Labarai

Kano: Ɗan majalisa ya ƙaddamar da tashar lantarki a Bichi don bunƙasa sana’o’i

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Ƙaramar Hukumar Bichi daga Jihar Kano, Alhaji Abubakar Kabir Abubakar, ya ƙaddamar da buɗe tashar wutar lantarki da ake kira Farno-farno a ƙaramar hukumar. A sanarwar da Jami'ar Yaɗa Labarai ta yankin, Jamila Abdullahi Rijiyar Lemo ta fitar, ta ce ya bayyana shekaru huɗu da suka wuce suke ta fafutukar yadda za a samar da tsayayyiyar wutarlantarkin a garuruwan mazaɓun yamma a garin Bichin, duba da ƙaruwar yawan jama'ar mazaɓun a halin yanzu, da hakan ya janyo matsalar rashin samun wuta yadda yakamata a yankunan. Mazaɓun da suka haɗa da; Ɗanzabuwa, Ƙyalli, Ƙauƙau da kuma…
Read More

Abin fashewa ya tarwatse a Abuja

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Al'umma a yankin Gadar Apo na Abuja sun shiga firgici a daren Alhamis wayewar Juma'a bayan ɓullar rahotannin tarwatsewar wani abin fashewa a kusa da gidan man Shafa, kusa da Otel ɗin Rita Lori da ke Garki. Wani shaida ya bayyana cewa ya ce ƙarar fashewar wani abu a lokuta mabambanta har sau bakwai, inda da fari ya yi zaton ko bom ne. An ruwaito cewa al'amarin ya faru ne a kuaa da gidan man, wanda ke haɗa jama'a, lamarin da ya haifar da tsoro da tilasta wa masi ababen hawa da mazauna yankin…
Read More

ICPC ta miƙa wa Tinubu rahoton binciken badaƙalar hukumar bogi, ta shawarci a gurfanar da Adeyemi

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ICPC, ta damƙa rahotonta na wucin-gadi ga Shugaba Bola Tinubu kan binciken da ta gudanar akan badaƙalar ƙagaggiyar hukumar nan ta bogi (PFIPC), inda ta bayar da shawarar a gurfanar da wanda aka zarga cewa shi ne Darakta-Janar, Adeniyi Adeyemi. Shugaban ICPC, Musa Aliyu ya bayyana haka a ranar Alhamis bayan ganawa da Shugaba Tinubu a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, kwana 30 da shugaban ya umarci hukumar yaƙi da rashawan da ta gudanar da cikakken bincike akan zargin badaƙalar PFIPC. A cewar Aliyu, binciken ya…
Read More
Shugaban ƙaramar hukumar Augie ya ƙaddamar da yasar magudanun ruwa

Shugaban ƙaramar hukumar Augie ya ƙaddamar da yasar magudanun ruwa

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Shugaban ƙaramar hukumar mulki ta Augie Honarabul Yahaya Muhammed Augie ya ƙaddamar da aikin yasar magudanun ruwa a manyan garururwan da ke ƙaramar hukumar. Da ya ke jawabi yayin ƙaddamar da aikin a garin Augie, Honarabul Yahaya Muhammed ya ce wannan yana daga cikin ayyukan da ya kamata a fuskanta saboda kaucewa barazanar ambaliya saboda masana sun yi hasashen akwai yiyuwar ambaliya a wannan daminar. Ya ƙara da cewa ko ba komai dai yana da kyau mutane su tsaftace muhallin su saboda gudun kamuwa da cututtuka musamman a yanayin damina. Ya nemi magidanta da su…
Read More

Shettima ya je hutu a karon fari bayan shekara uku

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima zai fara hutun mako biyu daga ranar Alhamis, 6 ga watan Agusta, 2026 bayan Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince masa, lamarin da ke nuna karon farko da irin haka ya faru tun bayan hawansu kan karagar mulki a shekarar 2023. Wannan hutu zai ba wa mataimakin shugaban ƙasar damar yin amfani da lokacin wajen yin nazari da kuma sararawa domin sabunta karsashinsa na cigaba da hidimta wa ƙasa da kuma kimtsa wa shirye-shiryen zango na gaba na gwamnatin nasu. Kakakin mataimakin shugaban ƙasa, Stanley Nkwocha ne ya sanar…
Read More

