Labarai

Hukumar NELFUND tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ga matasa – Tinubu

Hukumar NELFUND tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ga matasa – Tinubu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban ƙasa, Bola Tinubu, ya yaba wa Hukumar Ba Da Lamunin Karatu ga ɗalibai ta Nijeriya (NELFUND), ya ce hukumar tana faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi. Shugaban ya bayyana haka ne lokacin da ya karɓi Shugaban hukumar ta NELFUND, Mista Jim Oɓia, tare da Manajan Darakta/Babban Jami’in Gudanarwa na NELFUND, Mista Akintunde Sawyerr, a Abuja ranar Talata. A yayin ganawar, Tinubu ya yaba wa NELFUND bisa gagarumin cigaban da ta samu wajen faɗaɗa damar samun ilimi mai zurfi ta hanyar nasarar aiwatar da Shirin Ba da Lamunin Karatu ga ɗalibai. Haka kuma, Shugaban…
Read More
Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa bayan alamun girgizar ƙasa a Abuja

Gwamnatin Tarayya ta ɗauki matakin gaggawa bayan alamun girgizar ƙasa a Abuja

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnatin Tarayya ta umarci a ƙara ƙarfafa sa ido kan motsin ƙasa bayan wata ƙaramar girgizar ƙasa da ta girgiza wasu sassan Babban Birnin Tarayya – Abuja. Hukumar Binciken Yanayin ƙasa ta Nijeriya (NGSA) ta tabbatar da cewa an samu girgizar ne a ranar Talata, lamarin da ya sa gwamnati ta ƙara tsaurara bibiyar duk wani motsin ƙasa da ke kewaye da Abuja. Ministan Raya Ma'adinai, Dele Alake, ya umarci NGSA da ta riƙa bayar da rahoton duk wani ci gaban da ake samu kan yanayin girgizar ƙasa a kowane sa'a. A cikin wata…
Read More
Cikakken bayanin sabon albashin da sojojin Nijeriya za su riƙa karɓa

Cikakken bayanin sabon albashin da sojojin Nijeriya za su riƙa karɓa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da sabon tsarin albashi ga jami’an rundunonin sojin Nijeriya, inda aka ƙara musu albashi da tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da Gwamnatin Tarayya ta ce zai inganta walwala da ƙarfafa gwiwar jami’an tsaro. Sabon tsarin albashin zai fara aiki daga ranar 1 ga watan Satumba, kuma ana sa ran sama da jami’an soji 250,000 za su amfana da wannan ƙarin. Mai Bai Wa Shugaban ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ne ya sanar da amincewar cikin wata sanarwa da…
Read More
Majalisar Dokokin Katsina ta nemi daidaita kuɗin makarantu masu zaman kansu

Majalisar Dokokin Katsina ta nemi daidaita kuɗin makarantu masu zaman kansu

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina  Majalisar Dokoki a Jihar Katsina ta yi kira ga ɓangaren zartarwa na gwamnati da ta samar da tsarin da zai daidaita yadda makarantu masu zaman kansu da na al'umma ke gudanar da ayyukansu, musamman kan yawan kuɗin makaranta da kuma tsarin gudanarwarsu. Hakan ya biyo bayan   kudiri da ɗan majalisa mai wakiltar Katsina, Alhaji Aliyu Abubakar Albaba, ya gabatar, inda ya nuna damuwa kan yawan ƙarin kuɗin makaranta ba tare da ingantaccen tsari na sa ido ba. A zaman Majalisar da Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Nasir Yahaya Daura, ya jagoranta, an kuma buƙaci gwamnatin jihar…
Read More
Ana naɗa Jamilu Lamir a matsayin Sarkin Maganin Fagge a Kano

Ana naɗa Jamilu Lamir a matsayin Sarkin Maganin Fagge a Kano

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Sarkin Maganin Gargajiya na Jihar Kano, Dakta Rabilu Muhammad, ya naɗa Alhaji Jamilu Lamir Jibrin a matsayin sabon Sarkin Maganin ƙaramar Hukumar Fagge, bayan rasuwar mahaifinsa, marigayi Dakta Lamir. An gudanar da bikin naɗin ne a fadar Sarkin Maganin da ke Kano a ranar Laraba, inda Sarkin ya shawarci sabon Sarkin Maganin da ya yi koyi da kyawawan halayen mahaifinsa na ƙaunar al'umma, karamci da biyayya ga masarautar maganin gargajiya ta Jihar Kano. Da yake jawabi a madadin iyalan marigayin, Alhaji Mukhtar Lamir ya gode wa Sarkin Maganin Kano da majalisarsa bisa wannan naɗi. Ya…
Read More
Gwamnatin Kano ta dakatar da shirin rigakafin zazzaɓin cizon sauro

