Labarai

Wike ya ƙaƙaba takunkumi kan ayyukan ‘yan acaɓa da masu adaidaita sahu a Abuja

Wike ya ƙaƙaba takunkumi kan ayyukan ‘yan acaɓa da masu adaidaita sahu a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya ce gwamnatin birnin ta kammala shirye-shiryen sake fasalin ayyukan babura da adaidaita sahu (Keke Napep) a Abuja, domin magance matsalolin tsaro da kuma inganta doka da oda. Wike ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin ganawarsa ta wata-wata da manema labarai a Abuja. Ya ce ayyukan babura da adaidaita sahu sun zama barazana ga tsaro a babban birnin tarayya, saboda haka ya zama dole a taƙaita zirga-zirgarsu zuwa wuraren da gwamnati za ta ware musu. Ministan ya bayyana ayyukansu a matsayin abin da ke kawo cikas…
Read More
Maigwari II ya yaba wa Tinubu, ya nemi a faɗaɗa aikin sake gina hanyar Kaduna-Birnin Gwari

Maigwari II ya yaba wa Tinubu, ya nemi a faɗaɗa aikin sake gina hanyar Kaduna-Birnin Gwari

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Birnin Gwari, Alhaji Zubairu Maigwari II, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa cika alƙawarin da ya ɗauka na sake gina hanyar tarayya ta Kaduna (Mando) zuwa Birnin Gwari mai tsawon kilomita 122, tare da roƙon Gwamnatin Tarayya ta faɗaɗa aikin zuwa sauran sassan hanyar da suka fi lalacewa. Sarkin ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin ƙaddamar da aikin sake gina hanyar, inda ya bayyana aikin a matsayin wani gagarumin ci gaba ga al'ummar masarautarsa. Ya ce fara aikin ya cika burin da al'ummar yankin suka daɗe suna fata, tare da…
Read More
Bwari ya ƙaryata zargin Obasanjo kan Na’Abba, ya tuna rikicin tsige Shugaban ƙasa

Bwari ya ƙaryata zargin Obasanjo kan Na’Abba, ya tuna rikicin tsige Shugaban ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Babban Mai Tsawatarwa (Chief Whip) na Majalisar Wakilai, Abubakar Bwari, ya ƙalubalanci ikirarin da tsohon Shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya yi kwanan nan kan marigayi tsohon Kakakin Majalisar Wakilai, Ghali Na’Abba, yana mai cewa bayanin Obasanjo game da yunƙurin tsige shi daga mulki a zamanin Jamhuriya ta Huɗu ba daidai ba ne, kuma bai yi wa marigayin adalci ba. Bwari, wanda ya riƙe muƙamin Chief Whip tsakanin shekarar 1999 zuwa 2007, ya bayyana hakan ne a cikin wata doguwar sanarwa da ya fitar ranar Litinin mai taken "Gyara Tarihi: Martani cikin Ladabi ga…
Read More
Gwamna Yusuf ya jagoranci ɗaurin auren gata na zawarawa da ’yan mata 1,500 a Kano

Gwamna Yusuf ya jagoranci ɗaurin auren gata na zawarawa da ’yan mata 1,500 a Kano

Daga RABI'U SANUSI a Kano Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci ɗaurin auren gata na zawarawa da ’yan mata 1,500, ƙarƙashin shirin gwamnatin jihar da hukumar hisbah ta Kano ta gudanar. Gwamnan ya bayyana shirin a matsayin wani gagarumin tsari na jin ƙai da tallafa wa al’umma, wanda ke da nufin dawo da fata, ƙarfafa zaman iyali da kuma inganta kyawawan ɗabi’u a cikin al’umma. Ya ce shirin ya nuna ƙudirin gwamnatinsa na rage wa marasa galihu nauyin da ke tattare da aure, tare da samar da damar kafa iyali cikin mutunci, bisa koyarwar addinin Musulunci da…
Read More

Majalisar Wakilai ta bankaɗo yadda aka naɗa Tinubu, Akume, Wike da wasu a matsayin amintattun hukumar bogi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Kwamitin wucin-gadi kan binciken badaƙalar hukumar bogi (PFIPC) na Majalisar Wakilai, ya bayyana cewa wasu manyan jami'an gwamnati sun kasance amintattun hukumar gudanarwarta duk da tambayoyi akan halascinta da dokance. Shugaban kwamitin, Yusuf Gagdi ne ya bayyana hakan a wata hirar bincike a ranar Alhamis, inda 'yan majalisa suka ƙalubalanci Shugaban Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Ƙasa (FRSC), Shehu Mohammed kan amincewa da bayar da alunan lamba na ababen hawa guda bakwai da aka danganta su da hukumar. Gagdi ya ce, waɗanda aka zayyano a matsayin amintattun sun haɗa da Shugaba Bola Tinubu, Sakataren Gwamnatin…
Read More
LCDA ta Gombe ta Kudu ta ƙulla ƙawance da RUWASA don kawo ƙarshen matsalar ruwa