Yanzu-yanzu: Tinubu ya umarci EFCC ta buɗe asusun bankin gwamnatin Osun

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci Hukumar Hana yi wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Ta'annati (EFCC) ta gaggauta neman kotu ta soke umarnin rufe asusun gwamnatin Jihar Osun da kuma daina ɗaukar dukkan wani mataki akan jihar game da al'amarin. Tinubu ya bayar da wannan umarni ne a wata takarda da ya sanya wa hannu a ranar Alhamis, 6 ga Agusta, 2026, inda ya ce ya ji takaici akan lokacin da hukumar ta ɗauki matakin, yana mai cewa ba ya inkarin ikon da dokar ƙasa ta ba EFCC na aiwatar da hukuncin saidai bai dace…
Read More
An ƙirƙiro masarautun iyayen ƙasa biyu a Kebbi

An ƙirƙiro masarautun iyayen ƙasa biyu a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Gwamantin jihar Kebbi ta amince da ƙirƙiro sababbin sarautun iyayen ƙasa biyu daga ƙaramar hukumar Argungu a cikin yankin masarautar Sarkin Kabin Argungu. Sanarawar tana ƙunshe ne a cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun kwamishinan ƙananan hukumomi da masarautu Honarabul Garba Umar Dutsinmari ranar Laraba ɗin nan. Takardar ta ce ƙirƙiro masarautun iyayen ƙasar Gwazange da Yamman ya biyo bayan yanke shawarar akwai buƙatar ƙarin sarautun iyayen ƙasa a cikin ƙwaryar garin Argungu, ƙaramar hukumar mulki ta Argungu ta kuma amince da haka inda aka ɗaga darajar hakimin anguwar Gwazange Muhammadu Ibrahim zuwa…
Read More
An yaba wa Bola Tinubu kan ƙarin albashi da ya yi wa sojoji

An yaba wa Bola Tinubu kan ƙarin albashi da ya yi wa sojoji

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Shugaban kwamintin sojoji a Majalisar Dattijai Sanata Abdul'aziz Musa yar'adua ya yaba wa shugaban ƙasa Bola Tinubu kan ƙarin albashi da yayi wa sojoji daga naira dubu 100 zuwa dubu 180. A hira da wata kafar sadarwa national update.ng a Abuja, Sanata Abdul'aziz yar'adua ya bayyana wannan ƙarin albashi a matsayin wani jari a harkan tsaron Najeriya. Sanatan ya ce sabon tsarin albashin da zai fara aiki a wata mai zuwa , "Sojoji 25000 za su amfana da shirin wanda haka ya nuna cikakken goyon baya na gwamnatin Najeriya ga sojojin da ke sadaukar da…
Read More

Hukumar Shige da Fice ta haɗe tsarin mallakar fasfo waje guda

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa (NIS), ta kammala shirin kawo karshen aikin buga fasfuna a ofisoshinta dake jihohin Nijeriya, inda yanzu ta mayar da tsarin bugawa a cibiya guda da ke hedikwatarta Abuja. NIS ta ɗauki wannan mataki ne da nufin ƙarfafa tsaro, inganta harkar gudanarwa da kuma zamanantar da tsarin samar da fasfo a Nijeriya. A wata sanarwa da jami'inta na hulɗa da jama'a, Akinsola Akinlabi ya fitar a ranar Laraba, ya ce masu neman samun fasfo za su cigaba da zuwa ofisoshin da suke so, yan ai tabbatar da cewa cibiyoyin…
Read More

Yadda ake duba jarrabawar kammala sakandare ta 2026

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Hukumar Shirya Jarrabawar Yammacin Afirka (WAEC), ta sanar da fitar da sakamakon jarrabawar kammala sakandare (WASSCE) ta 2026 ga ɗaliban da suka rubuta. Domin duba sakamakonsu, ana buƙatar ɗalibi ya samo lambobin sirri (PIN) da lambar shaida (serial number) daga sahihin shafin WAEC kafin cigaba da cika ƙa'idojin duba sakamakonsa. Haka kuma, wajibi ne ɗalibi ya bayar da lambarsa ta jarrabawa, lambar katin shaidar zama ɗan ƙasa (NIN) da ya yi amfani da ita yayin rajista da wasu bayanansa kafin kammala bin hanyoyin tantancewar. Ga matakan da ɗalibi zai bi wajen samun duba sakamakon…
Read More