Adabi

Martin Cooper: Wanda fara ƙirƙiro wayar salula

Martin Cooper: Wanda fara ƙirƙiro wayar salula

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babu shakka batun wayar salula abu ne da ya dabaibaye duniya a halin yanzu. Da dai kafin zuwan wayar Salula, mutane suna rayuwarsu ne hankalin su a kwance, amma yanzu da wayar Salula ta zama ruwan-dare game duniya, babu wanda ya ke so ya rayu ba tare da ita ba. To shin zargi za mu yi ko kuma godiya ga wanda ya ƙirƙiro mana da wannan abu, wanda ya ke cinye wa mutane kuɗi? To imma dai zargin ne ko kuma yabon, to wanda za a zarga ko kuma a yaba shi ne Dakta Martin Cooper.…
Read More
Na gaji fasahar rubutu daga mahaifiyata – Khairat U.P

Na gaji fasahar rubutu daga mahaifiyata – Khairat U.P

"Rubutu ba ruwansa da girman ka ko ƙanƙantarka" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Akwai masu ganin cewa ba a gadon basira ko wata baiwa ta ƙirƙira, domin kuwa wannan kyauta ce ta Allah. Amma fa duk da haka da akwai waɗanda za a iya cewa ƴan na gada ne da sun wuce ƴan na koya. Ummulkhairi Sani Panisau da aka fi sani da Khairat UP na daga cikin marubutan da suka taso cikin gidan rubutu, domin kuwa ƴa ce a wajen fitacciyar marubuciyar nan Sadiya Garba Yakasai, wacce ta rubuta littattafai fiye da 80, kuma har yanzu tana jan zarenta a…
Read More
Tarihin Gidan Arewa a Kaduna

Tarihin Gidan Arewa a Kaduna

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gidan tarihi na Arewa (Arewa House Centre For Historical Research and Documentation) da ke garin Kaduna a yankin arewa maso yammacin Nijeriya, cibiya ce da ke tattara tarihin Marigayi Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato da Lardin Arewa da kuma tarihi da al'adu da sana'o'in yankin. An kafa cibiyar ne bayan kisan gillar da aka yi wa Firimiyan Arewa na farko Sardauna, a juyin mulkin da sojoji suka yi a Ranar 15 Ga Watan janairun shekarar alif 1966. Sojojin sun tayar da bam, suka kuma kashe Sardauna da matarsa da ma'aikatansa a wannan gida. A juyin mulkin ne…
Read More
Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi sabbin shugabanni

Ƙungiyar Marubuta ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi sabbin shugabanni

Daga IBRAHIM HAMISU, Kano Ƙungiyar marubuta ta ƙasa reshen Jihar Kano, wato Association of Nigerian Authors (ANA) ta yi sabbin shugabanni da ya biyo bayan taron da ya gudana a ɗakin karatu na Murtala Muhammed ranar Lahadi da ta gabata. An dai yi zaɓen ƙungiyar ne yayin gabatar da manyan taruka da ta saba gudanarwa duk ƙarshen wata. An kuma zavi Dr.Murtala M. Uba wanda malami ne a sashen ilimin nazarin ƙasa wato (Geography) da ke jami'ar Bayero Kano a matsayin sabon shugaban ƙungiyar. Jim kaɗan bayan kammala zaɓen ne dai, sabon shugaban Dr. Murtala Uba ya ce, za su…
Read More
Kowa ya yi rubutu mai kyau zai samu karɓuwa – Ado Ahmad MON

Kowa ya yi rubutu mai kyau zai samu karɓuwa – Ado Ahmad MON

"Kyakkyawar mu'amala da mutane tasa ake karrama ni" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Sunan Ado Ahmad Gidan Dabino (MON) Sani Mai Nagge, ba ɓoyayye ba ne a duk faɗin ƙasar nan, ba ma tsakanin marubuta da masu shirya finafinai ba, har ma da manazarta na ƙasa da ƙasa. Ya yi rubuce-rubuce da dama cikin harsunan Hausa da Turanci, a ciki har da littafin da yanzu haka ya shiga cikin manhajar koyar da Hausa a manyan makarantun sakandire na qasar nan. Ya samu shaidar karramawa iri-iri da suka jawo masa ɗaukaka a duniya fiye da duk wani marubucin Hausa. A zantawarsa da…
Read More
Tarihin Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Hussaini CON, RTA (2)

Tarihin Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Hussaini CON, RTA (2)

