Adabi

Alƙalancin gasar rubutu

Alƙalancin gasar rubutu

Daga KABIRU YUSUF FAGGE Bayan da na saurari bayanan wasu alƙalan gasannin rubuce-rubucen ƙagaggun labarai a mabambantan gasanni, na tsinkayi akwai abubuwan da za su amfani marubuta masu sha’awar shiga gasa don yin nasara. ɗabi’ar karatu Wannan a bayyane yake cewa, yanzu al’umma sun fi son su kalla ko su saurara fiye da karantawa. Idan haka ne, to kai marubuci kana da gagarumin ƙalubale rubuta labarin da zai sa alƙalan gasa ko suna so ko ba sa so za su karanta, wato ko ba don aikin da aka ba su na karanta labarin su yi alƙalanci ba, ko don salo…
Read More
An fitar da sanawar bayan taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya

An fitar da sanawar bayan taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Taron Ranar Marubuta Hausa ta Duniya ya gudana cikin nasara a ranar 31/12/2025 a garin Dutse Jihar Jigawa, inda ya haɗa marubuta, manazarta, malamai, ɗalibai, da wakilan gwamnatoci daga sassa daban-daban na Nijeriya da maƙwabtanta. Taron ya ƙara jaddada muhimmancin rubutun Hausa a ƙarni na 21, musamman a fuskokin tsaro, tattalin arziki, al’adu, da ci gaban al’umma. Muhimman abubuwan da taron ya tattauna: 1. ƙalubalen Tsaro da Al’adar Karatu: An jaddada cewa duk da ƙalubalen rashin tsaro, akwai babbar matsala ta raguwar al’adar karatu musamman a tsakanin matasa, wadda ke buƙatar tsayuwar daka. An…
Read More
Burina shine fito da daraja da mutuncin matan Arewa – Hajara Kabir

Burina shine fito da daraja da mutuncin matan Arewa – Hajara Kabir

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Kamar yadda ya gabata a kundin farko (na shekarar 2010), wannan kundin na gaba ya ƙunshi jerin muƙaloli masu alaƙa da juna amma mabambanta, waɗanda ke bayani kan mata daga fannoni daban-daban na al’umma, tare da bambancin matakan nasara daga Arewacin Nijeriya. (Northern Women Development: A Historical and Contemporary Perspective on Northern Nigerian Women) yana nazartar rikitarwa da ke tattare da nasarorin da mata suka samu cikin yanayin al’adu da addini na Arewacin Nijeriya, na tarihi da na zamani. Lokacin da ƙwararrun marubuta mata, masana da ‘yan jarida irin su Hajara Muhammad Kabir suka raba…
Read More
Ranar Marubuta 2025: Wacce wainar aka toya tsakanin marubuta da manazarta?

Ranar Marubuta 2025: Wacce wainar aka toya tsakanin marubuta da manazarta?

"Jihar Katsina ta yi alƙawarin ɗaukar nauyin taron Ranar Marubuta wanda za a yi na gaba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A karo na uku, marubuta da manazarta adabin Hausa daga sassan nahiyar Afirka da Nijeriya sun yi haɗuwar yaushe rabo, a garin Dutse, Babban Birnin Jihar Jigawa, wanda aka gudanar a ranar 31 ga watan Disamba, 2025, domin ƙarfafa zumunci da tattauna hanyoyin inganta rubutun Hausa, don a duba yadda za a samar da haɗin gwiwa tsakanin marubuta da mahukunta, da nufin gano bakin zaren warware matsalolin tsaro da tattalin arziƙi da suke addabar wasu jihohin Arewa. An zaɓi a…
Read More
Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya: Kwalliya ta biya kuɗin sabulu

Taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya: Kwalliya ta biya kuɗin sabulu

Daga MUKHTAR YAKUBU  A ranar Laraba 31 ga Disamba 2025 aka gudanar da taron Ranar Marubutan Hausa ta Duniya a babban ɗakin taro na Manpower Deɓelopment Institute dake birnin Dutse Jihar Jigawa. Taron ya samu halartar marubuta manazarta tarihi da al'adu daga cikin Nijeriya da ma wasu ƙasashe na Afrika. Taron wanda ya kasance na kwana guda ne an yi jawabai da sharhi da kuma tattauna muhimman batutuwa da suka shafi rayuwar marubuta da shi kanka rubutun. An dai fara taron ne da misalin ƙarfe 11 na safe inda bayan jawabin buɗe taro aka shiga taron, inda a farkon aka…
Read More
Yadda aka gudanar da bikin auren marubuci  Zubairu Musa Balannaji