LCDA ta Gombe ta Kudu ta ƙulla ƙawance da RUWASA don kawo ƙarshen matsalar ruwa

Daga ABUBAKAR A BOLARI Gombe Shugabannin gundunar ci gaban yankin Gombe South Local Council Development Area (LCDA) da ƙaramar hukumar Gombe sun ƙulla sabuwar alaƙar haɗin gwiwa da hukumar samar da Ruwa da Tsaftar Muhalli a karkara (RUWASA), domin faɗaɗa ayyukan samar da tsaftataccen ruwan sha da inganta tsaftar muhalli a yankunan. Sabuwar haɗin gwiwar ta samu tabbaci ne yayin da tawagar RUWASA, tare da mai kula da shirin WASH na ƙaramar hukumar Gombe, suka kai ziyarar ban girma ga shugaban Gombe South LCDA, Hon. Auwal Jauro Bappi, da kuma Shugaban ƙaramar hukumar Gombe Farfesa Bappah Garkuwa. Tawagar ta bayyana…
Read More
Hukumar KASSAROTA ta cigaba da ziyarar ofishoshin ta a Katsina

Hukumar KASSAROTA ta cigaba da ziyarar ofishoshin ta a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Hukumar kula da tsaro da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar Katsina, KASSAROTA, ta ci gaba da rangadin duba ayyukan hukumar a ƙananan hukumomin shiyyar Daura, inda ta kai ziyara ƙananan hukumomin Dutsi da Ingawa. Tawagar, wadda shugaban hukumar gudanarwar KASSAROTA, tsohon mataimakin Sufeto-Janar na ’yan sanda, AIG Danlami Yar’adua ya jagoranta, ta gana da hakimai, shugabannin ƙananan hukumomi, jami’an ’yan sanda masu kula da sassan, DPOs, da jami’an hukumar tsaro da kare fararen hula ta Najeriya, NSCDC, a ƙananan hukumomin. Da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki,a ƙananan hukumomin,shugaban hukumar ya bayyana cewa manufar…
Read More
Kotun Tarayya a Gusau ta ɗage ƙarar zaɓen fidda gwani na majalisar dattawa a Zamfara

Kotun Tarayya a Gusau ta ɗage ƙarar zaɓen fidda gwani na majalisar dattawa a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Kotun tarayya mai zaman ta a Gusau a yau Juma’a, ta ɗaga ƙarar da Dr. Sani Abdullahi Shinkafi ya shigar, yana ƙalubalantar zaɓen fidda gwani na majalisar dattawa na Jam’iyyar APC a Zamfara ta Arewa zuwa 31 ga Agusta, 2026 domin yanke hukunci na ƙarshe. Lauyan mai ƙara, Barr. Bello Galadi, ne ya bayyana hakan ga manema labarai jim kaɗan bayan kammala zaman kotun. A cewarsa, Dr. Shinkafi ya shigar da ƙarar ne a kan hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC, Jam’iyyar APC, da kuma sanata mai wakiltar Zamfara ta Arewa a yanzu,…
Read More
Gwamna Raɗɗa ya bude babban asibiti na farko a ƙaramar hukumar Zango

Gwamna Raɗɗa ya bude babban asibiti na farko a ƙaramar hukumar Zango

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa,ya ƙaddamar da sabon babban asibiti (General Hospital) na Zango, wanda shi ne babban asibiti na farko da aka taɓa kafawa a ƙaramar hukumar. A jawabin sa, kwamishinan lafiya na Jihar Katsina, Hon. Musa Adamu Funtua, ya bayyana aikin a matsayin wani babban ci gaba a ƙoƙarin gwamnatin jihar na bunƙasa tsarin kiwon lafiya da kuma inganta samar da ayyukan kiwon lafiya ga al’umma. Gwamnan ya bayyana cewa, an tanadi asibitin da ingantattun kayan aiki na zamani domin samar da ayyukan jinya da tiyata masu inganci, lamarin da zai…
Read More

Atiku ya tayar da ƙura bisa shigar wani kuɗi asusun bankinsa

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar ADC, Atiku Abubakar, ya bayyana damuwa kan wasu kuɗaɗe da aka tura cikin ɗaya daga cikin asusunsa na sirri ba tare da saninsa ko amincewarsa ba. A wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Phrank Shaibu, ya fitar a ranar Juma'a, an ce wani mutum da ba a san ko wanene ba ne ya tura kuɗin tare da rubuta cewa: "Contribution Electioneering Campaign." Atiku ya ce ba shi ko tawagarsa suka nemi ko suka amince da wannan kuɗi ba, yana mai cewa abin ya tayar da…
Read More