Labarai

Ana ci gaba da addu’a da tunawa da Malam Adamu Direba shekaru 11 bayan rasuwarsa

Ana ci gaba da addu’a da tunawa da Malam Adamu Direba shekaru 11 bayan rasuwarsa

Daga MUHAMMAD MUJITABA a Kano An ci gaba da gudanar da addu'o'i da tunawa da marigayi Malam Adamu, tsohon direba da aka bayyana a matsayin mutum mai kyakkyawar mu'amala, zaman lafiya da kuma bayar da gudunmawa ga al'umma, shekaru 11 bayan rasuwarsa. Iyalan marigayin, 'yan uwa da abokan arzikinsa sun ce har yanzu ba su manta da shi ba, kuma suna ci gaba da yi masa addu'a tare da tuna kyawawan halayensa. An haifi Malam Adamu a ranar 2 ga Fabrairu, 1920, sannan ya rasu a ranar 17 ga Janairu, 2015. Da yake jawabi a wajen taron addu'ar, shugaban masu…
Read More

‘Yan takara 334 sun wakilci ƙasashe a musabaƙar ƙasa-da-ƙasa ta Sarki Abdulaziz a Makkah

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja An fara gudanar da karatun Musabƙar Al-Ƙur'ani Mai Girma na Sarki Abdulaziz na Ƙasa-da-ƙasa karo na 46 a Makkah, Saudiyya, inda aka samu jimillar 'yan takara 334 da suka ƙunshi maza da mata daga ƙasashe 133 da suka halarta. Rahotanni sun bayyana cewa, a ranar Alhamis aka fara gasar a ƙarƙashin jagorancin Masallatai biyu Masu Alfarma na Sarki Salman, wadda Ma'aikatar Harkokin Addinin, Kira da Kariya ta ƙasar ta shirya. A ranar 6 ga watan Rabi Al-Awwal (19 ga Agusta) ne za a kammala gasar, wadda ta samu adadin 'yan takara mafi yawa tun…
Read More
Rashin koyar da yara sana’o’i na daga cikin abubuwan da ke gurɓata tarbiyyar matasa — ABM

Rashin koyar da yara sana’o’i na daga cikin abubuwan da ke gurɓata tarbiyyar matasa — ABM

Daga MUHAMMAD MUJITABA a Kano Alhaji Abubakar Muhammad, wanda aka fi sani da ABM Uba, ya bayyana cewa rashin koyar da yara sana'o'in gargajiya da na zamani na daga cikin manyan abubuwan da ke haifar da gurɓacewar tarbiyyar matasa a yau. ABM, wanda fitaccen ɗan kasuwa ne a ƙungiyar masu sayar da motocin noma a Arewa, ya ce sana'o'i irin su ɗinki, kafinta, jima, saƙa, ƙira da sauran sana'o'in hannu sun kasance hanyoyin neman halal da iyaye ke amfani da su wajen rufa wa kansu asiri, amma yanzu an yi watsi da koyar da yara waɗannan sana'o'i. Ya ce idan…
Read More
Kaduna: ‘Yan sanda sun kama masu garkuwa 16, sun ƙwato bindigu da shanu 410 da aka sace

Kaduna: ‘Yan sanda sun kama masu garkuwa 16, sun ƙwato bindigu da shanu 410 da aka sace

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta ce ta kama mutane 16 da ake zargi da garkuwa da mutane tare da ƙwato bindigogi 10 na nau’o’i daban-daban a cikin makonni biyu da suka gabata. Kwamishinan ‘Yan Sandan jihar, Rabiu Muhammad, ne ya bayyana hakan a ranar Talata yayin da yake yi wa manema labarai bayani a Kaduna. Ya ce rundunar ta kuma kama wasu mutum uku da ake zargi da safarar makamai, da kuma mutum shida da ake zargi da kasancewa cikin wata ƙungiyar masu safarar kuɗaɗen bogi. A cewarsa, jami’an sun kuma ƙwato takardun…
Read More
Sarkin Musulmi ya musanta goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Sarkin Musulmi ya musanta goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Musulmi, Muhammad Sa'ad Abubakar III, ya musanta rahotannin da ke yawo cewa ya bayyana goyon bayansa ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin ya sake tsayawa takara a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Bashir Adefaka, ya fitar, an bayyana rahotannin a matsayin ƙarya da kuma masu yaudara, tare da jaddada cewa Sarkin Musulmin ba shi da wani ɗan takarar da yake marawa baya a zaɓen shugaban ƙasa na 2027. Sanarwar ta ce matsayinsa na jagoran addini da na gargajiya, kuma uba ga…
Read More
BUKSWA ta ƙulla yarjejeniya da WOFAN domin bunƙasa tattalin arzikin matan ma’aikatan BUK

