07
Aug
Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Fitaccen mawakin Nijeriya, David Adeleke da aka fisani da Davido da tsohon hadimin marigayi tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari kan lamuran kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad, sun tayar da hazo a Soshiyal Mediya inda suka yi musayar kalamai masu zafi a shafin X. Wannan al'amari ya janyo hankalin jama’a musamman ganin yadda ba a saba ganin irin haka ba tsakanin mawaƙi ɗan kudu da ɗan siyasa daga arewacin Nijeriya. Al'amarin ya samo asali ne a lokacin da aka ruwaito Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta'annati EFCC, ta sanya wa asusun gwamnatin Jihar…