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Cigaba daga makon da ya gabata. Ya na iya zama abin farin ciki sanin cewa, Sheikh Ibrahim Saleh ya yi shekaru ashirin ne kacal (1944-1964) a matsayin ɗalibi, kuma ya samu kusan dukkan horon da ya yi a Nijeriya. Duk da haka, wannan ba ya na nufin cewa dukkan malamansa ’yan Nijeriya ne ba. Amma duk da haka, ya kasance masani na gida, wadda aka samar a cikin gida ta hanyar tsarin Tsangaya. Watau, horon da ya samu a cikin tsarin karatun gida ne ya ba shi damar kasancewa mashahuri a ƙasashen duniya, da kuma karrama…
Read More
Rubutuna ya fi mayar da hankali kan illolin bin bokaye da ‘yan tsubbu – Lailat Abdullahi

Rubutuna ya fi mayar da hankali kan illolin bin bokaye da ‘yan tsubbu – Lailat Abdullahi

"Ya kamata manyan marubuta su kama hannun ƙanana, su yi masu jagora" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Zainab Abdullahi Musa mai laqabi da Lailat, matashiyar marubuciya ce daga Jihar Katsina, wacce ta kasance mai himma da kishin rubutun adabin Hausa. Duk da kasancewarta ɗalibar koyon aikin jinya, bai hana ta ware lokaci na musamman don yin rubutun da zai taimaka wajen ilimantar da matasa ƴan'uwanta game zamantakewar rayuwa, da muhimmancin bin iyaye. Kawo yanzu ta rubuta littattafai guda biyar, har yanzu tana cigaba da rubutu. A zantawarta da wakilin Blueprint Manhaja, marubuciyar ta bayyana masa irin gwagwarmayar da ta sha kafin…
Read More
Tarihin Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Hussaini CON, RTA (1)

Tarihin Sheikh Sharif Ibrahim Saleh Al-Hussaini CON, RTA (1)

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fitaccen malamin addinin Musulunci a Nijeriya, wanda ya rubuta fiye da littattafai (400) na addinin Musulunci da hannunsa. Malamin, wadda jigo ne a ɗarikar Tijjaniyya a halin yanzu shi ne shugaban Majalisar Ƙoli ta Fatawa da Al'amuran Musulunci a Nijeriya (NSCIA). Malamin ya kasance ɗan ƙabilar Shuwa Arab, kuma ya yi karatu a wurare da dama da suka haɗa da; Makka, da Madina, da Masar, da Pakistan, da Iran, Senegal da sauran su, a wajen manyan malaman Musulunci, ciki har da babban makarancin Al-Ƙur'anin nan Mahmoud Khalilul Khusari, a Masar. An haifi Sheikh Sharif Ibrahim Saleh…
Read More
Marubuta a dinga bincike kafin rubutu – Gimbiya Rahma

Marubuta a dinga bincike kafin rubutu – Gimbiya Rahma

"Tun Ina firamare na fara rubutu" Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Sanannen abu ne, rubutun adabi ya ta shi daga hannun masu buga littafai zuwa yanar gizo, wanda hakan ne ya ba wa matasa damar baje basirarsu ba tare da tunanin fara neman kuɗin buga littafi ba. Ta dalilin hakan ya sa ake samun marubuta da yawa masu rubutu kuma mai ma'ana, hakan ya tabbatar da cewa, matasan marubuta na matuƙar ƙoƙari wurin samar da labarai da za su ƙayatar da masu karatu. Duk da cewa, an yi ammana rubutun intanet ba karɓe wa marubuta kasuwa ya yi ba, samar…
Read More
Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski Ƙasar Hausa

Tarihin Gobir da yadda Gobirawa suka riski Ƙasar Hausa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙasar Gobir na ɗaya daga cikin ƙasashen Hausa na ainii, an ce ita ɗin tsohuwar daula ce kuma wata babbar ƙasa ce da ta yi iyaka da Agades daga arewa, ta yi iyaka da Zamfara daga Kudu, ta yi iyaka da Mayali daga Gabas, sannan kuma daga yamma ta yi iyaka da Konni. Amma magana anan ita ce, asalinsu ba hausawa bane tunda wasu na cewa asali wai daga gabas ta tsakiya suka fito musamman ma Misira, inda ake da yaƙinin cewa Sarakuna ukku daga cikin sarakunan Misira gobirawa ne. Sarkin Gobir Mai Martaba Alhaji Abdulhamid…
Read More