, yana mai jaddada cewa ya zaɓi kare Nijeriya da dimokuraɗiyya fiye da biyayya ga mutum. Atiku, wanda shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC a zaɓen 2027, ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar. Martanin na Atiku ya biyo bayan kalaman da Obasanjo ya yi, inda ya…
Read More