08
Aug
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Iyalan Marigayi Malam Aliyu S. Abubakar Tunga (Baba A.T.) sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Kebbi da ta biya kuɗaɗen kwangilar da ake bin marigayin domin su samu damar biyan bashin da ya bari. Da yake zantawa da wakilin Blueprint Manhaja a ranar Litinin, Malam Aminu Aliyu Abubakar Tunga, wanda ya yi magana a madadin iyalan marigayin, ya bayyana cewa shekaru shida kenan da rasuwar mahaifinsu, amma har yanzu ba su samu damar biyan bashin da ya bari ba saboda gwamnatin jihar ba ta biya kuɗaɗen kwangilar da ake binsa ba. A cewarsa, marigayin na…