Yadda aka gudanar da bikin auren marubuci  Zubairu Musa Balannaji

Daga MUKHTAR YAKUBU  Masu magana su kan ce rana ba ta karya, sai dai uwar 'ya ta ji kunya. Kamar yau ne ake ta maganar an saka ranar auren marubuci Zubairu Musa Balannaje. Cikin hukuncin Allah sai ga shi kuma har ranar ta zo. Domin kuma a ranar  Lahadi 28 ga Disamba 2025 ne aka ɗaura auren Zubairu Musa Balannaje da amaryasa A'isha Auwal Umar. An ɗaura auren ne da misalin ƙarfe 10 na safe a masallacin Juma'a na Ammar Ibn Yassir dake Unguwar Samegu Gangar ruwa a cikin garin Kano inda ɗumbun jama'a suka taru domin shaida ɗaurin auren.…
Read More
Yadda aka gudanar da taron ranar marubuta Hausa ta duniya a Jigawa

Yadda aka gudanar da taron ranar marubuta Hausa ta duniya a Jigawa

Daga IBRAHIM HAMISU a Jigawa Haɗakar ƙungiyar ƙungiyoyin marubuta ta Nijeriya ta gudanar da taron ranar marubutan Hausa ta duniya, da ya gudana a Jihar Jigawa, ranar Laraba 31 ga Disambar 2025. Taron wanda aka assasa shi domin al'amura da harkokin marubuta, da kuma bajekolin fasahohin marubuta da littattafai. Kabir Yusuf Anka shi ne mai magana da yawun babban kwamitin shirya taron, ya bayyana cewa manufar shirya taron shi ne sada zumunci da haɗuwa da juna da buɗe ido. Ya ce taron ya kasance ana tattaunawa rubuce-rubucen ƙagaggun labarai na Hausa da al'adu da harshe da tarihi duka na Hausawa.…
Read More
Daga Labarawa Bahaushe ya aro amfani da ƙafiya – Khalid Imam

Daga Labarawa Bahaushe ya aro amfani da ƙafiya – Khalid Imam

"Waƙa saƙa ta ake yi kamar tabarmar kaba, shi kuma zube gina shi ake kamar yadda ake gida" Daga AISHA ASAS Shahararre kuma sanannen marubuci da ake alfahari da shi a duniyar Adabin Hausa Khalid Imam, ya samu damar amsa gayyatar jaridar Blueprint Manhaja inda masu karatu za su ji cikakken tarihi tare da nasarorin da ya samu a duniyar rubutu. An dai ce waƙa a bakin mai ita za ta fi zaƙi, ku biyo wakiliyar mu Aisha Asas don jin wane ne Khalid Imam. MANHAJA: Masu karatu za su so jin tarihinka. KHALID: Sunana Khalid lmam. An haife ni…
Read More
Bambancin da ke tsakanin Hikayata da sauran gasa tamkar jami’a ce da kwaleji – Hafsat Sani Tanko 

Bambancin da ke tsakanin Hikayata da sauran gasa tamkar jami’a ce da kwaleji – Hafsat Sani Tanko 

Gasar Hikayata ita ce babbar gasar da babu kamar ta - Fadila Lamiɗo  Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A bana Gasar Hikayata ta marubuta mata zalla da tashar BBC Hausa ta saba gabatarwa duk shekara ta cika shekara goma. A kowacce shekara kamar yadda muka saba gani, mata marubuta daga sassan duniya daban-daban, inda ake da Hausawa ko masu amfani da harshen Hausa, suna aikawa da labaransu, domin neman shiga gasar ƙirƙirarrun gajerun labarai ta Hikayata. A ƙarshen gasar ana fitar da gwaraza uku da labaransu suka yi fice, tare da jinjina ga rukuni na biyu na mutane goma sha biyu…
Read More
Yin amfani da marubuta zai iya shawo kan matsalar tsaro a Nijeriya – Malumman Matazu

Yin amfani da marubuta zai iya shawo kan matsalar tsaro a Nijeriya – Malumman Matazu

 "Da Rana tsaka na tsinci kaina a matsayin marubucin waƙa" Daga AISHA ASAS Abdulhamid Muhammad Sani wanda yawanci suka fi sani da Namatazu ko Maluman Matazu, marubuci wanda ya yi fice kuma ya shahara wajen rubutawa da tsara rubutacciyar waƙa. Shi dai mazaunin garin Matazu da ke Jihar Katsina. A wannan hirar da Aisha Asas ta yi da shi ya taɓo batutuwa da dama da suka shafi rayuwar sa, ƙalubale da kuma irin gudunmuwar da marubuta ke bada wa ga al'umma. Ga dai yadda hirar tasu ta kasance: MANHAJA: Masu karatu za su so jin taƙaitaccen tarihinka? NA MATAZU: Bismillahir…
Read More