BUKSWA ta ƙulla yarjejeniya da WOFAN domin bunƙasa tattalin arzikin matan ma’aikatan BUK

Daga RABIU SANUSI a Kano ƙungiyar Matan Ma'aikatan Jami'ar Bayero Kano (BUKSWA) ta sanar da fara haɗin gwiwa da ƙungiyar Women Farmers Advancement Network (WOFAN) domin inganta tattalin arziki da rayuwar mambobinta ta hanyar noma, sarrafa amfanin gona da sauran harkokin kasuwancin noma. An cimma wannan matsaya ne a wani taron dabaru da aka gudanar a hedikwatar WOFAN, inda shugabannin BUKSWA suka gana da wadda ta kafa WOFAN kuma Jakadiyar ƙasa da ƙasa, Hajiya Dakta Salamatu Garba, domin tattauna hanyoyin haɗin gwiwa a ƙarƙashin shirin Skills Improvement to Boost Livelihood and Nurture Growth (SIBLING) da ake aiwatarwa tare da Jami'ar…
Read More
Ambaliya ta hallaka jami’in tsaro da matashi a Yobe

Ambaliya ta hallaka jami’in tsaro da matashi a Yobe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutane biyu sun rasa rayukansu bayan ruwan sama mai ƙarfi ya haddasa ambaliya a wasu sassan birnin Damaturu, babban birnin Jihar Yobe. Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) ta tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Talata. An bayyana waɗanda suka rasu da suna Isa Haruna, mai shekara 38, jami'in tsaro da aka fi sani da Mallam Matari, da kuma Abba Kyari, mai shekara 18, wanda rahotanni suka ce ya nutse a yankin Pompomari. A cewar SEMA, ambaliyar ta afku ne a unguwannin Malari, Pompomari da…
Read More
NSCDC ta hukunta jami’an ta 79, ta kama mutane 18 kan lalata kayayyakin gwamnati

NSCDC ta hukunta jami’an ta 79, ta kama mutane 18 kan lalata kayayyakin gwamnati

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rundunar Tsaron Farin Kaya ta Nijeriya (NSCDC) ta hukunta jami'anta 79 bisa laifuka daban-daban, tare da kama mutane 18 da ake zargi da lalata bututun mai, barnata muhimman kayayyakin gwamnati da kuma safarar makamai ba bisa ƙa'ida ba. Babban Kwamandan NSCDC, Ahmed Audi, ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar rundunar da ke Abuja. Kakakin rundunar, Babawale Afolabi, ne ya wakilce shi. Audi ya ce an kammala hukuncin jami'ai 75, yayin da wasu huɗu ke ci gaba da fuskantar matakan ladabtarwa kan zarge-zarge daban-daban. Ya ce cikin…
Read More
Sarkin Machina ya kai ziyarar girmamawa ga Sarkin Agadez 

Sarkin Machina ya kai ziyarar girmamawa ga Sarkin Agadez 

Daga GAMBO ISA a Abuja Mai Martaba Sarkin Machina, Alhaji (Dr.) Bashir Albishir Bukar Machinama (OON, L'ONN), ya kai ziyarar girmamawa ga Sarkin Agadez (Sultan d'Aïr) da kuma Shugaban Hukumar Gudanarwar Birnin Agadez, Chef de Bataillon Assarid Almoustapa, Administrateur Délégué (AD), a Jamhuriyar Nijar. Ziyarar, wadda aka gudanar a ranar Laraba, 5 ga Agustan 2026, na da nufin ƙara ƙarfafa zumunci, haɗin kai da haɗin gwiwa tsakanin masarautun gargajiya, tare da bunƙasa dangantakar tarihi da ta daɗe tsakanin al'ummar Tarayyar Nijeriya da Jamhuriyar Nijar tun daga zamanin Daular Kanem-Borno. A yayin ziyarar, Mai Martaba Sarkin Machina ya jaddada muhimmancin ci…
Read More
Hukumar NELFUND tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ga matasa – Tinubu

Hukumar NELFUND tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ga matasa – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya yaba wa Hukumar Ba Da Lamunin Karatu ga ɗalibai ta Nijeriya (NELFUND), ya ce hukumar tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi. Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi Shugaban hukumar ta NELFUND, Mista Jim Oɓia, tare da Manajan Darakta/Babban Jami’in Gudanarwa na NELFUND, Mista Akintunde Sawyerr, a Abuja ranar Talata. A yayin ganawar, Tinubu ya yaba wa NELFUND bisa gagarumin cigaban da ta samu wajen faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ta hanyar nasarar aiwatar da Shirin Ba da Lamunin Karatu ga ɗalibai. Haka kuma, Shugaban…
Read More