Gwamnatin Kano ta dakatar da shirin rigakafin zazzaɓin cizon sauro

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Kano ta dakatar da dukkan ayyukan Shirin Rigakafin Zazzaɓin Cizon Sauro na Lokacin Damina (SMC) a faɗin jihar, tare da kafa wani babban kwamitin bincike domin tantance yadda aka gudanar da shirin. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Jami'in Hulɗa da Jama'a na Ma'aikatar Lafiya ta Jihar Kano, Nabilusi Abubakar K/Na'isa, ya fitar a ranar Alhamis. A cewar sanarwar, matakin ya biyo bayan kafa kwamitin da aka ɗora wa alhakin gudanar da cikakken bincike kan yadda aka tsara shirin, yadda aka rarraba rigakafin da kuma yadda aka aiwatar da shi, domin tabbatar…
Read More
Zan fice daga APC idan Tinubu ya ci mutuncin limaman Cocin Katolika — Orji Kalu

Zan fice daga APC idan Tinubu ya ci mutuncin limaman Cocin Katolika — Orji Kalu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Tsohon Gwamnan Jihar Abia, kuma Sanatan da ke wakiltar Mazaɓar Abia ta Arewa, Orji Kalu, ya bayyana cewa zai yi murabus daga jam'iyyar APC matuaar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya taɓa kimar limaman Cocin Katolika. Sanatan ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata hira da aka yi da shi a shirin Politics Today na gidan talabijin na Channels, inda ya kare Shugaba Tinubu daga zarge-zargen cewa ya ci mutuncin Cocin Katolika bayan musayar kalamai da aka samu tsakanin Fadar Shugaban ƙasa da shugabannin cocin kan halin da ƙasa ke ciki. Orji Kalu ya ce,…
Read More
Sarkin Musulmi ya buƙaci a binciki zargin kashe Kanal Abdulkarim

Sarkin Musulmi ya buƙaci a binciki zargin kashe Kanal Abdulkarim

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa'ad Abubakar, ya buƙaci gwamnatin tarayya da rundunar sojojin Nijeriya su gudanar da cikakken bincike kan zargin kisan jami'in soji, Kanal Abdur-Razaƙ AbdulKarim Ode, tare da tabbatar da cewa an gano waɗanda ke da hannu a lamarin kuma an hukunta su bisa doka. A cikin wata sanarwa da Yarima Bashir Adefaka ya fitar a madadin tawagar yaɗa labaran Sarkin Musulmi, Sarkin ya bayyana damuwarsa kan yadda aka ce an harbe Kanal Ode a gidansa da ke Abuja, yana mai cewa wajibi ne a gano haƙiƙanin abin da ya faru. Sarkin…
Read More
Sanata Ogoshi ya bayyana dalilinsa na barin jam’iyyar ADC

Sanata Ogoshi ya bayyana dalilinsa na barin jam’iyyar ADC

Daga JOHN D. WADA a Lafiya  Sanata Ogoshi Onawo mai wakiltar mazaɓar sanatan Nasarawa ta Kudu a majalisar dattawa ya bayyana cewa ya bar Jam’iyyar African Democratic Congress ADC ne saboda zaɓen fidda gwamnan jam’iyyar bai kasance cikin gaskiya da adalci ba. Onawo wanda a kwanan nan ya sauya sheka zuwa jam’iyyar Allied People’s Movement APM bayan ya sha kaye a zaɓen fidda gwamin ADC ɗin a hannun James Angbazo a kujerar gwamnan jihar na 2027 mai zuwa yace da an gudanar da zaɓen cikin gaskiya da adalci da zai karɓi sakamakon. Da yake tattaunawa da manema labarai a gidansa…
Read More

An maka tsohon jami’in DSS a kotu kan zargin zama mamban IPOB

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Tsaro ta Farin kaya DSS, ta gurfanar da ɗaya daga cikin tsofaffin jami’anta mai suna Nwaogu Ezeakolam a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja bisa zargin sa da danganta kansa da ƙungiyar ta'addanci ta 'yan fafutukar kafa ƙasar Biafara IPOB. Rahotanni sun bayyana cewa, Daraktan kula da Shari'o'in Gwamnatin Tarayya (DPPF), Rotimi Oyedepo ya shigar da ƙarar, inda aka gurfanar da Ezeakolam a gaban Mai Shari'a Mohammed Umar bisa tuhumarsa da hannu a laifuka huɗu na zargin zama mamban IPOB da kuma wasu da suka saɓa wa dokokin haramcin ta'addanci na 2022…
Read More